← Book details Rabo Ajali Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 41 OF 48

Sashe 41

Rabo Ajali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Suna fita oyizah rufo kofar ta dawo gurin Afeeyah tana dariyar murna,
pillown kan Afeeyah ta cire tana fadin yau taki ta kare,
yau zan karar da duk wata matsalata in huta da bakin ciki, tana daura pillown kan Afeeyah taji an murďa kofar,
da sauri ta zauna ta zame pillown tana dariya tace doctor ka dawo,
doctor musah ya kalleta sosai yace eh na dawo,
nazo daukarta muje ayi mata scanning daga nan zata wuce resting room,
zaifi kyau ki tafi gida hajiya saboda bama yarda kowa ya shiga dakin hutu in ba likita ko nurse ba,
oyizah tayi mishi wani irin kallo tace kana nufin ita kadai xamu bari a asibitin babu wanda zaiyi jinyarta sai kace marar gata,
doctor musah yace haka ka'idar take hajiya baki ga conditn din da take ciki ba, oyizah ta fara masifah tace wallhy baka isa ba, babu inda zaka kaita haka kawai zaka wani zo kayi min iyayi anan,
to anan zaka barta tunda ko ina ka kaita Allah ne zai bata lafiya ba kai ba,
yayi mata wani irin kallo sannan yasa aka shigo da wani gado yace hajiya aiki na nakeyi tunda ba ke kike biyana ba dan Allah ki barni inyi aiki na,
ya kalli nurses din yace ku daura ta muje, suka kinkimeta suka daurata akan gadon,
rike gadon oyizah tayi tana ta bala'i tana wallhy baza'a tafi da ita ko ina ba,
mutane suka taru a gurin anata bata hakuri amma tace ita sam babu inda za'a tafi da ita,
doctor musah da kanshi ya amshi gadon yasa iya karfinshi ya fara turawa oyizah na binsu tana bala'i kamar zararriya,
dr musa bai tsaya a ko ina ba sai office dinshi, da karfi ya bude kofar ya tura gadon haďe da bangajeta ta fadi kasa yayi saurin shigewa ya datso kofar,,
wani sabon bala'i oyizah ta dasa ta dinga masifa cikin daga murya,
babu wanda ya kalleta a asibitin kowa harkar gabanshi yakeyi saboda su a ganinsu mahaukaciya ce in ba mahaukaci ba waye zaiyi wannan daga cewa za'a kai patient resting room,
ita kuwa oyizah musabbabin tashin hankalinta shine yanzu Afeeyah tasan ita wacece in har tabar Afeeyah ta kara kwana a doron kasa to tabbas asirinta zai tonu dan zata iya farkawa a ko da yaushe,
(oyizah bata san ba tun yau Afeeyah tasan ko wacece ita ba, kuma bata san bayan Afeeyah akwai mutanen da suka san ko wacece ita kuma suna nan tunkarota cikin kankanin lokaci )
sai da ta gaji da masifar dan kanta sannan ta wuce gida cikin kunan rai...

Tana isa gida ta faďa ma alhj karya da gaskiya akan abun da doctor musah yayi mata,
alhj basheer yace safiya mutumin nan fa aikin shi ne ya fiki sanin abinda ya dace, oyizah tace babu abinda ya sani alhj kawai mu canza mata asibiti,
alhj basheer ya girgiza kanshi yace babu inda zan kaita a can zata zauna har Allah ya bata lafiya,
in ma yace kar wanda ya kara zuwa gurinta to na yarda dan nasan zai kula da ita sosai, oyizah ta tsaya tana kallon alhj basheer tana huci kamar bakar zakanya,
mikewa yayi ya fita daga gidan gaba ďaya ya barta tsaye kamar zata kurma ihu...

