Sashe 16
Rabo Ajali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Watanshi ďaya a asibiti ana fama da lalura ďaya,
saidai a kawo babban likitan mahaukata gurinshi ya dinga mishi treatment saboda ciwon da ke kanshi,
yanzu kam ciwon yayi sauki sosai dan haka doctor musa ya bada shawarar a kaishi "psychiatric" alhj basheer sam yaki yarda yace saidai ya fita dashi waje,
doctor musah yace hakan ma zaifi Alhj, gara ka kaishi wajen, akwai wani asibiti a "New Toronto, Canada" sunanshi "LAKESHORE PSYCHIATRIC HOSPITAL" asibitin sun kware sosai alhj, in dai waje zaka fita dashi gara ka kaishi can,
kuma anan nigeria ma fa akwai psychiatric masu kyau kuma ana kula sosai, kamar su "FEDERAL NEURO PSYCHIATRIC" dake kaduna da kuma na Lagos, da ma sauransu, amma tunda hankalinka yafi ga fita dashi din gara ka fita dashi, mudai fatanmu a koda yaushe shine ya samu lfy,
, alhj basheer yace hakane doctor, nagode sosai in shaa Allah gobe zamu fara processing tafiyar,, doctor musah yace to Allah ya kaimu alhj shi kuma Allah ya------- doctor musa ya kasa karasawa saboda datse harshenshi da yayi, ya kalli alhj basheer ya mika mishi takardun sallama da reports din ciwon Affan tare da magunguna...
Watan Affan biyu a canada, oyizah ke zaune dashi saboda yawan tafiye tafiyen da alhj basheer keyi, jikinshi yayi kyau sosai saidai duk wanda ya ganshi yaga mai tabin hankali, komai na yara yakeyi, ga yawan son wasa, kallon ruwa da kifaye da sauransu,
a cikin wata biyun nan oyizah ta mallake Affan sai abinda tace yayi, sam bata nuna mishi hanyar kwarai saidai ta nuna mishi mara billewa, magungunan tsafi kuwa su ke ďawainiya dashi tun zuwansu canada,
doctors sunyi mamakin yadda akayi magungunan da suke bawa Affan bai mishi aiki ba,
sudai sunsan larura indai ta haukace to wacce tafi ta affan ma sun warkar bare tashi da suke ganinta minor, basu san duk magungunan da suke zuwa bashi oyizah ta karba tace zata bashi zubar dasu takeyi ba,
wani lokacin ne ma take bashi ba bisa ka'ida ba,
A ranar da suka cika wata biyu da sati biyu aka sallamesu saboda haukar affan ba ta barna bace kuma sunga in oyizah tace ya zauna nan to bazai tashi ba har sai tace ya tashi,
wannan dalilin yasa suke ganin kamar in suka basu isassun magunguna nan da wasu yan watanni zai samu sauki..
Ranar oyizah tayi murna saboda dama ta kosa ta koma gida,
yawo ta fita da Affan tayi mishi siyayyar kayan wasa da uban yawa tana zaba tana mishi dariyar mugunta shi kuwa banda murna da tsalle babu abinda yakeyi,
a daren ranar suka hawo jirgi tare da alhj basheer sai kasar mu ta gado...
Cikin dare suka iso gida a gajiye, kowanne daki yaje ya kwanta banda Affan da shi a gurinshi ma safiya ce,
zama yayi a parlor yana wasa sosai gaba daya ya hargitsa parlon,
in ya kalli hanyar dakin zeenatu sai ya runtse idonshi wasu abubuwa su dinga gifta mishi kamar rayuwar cartoon,
kuma sai yaga kamar harda shi a cikin cartoon din,
tashi yayi yana kokarin zuwa kofar dakin yaji muryar oyizah ta daka mishi tsawa,
da sauri ya dawo bayanta ya tsaya yace mummy wannan kofar wanene,
kamar na taba zama a ďakin, kin gani kofar ma kamar ta drawing ko,
oyizah ta shafa kanshi tace my baby kasan meye a kofar nan, ya girgiza mata kai, ta ja hannunshi ta fara nuna mishi kofar har zuwa hanyar steps din can saman da ya faďo tace duk nan gurin zaman macizai, da namun daji ne, kana son su cinye ka, ya noke wuyanshi ya make a bayanta,
tace to karka kara zuwa arean gurin kaji, yace to mummy,
ta kama hannunshi ta wuce side dinta dashi ta sashi a wani daki ta rufe tana kyakyata dariyar mugunta da jindadi..
