← Book details Rabo Ajali Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 36 OF 48

Sashe 36

Rabo Ajali Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Tun ranar da salma ta mutu nutsuwa tayi ma oyizah tawaye,
kullum cikin mafarke2 take tana bakin cikin yadda akayi aka bada ďiyarta a cikin kungiyarsu ita kuma shegiyar kungiyar mai lakabin sabo da kaza baya hana a yanka ta, in ba haka ba ay sunsan yadda takeson yayanta kamar yar ranta,
a ranar da akayi uku ne ta fara shirin zuwa gurin meeting dan ta warware musu kuma a binciko mata dalilin da yasa wannan farin kyallen ya koma ďakinta.....

Mrs tijjani shattima...
[15/12 09:37] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 5⃣2⃣ By Aysha Ya'u Kurah

Karfe biyun dare suka hadu a gurin meeting kamar yadda suka saba,
oyizah na zaune gaban chummy bayan ta gama masifarta sai cika takeyi tana batsewa,
Chummy ta dafa kanta tace oyeee naji duk bayanan ki
, kuma na fahimci fushinki, amma kinsan mu nan duk wanda aka kawo baya tafiya ba tare da munsha jinin shi ba ko,
mistake din daga gareki yake tunda ke kika shimfiďa farin kyallen,
oyizah cikin fushi tace ba a dakina na shimfiďa ba my lord a dakin yarinyar da na bada anan na shimfiďa bansan yadda akayi ya dawo ďakina ba,
alhj sambo ya kalleta yace haba oyizah dan kin bada yarki daya shine kike ta wannan fushin,
ni yayana biyu na bayar da kannena biyu da nake matukar so,
a hassale oyizah tace abin da kake nema ne dole sai kayi wannan sacrifice din,
ni ay na riga na bada nawa wannan kyauta na bayar saboda kungiya taji dadi,
esther tace calm down oyee,
chummy tace barta ta cigaba,
ta manta duk abinda kungiya tayi mata ne, ta manta da irin rufin asirin da mukayi mata, ta manta da duk wani wanda zai tona asirinta mun kawar mata dashi saboda tasamu nutsuwa a gidan aurenta,
ta manta yadda muka mallaka mata alhj basheer
, ta manta yadda muka lalata rayuwar dan kishiyarta ita kuma muka mayar da ita matacciya alhali tana raye,
oyizah ta sunkuyar da kanta kasa tace am sorry my lord, ni ba fushi nayi ba,
kawai dai ina son in san wanda yayi min wannan aikin ne,

chummy ta janyo wani kokon tsafi ta fara bincikenta cikin kwarewa dan gano wanda ya canza farin kyallen,
a wannan lokacin kuma Afeeyah na zaune kan dadduma tana kallon gabas tana rokon Allah ya karesu daga dukkan sharrin masu sharri,

Babu irin duban da chummy batayi ba amma sam bata ga komai ba sai duhu da ya mamaye kwaryar, ajiye kwaryar tayi hannunta na rawa tace kaii oyee gaskiya na kasa gane ko waye, kar mu zurfafa bincike ko ma waye zamu gane shi wata rana, kedai kije ki cigaba da mulkinki kamar yadda kika saba tunda babu wanda ke taka miki birki,
cikin damuwa oyizah ta ďago da niyyar faďin damuwarta akan Afeeyah amma ta kasa,
daga ta bude baki zatayi magana sai taji wani abu na mata yawo a makoshinta, sai gab da asubahi suka fara bacewa suna komawa gidajensu,
har lokacin bakin oyizah naso ta furta sunan Afeeyah amma ta kasa,
gurin wata kwalba suka je wacce ke dauke da gunki a cikinta,
d'aga kwalbar chummy tayi tana dariya ta mayar ta ajiye tace haka kishiyarki zata dawwama babu motsi a duk inda take,
fanne da fanna dake cikin wata kwalba sukace saidai in bamu fita anan ba, wallhy muna fitowa zamu fasa kwalban nan,
oyizah ta buga glass din tace to dan ubanku ku fito mu gani,
fanne tayi dariya tace wit tym,
chummy tace rabu dasu oyee tafi gida sa'a na tare dake a ko da yaushe,
ta russuna kamar zata mata sujjada tace thank you my lord.....