Mrs tijjani shattima....
[15/12 09:38] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 5⃣9⃣ By Aysha Ya'u Kurah

Kwanan Afeeyah uku a asibiti bata farfaďo ba, a cewar doctors buguwa tayi sosai kuma suna iyakacin kokarinsu gurin ganin ta farfaďo nan da yan kwanaki,
babu wanda ke zuwa dubata daga gida sai alhj basheer da Affan da har wannan ranar bai bar zubar da hawaye ba,
ba karamin damuwa alhj basheer yakeyi ba akan yawan kukan Affan,
gani yakeyi kamar yin kukan yanada nasaba da ciwonshi,
saida doctor musah ya kwantar mishi da hankali yace babu abinda ke damunshi may be ciwon matarshi ne ke sashi yawan kuka,
alhj yayi dariya da dr musa ya fada mishi haka, yace yanzu wannan da kwakwalwrshi bata da amfani har yake iya yin kuka dan wani nashi baida lafiya, kenan yasan zafin ciwo kuma yasan meye damuwa,,
doctor musah yace me zai hanashi yin kuka, alhj ni fa har yanzu kana bani mamaki akan wasu abubuwa da ka kasa fahimt-- wani irin kallo Affan yayi ma doctor musah nan da nan yayi saurin canza magana yace kamar ciwon Affan ka kasa fahimtar kullum yana samun cigaba dan wani lokacin yakanyi abubuwa irin na masu hankali,
alhj basheer yayi murmushi yace hakane doctor, Allah dai ya kara bashi lafiya,
dr musah yace ameen alhj, mikewa alhj basheer yayi yace to mu zamu wuce dan inada inda zani,
dr musah yace to sai anjima alhj, nan suka fita dr musah ya bi Affan da kallon mamaki...

Affan ne zaune a kan kujera a palour ya haďa kai da gwiwa yana kuka sosai harda sheshsheka,
mamakin al'amarin nayi a zuciyata nace shi kuwa wannan tababben ko kukan me yake yawan yi tun ranar da aka kai Afeeyah asibiti oho,,
a hankali naji yana faďin sai na dauki fansar kisarku, bazan kyale duk wanda yakeda hannu a cikin kisan ku ba, wannan yakin ni zan karasa shi cikin kankanin lokaci in shaa Allahu,
sosai yake kuka yana faďin wadannan kalaman,
cikin kidima na kureshi da ido a zuciyata nace anya wannan bai samu sauki ba,
anya ba basaja yakeyi ba kuwa?,

Da sauri na maida computer cikin kwakwalwrta baya zuwa ranar da Afeeyah ta aiwatar da ayukanta na karshe wanda yayi sanadiyyar zuwanta asibiti,
da sauri na ciro yar makallaliyar camerar da ke makale a dakin oyizah na kunna,
cikin mamaki na fara dauko muku rahoton abin da ke ciki,
da naso in boye muku kamar yadda Affan ya boye ma su daddy sai naji wayar "Badiyya Aliyu" tana gargadina akan in rubuta muku komai har coma, da fullstop. kamar yadda "bingel" takeyi,