Tun karfe 12 jabeer keta fama da masu gadin gidan akan su bude mishi kofa sunki, dan oyizah tace kar a kara barin kowa ya shigo saida izininta, ran jabeer ya baci sosai idonshi yayi jawur,
yace yanzu Halilu har ni ma sai ku hana shiga in an saku,
halilu yace kwarai kuwa saboda ina mutunta aikina,
jabeer yayi kwafa kamar zai juya sai ya dawo da karfinshi ya tura halilu ya ruga ciki da gudu suna binshi a baya,
da sauri alhj basheer ya fito jin hayaniyar tayi yawa,
tsawa ya daka ma su halilu yace lafiya kuke binshi kamar wani barawo,
halilu yace ranka ya dade madam ce tace kar abar kowa ya shigo,
alhj basheer yace jabeer ne kowa, baku san matsayinshi a gidannan bane,
oyizah ta fito da sauri tace yi hakuri alhj mantawa nayi in ce musu kar su hana jabeer shigowa,
alhj basheer yace to su sauran mutanen kuma fa meye dalilin hanasu shigowa,
ta fara matsar kwallah tace bana son a shigo a dinga yi ma affan dariya na fi son sai ya warke mutane su ganshi,
alhj basheer ya jinjina kai cikin damuwa yace na gamsu da bayananki, share hawayenki Allah yayi miki abinda kikayi mana na alkhairi, tace ameen haďe da hararar jabeer,
alhj basheer yace jabeer ka shiga ciki mana abokin naka yana ciki ai,
jabeer yasa kai ya shiga cikin parlon da sallama,
Zaune ya tarar da Affan da wasu kayan wasa a hannunshi, wuyanshi yasha hoda idonshi kuma kwalli, kallon jabeer yakeyi sosai wasu abubuwa na mishi yawo a kwakwalwarshi,
sai da yayi minti biyar yana kallonshi sannan ya zubar da kayan wasan ya rungumeshi yace daddy wannan abokina ne sosai tare muke wasa dashi, kaga fuskarshi ma shima drawing dinshi akayi kamar waccan kofar,
Salma da fareeda suka kwashe da dariya harda rike ciki, yayin da jabeer ya fashe da kuka haďe da kankameshi......
Mrs tijjani shattima...
[15/12 09:34] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 2⃣5⃣ By Aysha Ya'u Kurah
A hankali Affan ya saki jabeer yana mishi wani irin kallo,
fuskarshi ya fara shafawa yana share mishi hawaye yace naji maka ciwo ne, ya ďaura hannunshi a kan jabeer yace yi hakuri kadaina kuka zo muje kaga kayan wasa na, kaima kana so ko?
jabeer ya gyada mishi kai hawaye na fita a idonshi,
Affan ya ďan bata fuska yace to ka daina kuka zan baka wasu sai ka tafi dasu kaji, Jabeer ya kasa daurewa ya saki hannun Affan ya fita daga gidan da gudu yana kuka sosai,
Affan ya bata rai sosai kamar zaiyi kuka ya kalli daddy yace daddy kaga ya tafi yana kuka ko,
kuma ay na bashi hakuri bansan zaiji ciwo ba, ka bishi ka dawo min dashi muyi wasa kaji,,
alhj basheer ya share kwallar da ta zubo mishi yace zai dawo yanzu affan yaje ya siyo maka abin dadi ne,
Affan ya daka tsalle yace daddy kace mishi ya taho min da sweets dinnan masu dadi,
alhj basheer yace karka damu affan je ka cigaba da wasanka, Affan ya gyaďa kai cike da murna ya koma gurin kayan wasanshi..
Salma da fareeda suka mike kunshe da dariya suka wuce daki,
suna shiga suka saketa kamar tababbu, fareeda tace salma kiga yadda affan ya koma kamar dan yaye, salma tace ni ba karamin dariya yake bani ba, ji wani kwallin da mummy tasa mishi a ido dan Allah, fareeda tace ay ni yanzu na samu film din kallo wanda zai dinga sani nishadi, salma tace ke ko ni, suka kara kwashewa da dariya...
