← Book details Rabo Ajali Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 48

Sashe 21

Rabo Ajali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hakan ta kasance da Afeeyah, wannan tsawar da akayi ita ta farkar da ita daga baccin da bata san tayi ba mai cike da mafarkai,
agogon wayarta ta duba taga 9:56 ta zauna tana sauraron zubar ruwan sama tana kara duba agogo kirjinta na harbawa da sauri,
10:20 ta kira wayar jabeer taji ta akashe, a hankali ta koma bayan hajja ta kwanta tana duba wayarta ko zata ji kiranshi shuru taji har 11 ta gota,
a hankali ta fara rero kuka tana kiran sunanshi,
kamar a mafarki hajja taji kukan ta farka da sauri tace yanzu ke Afeeya har yanzu baki bar kukan nan ba,
wani irin iskanci ne wannan,
Afeeyah tace hajja sha ďaya fa ta wuce kuma shi ya cemin goma da wani abu zai dawo,
hajja cikin masifa tace shikenan kuma ana wannan ruwan in ya dawo sai yaki zuwa ya huta yazo gurinki saboda gaki yar gwal ko,
Afeeyah ta shige jikin hajja tana kuka sosai tace hajja fa ya kashe wayar shi ne, kuma tun jiya fa ban ganshi ba, dan Allah ki taimaka min wallhy bazan iya bacci ba in ban ganshi ba,
hajja taji tausayinta sosai tace to yi shuru ya isa haka,
kinga yanzu dare yayi babu mamaki wayarshi ta mutu babu charge kuma bayason yazo ya sameki kina bacci kinga kuma ruwa akeyi kina son ya fito cikin ruwan nan ne, Afeeyah ta girgiza kanta,
hajja tace to ki mishi uzuri gobe nasan tun kafin ki tashi daga bacci zaizo kinji, Afeeyah ta gyada kanta tana share hawaye haďe da ajiyar zuciya,
hajja ta kwantar da ita tace yi addu'a kiyi bacci,
Afeeyah ta fara karanto adduoi hawaye na zubo mata ta gefen idonta a zuciyarta tana jin haushin jabeer na kin cika alkawarin da yayi mata, yanzu haka zanyi bacci banganka ba yaya jabeer, atlst ko waya ya kunna naji muryarshi zan dan rage wani zafin abinda ta dinga fadi a zuciyarta kenan, baccin ranar a gurin Afeeya rabi da rabi ne, saboda duk farkawa saita duba wayarta taga ko ya kirata,
( Allah sarki Afee zanso ace kinsan gani da muryar jabeer ma bazaki kara ji ba bare har kiga missd call dinshi,)

Abida ma juyi take tayi idonta na kan agogo, babu irin kiran da batayi ma wayar jabeer ba amma taki shiga,
Alhj bara'u yace Abida ya kamata ki cire duk wasu tunani a ranki kiyi addu'a ki kwanta kiyi bacci in shaa Allahu babu abinda ya sameshi babu mamaki mota ce ta bashi matsala,
Abida tace matsalar mota sai tasa ya kashe wayarshi yasan dole hankalin mu zai tashi alhj,
alhj bara'u da shi kanshi daurewa yakeyi yace kinsan sharrin netwk mu zuba ido zuwa da safe mu gani, Abida dai uhum kawai tace saboda yadda takejin nauyi a kirjinta, rungumeta yayi ta baya yana faďa mata kalamai masu kwantar da hankali dan in ya bari tasan shima hankalinshi a tashe yake to fa zata kara daga hankalinta fiye dashi ma,
Kaka liman ma ya kira har sau uku yaji ko ya iso,
shima hankalinshi a tashe yake saboda jin har lokacin jabeer bai isa gida ba...