Da sauri na dauki wayata na shiga typo muku abin da na gani mai ban mamaki,

cikin bacci naga Affan ya rike kanshi yana juyi anan inda yake kwance a kasa,
a hankali bakinshi ke motsi yana faďin umma,
Jabeer,
daddy,
can kuma naga ya matse kanshi da karfi yana faďin wayyo ummana,
sun kasheta,
sun kasheta,
sun kashetaaaaaaaa....
ya faďi da karfi hade da mikewa zaune zufa duk ta jika mishi jikin shi,
waige2 ya fara yi a rude yana fadin ina ne nan, waya kawoni nan,, ya maza ya mike ya buďe kofar dakin a firgice ya farayin hanyar dakin zeenatu,
ihu ya jiyo a side dinshi yayi saurin daukar hanyar gurin, yana zuwa kofar dakin yaji oyizah na faďin "kamar yadda na kawar da zeenatu da jabeer" kema haka zan kawar dake,
lekawa yayi dan ganin ko dawa take,
a gigice ya ja baya saboda ganin Afeeyah da yayi bakinta duk jini,
a ruďe yace yaushe jabeer ya mutu, me Afeeyah takeyi a nan gidan, yanzu ummanshi ta mutu kenan,
tambayoyin da ya dinga ma kanshi kenan idonshi na ambaliyar hawaye,
da sauri yaja baya ya boye ya shiga dawo da abubuwan da suka faru dashi shekaru uku da suka wuce,
babu abinda idonshi ke hangowa sai lokacin da ya tarar da kartin maza su biyu sun bankare mahaifiyarshi suna shirin shaketa da farin kyalle gabansu cike da kayayyakin tsafi mummy kuma tazo da wuka tana kokarin dab'a mata a wuya,, ,
shi dai yasan tun daga lokacin bai kara sanin inda hankalinshi yake ba sai yau da ya farka ya kuma tarar da wani tashin hankalin,
me jabeer yayi mata ta kasheshi,
wani irin kuka ya kufce mishi mai ban tausayi ya mike da niyyar komawa dakinshi ya ceci Afeeyah daga kaidin oyizah,
har yakai kofar ďakin ya hango oyizah da wata a bakin kofar,
da sauri ya juya yayi hanyar dakin da ya farka ya ganshi a ciki ko zai samu makamin da zai iya yakar ta dashi,
yana shiga dakin yaji karar waya, da kamar bazai dauka ba, sai kuma yayi saurin dauka,
ba"a bari yayi magana ba daga daya bangaren, murya yaji ta tsofaffi cikin rudewa tana cewa ina fatan kina nan lafiya Afeeyah,
nayi wani mummunan mafarki akanki,
ki tabbatar kin mike kinyi sallah dan komai na iya faruwa cikin daren nan,
a hankali Affan yace waye ke magana, daga daya bangaren kaka liman yace kai din waye,
Affan yace nine Affan, kai fa,
cikin mamaki kaka liman yace Affan nine, kaka liman ne na daura,
Affan ya fashe da kuka yace kaka kana ina aka kashe min jabeer, me jabeer yayi kuka bari aka kasheshi,
kaka liman yayi kabbara da karfi yace Affan ka dawo cikin hayyacinka,
Allah mai iko,
ka daina kuka wannan maganar ba ta waya bace yanzu ina matarka,
a gigice Affan yace wacece matata kaka,
kaka liman yace Afeeyah itace matarka wacce take dauke da cikinka,!
wacce ta yarda ta aureka cikin larura domin ta kubutar dakai daga cikin masifar da kake ciki,!
wacce ta fara zame ma matsalarka ciwon ido,!
nan ya takaita mishi duk yadda akayi ya auri Afeeyah da kuma irin taimkon da tayi mishi,
zaman dirshan Affan yayi yana kuka sosai yace kaka babu mamaki itama bazata rayu ba don gata can sun ritsata a daki zasu kasheta,
innalilliahi W.I.I.R kadai kaka liman ke iya fada yana sauraren kukan da Affan keyi,

a hankali yace ka kwantar hankalinki Allah zai kareta ko don Rabon dake jikinta,
karar da tayi ne yasa shi saurin kashe wayar ya mike zai fito yaji mahaifinshi ma ya fito, jingina yayi da bango yana zubar da hawaye har suka fita da ita suka sata cikin mota,
kara kira kaka liman yayi Affan ya dauka yace ta kasheta kaka, gashi can sun tafi kaita asibiti da daddy,
da sauri kaka liman yace bata mutu ba,
na fada maka bazata mutu ba sai wannan rabon ya taka duniya, kayi saurin bin su karka sake ka barta ita da wannan matar dan zata iya yi mata illah, kuma karka nuna ma kowa kaji sauki domin yin hakan kamar ka bata goma ne daya bata gyaru ba,
da sauri Affan ya fita, musababbin binsu asibitin kenan,
Chapter 41 · 0% Book details