Jabeer bai dawo gidansu affan ba sai can da yamma, idonshi a kode saboda tsabar kukan da yaci,
a waje ya sameshi yana buga kwallo, affan na ganinshi ya rungumi kwallonshi ya rugo da gudu zai rungume jabeer sai kuma yaja ya tsaya saboda tunanin kar ya kara sashi kuka irin na dazu,
jabeer yayi murmushi ya buďe hannunshi, affan ya kwashe da dariya sosai ya shige jikinshi yace yanzu banji maka ciwo ba ko, jabeer yace ehh friend, Affan ya ďago kanshi yace ina abin dadin da daddy yace zaka siyomin,
jabeer yasa hannu a aljihu ya fito da chocolates ya mika mishi,
tsalle yayi ya dane jikin jabeer yana murna ya karba yace bari in nuna ma mummy dan tace duk wanda ya bani abu in nuna mata kafin in ci, bai jira jin abinda jabeer zaice ba ya ruga ciki da gudu,
jabeer ya rungume hannunshi yana girgiza kanshi a zuciyarshi yana kara jin tsoron Allah mai maida bawanshi yadda yaso a kuma lokacin da yaso,,,
Tun daga ranar kullum jabeer ya taso aiki zai tsaya a gurin affan suyi hirarsu yayi ta mishi shirme, in lokacin sallah yayi duk yadda zai buga ya raya affan yazo suje zaiki yace sai ya tambayi mummy, daga yaje ya tambayeta zata hanashi ta tsoratar dashi sosai, da taga kullum jabeer na matsama affan akan sallah sai ta bijiro da kokarin rabasu,
da farko tayi nasara dan kuwa ko jabeer yazo bata barin affan ya ganshi, da affan yaga har sati daya baiga abokinshi ba ya ďaga musu hankali sosai a gidan duk irin tsoron da mummy ta bashi bai shigeshi ba shidai kawai a kira mishi abokinshi abinda yake fadi kenan,
da taga kullum bashi da aiki sai kuka kuma baya cin abinci sai tasa masu gadi su nemo mata jabeer dan in alhj ya dawo ya tarar dashi a haka to bazai mata da kyau ba..
saidai a kawo babban likitan mahaukata gurinshi ya dinga mishi treatment saboda ciwon da ke kanshi,
yanzu kam ciwon yayi sauki sosai dan haka doctor musa ya bada shawarar a kaishi "psychiatric" alhj basheer sam yaki yarda yace saidai ya fita dashi waje,
doctor musah yace hakan ma zaifi Alhj, gara ka kaishi wajen, akwai wani asibiti a "New Toronto, Canada" sunanshi "LAKESHORE PSYCHIATRIC HOSPITAL" asibitin sun kware sosai alhj, in dai waje zaka fita dashi gara ka kaishi can,
kuma anan nigeria ma fa akwai psychiatric masu kyau kuma ana kula sosai, kamar su "FEDERAL NEURO PSYCHIATRIC" dake kaduna da kuma na Lagos, da ma sauransu, amma tunda hankalinka yafi ga fita dashi din gara ka fita dashi, mudai fatanmu a koda yaushe shine ya samu lfy,
, alhj basheer yace hakane doctor, nagode sosai in shaa Allah gobe zamu fara processing tafiyar,, doctor musah yace to Allah ya kaimu alhj shi kuma Allah ya------- doctor musa ya kasa karasawa saboda datse harshenshi da yayi, ya kalli alhj basheer ya mika mishi takardun sallama da reports din ciwon Affan tare da magunguna...
Watan Affan biyu a canada, oyizah ke zaune dashi saboda yawan tafiye tafiyen da alhj basheer keyi, jikinshi yayi kyau sosai saidai duk wanda ya ganshi yaga mai tabin hankali, komai na yara yakeyi, ga yawan son wasa, kallon ruwa da kifaye da sauransu,
a cikin wata biyun nan oyizah ta mallake Affan sai abinda tace yayi, sam bata nuna mishi hanyar kwarai saidai ta nuna mishi mara billewa, magungunan tsafi kuwa su ke ďawainiya dashi tun zuwansu canada,
doctors sunyi mamakin yadda akayi magungunan da suke bawa Affan bai mishi aiki ba,
sudai sunsan larura indai ta haukace to wacce tafi ta affan ma sun warkar bare tashi da suke ganinta minor, basu san duk magungunan da suke zuwa bashi oyizah ta karba tace zata bashi zubar dasu takeyi ba,
wani lokacin ne ma take bashi ba bisa ka'ida ba,
A ranar da suka cika wata biyu da sati biyu aka sallamesu saboda haukar affan ba ta barna bace kuma sunga in oyizah tace ya zauna nan to bazai tashi ba har sai tace ya tashi,
wannan dalilin yasa suke ganin kamar in suka basu isassun magunguna nan da wasu yan watanni zai samu sauki..