Mrs tijjani shattima....
[15/12 09:34] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 3⃣1⃣ By Aysha Ya'u Kurah

Washe gari tunda alhj Bara'u ya idar da sallah yake zaune kan dadduma,
hankali tashe ya kalli Abida da ta zuba tagumi tana jan carbi yace Abida har yanzu wayar yaron nan bata shiga ba ko,
Abida ta gyada kanta kawai tana kallonshi,
yace innalillahi wa inna ilaihir rajiun, Allah dai yasa jabeer lfy yake dan bai taba irin wannan abun ba, ko wayarshi nada matsalar charge ay duk inda yake bazai rasa wayar da zai kiramu ya sanar damu halin da yake ciki ba,
Abida tace uhummm zuciyata tana faďamin duk inda jabeer yake ba lafiya yake ba,
alhj bara'u yace ki daina faďin haka, haka kawai zuciyarki ta dinga kitsa miki mugayen tunani, ya mike tsaye yana duba lokaci yaga 7 har ta wuce ya fita daga dakin yayi hanyar waje,
Abida ta share kwallar data ďan fito daga idonta tace ya Allah ka sassauta min zafin da nake ji a zuciyata ka bani ikon jure duk wani abu da zanji game da jabeer,

Malam Atiku na kwance idonshi a lumshe da radio a gefenshi yanajin labaran karfe 7 kamar yadda ya saba kullum, bayan an gama labarai akan halin da kasarmu take ciki da kuma na kasashen ketare, sai aka sako labaran kwallon kafa, cikin kosawa ya mika hannu zai kashe radion saboda sam labaran kwallon kafa basa gabanshi,
tsayar da hannunshi yayi sakamakon jin sanarwar hatsari da akayi anan hanyar shigowa gari wanda akace an tsinci gawar saurayi mai suna Jabeer Bara'u, wadanda suka cinci gawar sunyi saurin mikashi ga hukumar yansanda, yanzu haka yana can asibitin Aminu kano, ga duk wanda yaji kuma yasan inda yan'uwan baw----- ay malam Atiku bai karasa sauraro ba ya diro daga kan gado yana faďin innalillahi wa inna ilaihir rajiun,
ko takalmi baisa a kafarshi ba ya fita waje da sauri jikinshi na rawa,
a kofar gida ya samu alhj bara'u zaune kan dakali, da sauri alhj bara'u ya mike yace malam Atiku lafiya na ganka haka ko takalmi babu,
Malam Atiku ya saki ajiyar zuciya yace tunda na ganka zaune lfy lau ay alhamdullh, wallhy wata sanarwa naji yanzu a radio akan wani hatsari da ya faru a daren jiya kuma sai naji an kira sunan jabeer shiyasa hankalina ya tashi,
Alhj Bara'u ya mike yana salati kamar zararre, malam atiku yace alhj lafy,
Alhj bara'u baki na rawa yace jabeer dina ne,
jabeer dina ne wallhy, tun jiya muke neman layinshi bamu samu ba, innalillahi wa inna ilaihir rajiun,
malam atiku yace lahaulu wala kuwwat illa billah, alhj bara'u ya rike hannun malam atiku ya rasa ta inda zai fara sai janshi yakeyi yana fadin muje asibitin da suka ce, malam Atiku zaiyi magana parking din motar alhj basheer ya dakatar dashi,
da sauri ya fito yace lafy alhj bara'u ,
alhj bara'u ido zuru2 yace jabeer ya tafi,
alhj basheer cikin rudewa yace ina ya tafi,
malam atiku yace karka yanke hukunci alhj muje asibitin tukunna, in shaa Allahu ma bashi bane, alhj basheer yace wani asibiti,
malam atiku ya fada mishi abinda yaji a radio, alhj basheer da sauri yace kuzo mu tafi asibitin,
alhj bara'u da bakinshi bai daina salati ba ya shiga motar jikinshi a sanyaye suka wuce Aminu kano T.H,