Kwanan salma biyar da mutuwa har lokacin oyizah bata walwala, kullum sai tayi kuka saboda yawan mafarkin salma da takeyi,
alhj basheer da farida kaďai ke tausarta se kuwa a gurin meeting dinsu,
sam ta tsani ganin Afeeyah dan gani takeyi sanadiyyar Afeeyah ta rasa yarta, jira kawai takeyi ayi sadakar bakwai tayi wani aikin akanta dan wannan karan da hannunta zata kashe shegiya,
mugun shiri takeyi akan Afeeyah dan so takeyi tayi mutuwar wulakanci,,,,

Afeeyah kuwa hankalinta kwance yake dan kula sosai takeyi da mijinta da take ganin yar nutsuwa a tare dashi kwana biyun nan,
shi kanshi hankalinshi a kwance yake saboda daina ganin salma da yayi kwana biyu,

karfe 5 na yamma ta gama girkinta sukayi wanka suka shirya cikin kyakyawar shiga sai kamshi sukeyi, dakin oyizah suka shiga Afeeyah ta tsuguna ta gaisheta tayi mata ya hakuri,
ko kallonta oyizah batayi ba idonta nakan Affan tana hararar shi, boye fuskarshi yayi a bayan Afeeyah yana leken fuskar mummy da har lokacin bata daina hararar shi ba,
mikewa Afeeyah tayi tace sai anjima mummy,
oyizah ta bita da mugun tsaki tace za kici ubanki ne,

Ta wani corridor taja shi tace yau ta nan zamu bi,
kasan tunda nazo gidan nan ban hau gurin nan ba,
yayi dariya yace to muje amma fa mummy tace akwai su lions a gurin,
Afeeyah tace haba dai babu komai muje may be basa so ka hau ka fado ne,
runtse idonshi yayi yace muje amma bazan bude ido na ba, dariya Afeeyah tayi taja hannunshi suka hau can saman gidan,

sakin hannunshi tayi da sauri tana fadin Wowww amma gurin nan ya hadu,
bude hannunta tayi ta lumshe idonta tana shakar iskar gurin flowers sai kaďawa sukeyi,
da gudu taje bayanshi ta fara mishi cakulkuli tana faďin ka buďe idonka ka gani babu komai a gurin sai flowers masu kamshi, dariya yake ta kyakyatawa sannan ya buďe idonshi a hankali,
wasu shuďaďďun abubuwa ya dinga gani suna mishi yawo a cikin kwakwalarshi da kwayar idonshi,
sosai yake ganin abubuwan da suka taba faruwa a gurin kuma yake ganinsu kamar zanen cartoon,
fuskar zeenatu ce take mishi gizo yanata so ya gano ko wacece saboda dishi2 yake ganinta,
rike kanshi yayi dasauri bakinshi na rawa a hankali ya furta
U-M-M-A,..... ..

Mrs tijjani shattima...
[15/12 09:37] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 5⃣3⃣ By Aysha Ya'u Kurah

Maimaita sunan ya dinga yi yana ja da baya kanshi na juyawa saboda yadda abubuwan ke zuwan mishi cikin kwakwalwarshi,
a firgice Afeeyah ta kamashi tana faďin me ya faru,
girgiza kanshi yayi da karfi ya runtse idonshi yace dan Allah ki sakko dani ki kaini ďaki,
Afeeyah cikin tsoro ta rike hannunshi taja shi tana waigen gurin ko itama zata ga abin da yake gani,
daki ta wuce dashi ta zaunar dashi ta tsuguna a gabanshi har lokacin bai buďe idonshi,
a hankali tace ka buďe idonka,
kara runtse idon yayi yana girgiza kanshi,
Afeeyah tace a daki fa muke ka bude idonka ka gani babu komai anan,
a hankali ya fara bude idonshi har ya bude su gaba ďaya ya saukesu a kan Afeeyah,
Afeeyah tace kaga ni ba komai ko,
ya gyaďa mata kai, tace to me ka gani a can saman,
ya ďaga kanshi sama yace babu komai sai fan,
Afeeyah ta dawo kusa dashi tace ina nufin a sama inda muka je, rufe idonshi yayi shi kanshi yana son tuno abinda ya gani duk da bai gansu clear ba amma yasan ya gane fuskar ďaya a cikinsu,,
bude idonshi yayi dan ya kasa tuno fuskar da ya ambaci sunanta a sama,
kallon Afeeyah yayi yace ni ban ga komai ba,
Afeeyah tace kagani mana, baza dai ka faďa min ba ko,
ya tabe baki yace ni na manta kome na gani,
Afeeyah tace to shikenan, tashi muje muyi sallah magriba tayi,
ba musu ya mike ya bita fuskar da ya gani a sama tana ta mishi gizo amma sam ya kasa tuna ta....

Zaune take a gefen gadonta rike da turaren da kaka liman ya bata a hannunta tana shafa shi tana addu'a kamar yadda ta saba,
tofe jikin Affan tayi da addu'a sannan ta kwanta tana istigfari har bacci yayi gaba da ita,,,,

Mafarki*****
Chapter 36 · 0% Book details