Ranar oyizah tayi murna saboda dama ta kosa ta koma gida,
yawo ta fita da Affan tayi mishi siyayyar kayan wasa da uban yawa tana zaba tana mishi dariyar mugunta shi kuwa banda murna da tsalle babu abinda yakeyi,
a daren ranar suka hawo jirgi tare da alhj basheer sai kasar mu ta gado...
Cikin dare suka iso gida a gajiye, kowanne daki yaje ya kwanta banda Affan da shi a gurinshi ma safiya ce,
zama yayi a parlor yana wasa sosai gaba daya ya hargitsa parlon,
in ya kalli hanyar dakin zeenatu sai ya runtse idonshi wasu abubuwa su dinga gifta mishi kamar rayuwar cartoon,
kuma sai yaga kamar harda shi a cikin cartoon din,
tashi yayi yana kokarin zuwa kofar dakin yaji muryar oyizah ta daka mishi tsawa,
da sauri ya dawo bayanta ya tsaya yace mummy wannan kofar wanene,
kamar na taba zama a ďakin, kin gani kofar ma kamar ta drawing ko,
oyizah ta shafa kanshi tace my baby kasan meye a kofar nan, ya girgiza mata kai, ta ja hannunshi ta fara nuna mishi kofar har zuwa hanyar steps din can saman da ya faďo tace duk nan gurin zaman macizai, da namun daji ne, kana son su cinye ka, ya noke wuyanshi ya make a bayanta,
tace to karka kara zuwa arean gurin kaji, yace to mummy,
ta kama hannunshi ta wuce side dinta dashi ta sashi a wani daki ta rufe tana kyakyata dariyar mugunta da jindadi..
Tun karfe 12 jabeer keta fama da masu gadin gidan akan su bude mishi kofa sunki, dan oyizah tace kar a kara barin kowa ya shigo saida izininta, ran jabeer ya baci sosai idonshi yayi jawur,
yace yanzu Halilu har ni ma sai ku hana shiga in an saku,
halilu yace kwarai kuwa saboda ina mutunta aikina,
jabeer yayi kwafa kamar zai juya sai ya dawo da karfinshi ya tura halilu ya ruga ciki da gudu suna binshi a baya,
da sauri alhj basheer ya fito jin hayaniyar tayi yawa,
tsawa ya daka ma su halilu yace lafiya kuke binshi kamar wani barawo,
halilu yace ranka ya dade madam ce tace kar abar kowa ya shigo,
alhj basheer yace jabeer ne kowa, baku san matsayinshi a gidannan bane,
oyizah ta fito da sauri tace yi hakuri alhj mantawa nayi in ce musu kar su hana jabeer shigowa,
alhj basheer yace to su sauran mutanen kuma fa meye dalilin hanasu shigowa,
ta fara matsar kwallah tace bana son a shigo a dinga yi ma affan dariya na fi son sai ya warke mutane su ganshi,
alhj basheer ya jinjina kai cikin damuwa yace na gamsu da bayananki, share hawayenki Allah yayi miki abinda kikayi mana na alkhairi, tace ameen haďe da hararar jabeer,
alhj basheer yace jabeer ka shiga ciki mana abokin naka yana ciki ai,
jabeer yasa kai ya shiga cikin parlon da sallama,
Zaune ya tarar da Affan da wasu kayan wasa a hannunshi, wuyanshi yasha hoda idonshi kuma kwalli, kallon jabeer yakeyi sosai wasu abubuwa na mishi yawo a kwakwalwarshi,
sai da yayi minti biyar yana kallonshi sannan ya zubar da kayan wasan ya rungumeshi yace daddy wannan abokina ne sosai tare muke wasa dashi, kaga fuskarshi ma shima drawing dinshi akayi kamar waccan kofar,
Salma da fareeda suka kwashe da dariya harda rike ciki, yayin da jabeer ya fashe da kuka haďe da kankameshi......