Tunda suka shiga gaban alhj bara'u ke faduwa har suka karasa cikin mortuary, suna shiga aka nuna musu D.L din jabeer sannan aka karasa dasu inda yake,
Juyawa alhj bara'u yayi da ya kalli gawar sau ďaya ya fara addua cikin sambatu kamar tababbe,
D.L din kawai yake kallo yana jujjuyashi yanaso ya gasgata shin wannan gawar ďanshi ne da gaske ko mafarki yakeyi,
dafashi alhj basheer yayi yana zubar da hawaye yace alhj muje kayi signn mu amshi gawarshi muje ayi mishi sutura,
alhj bara'u bai kalleshi ba yace kaima mahaifinshi kaje kayi signn din, Allah ya amshi bakuncinshi yana gama faďin haka ya fita,
nurse din dake tsaye a gurin ta fashe da kuka tace alhj kuje kawai no need, Allah ya jikanshi da rahama,
nan aka gunguro gawar jabeer aka sata a ambulance suka wuce gida cikin jimami suna kallon alhj bara'u da ya kurawa d.l din jabeer ido,
kallon motar aka dinga yi a layin wasu suka bita dan ganin inda zata tsaya, motar na tsayawa a kofar gidan, alhj bara'u ya fito da sauri ya shiga ciki,
a parlor ya tarar da Abida Amirah na tsaye a kanta da ruwan tea da magani a hannunta, kallon Amirah yayi kamar babu abinda ya faru yace har yanzu baki shirya kin wuce makaranta ba,
Amirah tace nayi wanka baba yanzu zan gama in---, sallamar su malam Atiku da wadanda suka shigo da gawar jabeer ita ta hana amirah karasawa,
da sauri Abida ta mike tabisu da ido har aka shimfiďe gawar jabeer a kasa,
cikin firgici ta karasa kan gawar zuciyarta na dukan uku uku ta tsuguna ta buďe fuskar da tayi faca2 da jini, runtse idonta tayi da sauri tana fitar da wani irin numfashi tace nasani jabeer, zuciyata ta sanar dani, Alhamdullilah da Allah yasa aka tsinci gawarka akan lokaci, Allah ya rahamceka jabeer, yadda ka faranta mana kayi mana biyayya Allah ya faranta maka a cikin kabarinka dan nan ne gidanka na gaskiya, Allah ya sanya aljanna firdausi ta zama makoma a gareka,
ta shafa fuskarshi a hankali tace na yafe maka,
na yafe maka jabeer,
ta mike da sauri ta wuce daki alhj bara'u ya bita,
Amirah kasa gasgata gawar tayi dan gaba daya ta kasa fahimtar abinda ake nufi, ta kalli su alhj basheer da suke sharar hawaye tace daddy, Abba, me ya samu yaya jabeer, alhj basheer yace Amirah addua zakuyi mishi dan wanda ya fimu sanshi ya karbi abinshi,
Amirah ta saki kofin hannunta ta tsuguna a gabanshi tana kuka mai tsanani tana kiran sunanshi,
da kyar alhj basheer ya rarrasheta yasa Dayyaba dake tsaye tana kuka ta shiga da ita ciki,

Mahmud kanin Afeeyah ya shiga gida da gudu ya ajiye biredin da ya siyo a tsakar gida ya karasa ďakin hajja,
hajja na zaune tana gyaran wake, Afeeya kuma tana kwance jikinta ya ďau zafi sosai saboda zazzabi, fadowa dakin mahmud yayi, hajja tace haba mahmu irin wannan shigowar ba sallama ay sai ka tsoratani, yace hajja motar gawa ta asibiti na gani kofar gidan alhj bara'u kuma naji mutane suna cewa yaya jab-- Afeeya ta diro daga kan gado tayi ma mahmud wani irin riko tace me ya sameshi, mahmud cikin jin zafin rikon yace ban sani ba mutane sunce sunga an fito dashi cikin jini...

Mrs tijjani shattima...
[15/12 09:34] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 3⃣2⃣ By Aysha Ya'u Kurah
Chapter 21 · 0% Book details