Mrs tijjani shattima...
[15/12 09:34] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 2⃣5⃣ By Aysha Ya'u Kurah
A hankali Affan ya saki jabeer yana mishi wani irin kallo,
fuskarshi ya fara shafawa yana share mishi hawaye yace naji maka ciwo ne, ya ďaura hannunshi a kan jabeer yace yi hakuri kadaina kuka zo muje kaga kayan wasa na, kaima kana so ko?
jabeer ya gyada mishi kai hawaye na fita a idonshi,
Affan ya ďan bata fuska yace to ka daina kuka zan baka wasu sai ka tafi dasu kaji, Jabeer ya kasa daurewa ya saki hannun Affan ya fita daga gidan da gudu yana kuka sosai,
Affan ya bata rai sosai kamar zaiyi kuka ya kalli daddy yace daddy kaga ya tafi yana kuka ko,
kuma ay na bashi hakuri bansan zaiji ciwo ba, ka bishi ka dawo min dashi muyi wasa kaji,,
alhj basheer ya share kwallar da ta zubo mishi yace zai dawo yanzu affan yaje ya siyo maka abin dadi ne,
Affan ya daka tsalle yace daddy kace mishi ya taho min da sweets dinnan masu dadi,
alhj basheer yace karka damu affan je ka cigaba da wasanka, Affan ya gyaďa kai cike da murna ya koma gurin kayan wasanshi..
Salma da fareeda suka mike kunshe da dariya suka wuce daki,
suna shiga suka saketa kamar tababbu, fareeda tace salma kiga yadda affan ya koma kamar dan yaye, salma tace ni ba karamin dariya yake bani ba, ji wani kwallin da mummy tasa mishi a ido dan Allah, fareeda tace ay ni yanzu na samu film din kallo wanda zai dinga sani nishadi, salma tace ke ko ni, suka kara kwashewa da dariya...
Jabeer bai dawo gidansu affan ba sai can da yamma, idonshi a kode saboda tsabar kukan da yaci,
a waje ya sameshi yana buga kwallo, affan na ganinshi ya rungumi kwallonshi ya rugo da gudu zai rungume jabeer sai kuma yaja ya tsaya saboda tunanin kar ya kara sashi kuka irin na dazu,
jabeer yayi murmushi ya buďe hannunshi, affan ya kwashe da dariya sosai ya shige jikinshi yace yanzu banji maka ciwo ba ko, jabeer yace ehh friend, Affan ya ďago kanshi yace ina abin dadin da daddy yace zaka siyomin,
jabeer yasa hannu a aljihu ya fito da chocolates ya mika mishi,
tsalle yayi ya dane jikin jabeer yana murna ya karba yace bari in nuna ma mummy dan tace duk wanda ya bani abu in nuna mata kafin in ci, bai jira jin abinda jabeer zaice ba ya ruga ciki da gudu,
jabeer ya rungume hannunshi yana girgiza kanshi a zuciyarshi yana kara jin tsoron Allah mai maida bawanshi yadda yaso a kuma lokacin da yaso,,,
Tun daga ranar kullum jabeer ya taso aiki zai tsaya a gurin affan suyi hirarsu yayi ta mishi shirme, in lokacin sallah yayi duk yadda zai buga ya raya affan yazo suje zaiki yace sai ya tambayi mummy, daga yaje ya tambayeta zata hanashi ta tsoratar dashi sosai, da taga kullum jabeer na matsama affan akan sallah sai ta bijiro da kokarin rabasu,
da farko tayi nasara dan kuwa ko jabeer yazo bata barin affan ya ganshi, da affan yaga har sati daya baiga abokinshi ba ya ďaga musu hankali sosai a gidan duk irin tsoron da mummy ta bashi bai shigeshi ba shidai kawai a kira mishi abokinshi abinda yake fadi kenan,
da taga kullum bashi da aiki sai kuka kuma baya cin abinci sai tasa masu gadi su nemo mata jabeer dan in alhj ya dawo ya tarar dashi a haka to bazai mata da kyau ba..