Sashe 38
Rabo Ajali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gurin Affan ta wuce yana zaune yana kallon kifayen dake cikin fishpond,
runtse idonta tayi saboda tuno mafarkin da tayi,
da sauri ta mike tayi hanyar ďaki tsigar jikinta sai tashi takeyi,
da sauri ya biyota dakin yana tambayarta me ya faru,
a hankali take maida numfashi tace wallhy na tsani ganin kifayen nan,
dan Allah muje gurin daddy yasa a fitar dasu daga gidan nan,
Affan ya bata rai yace kifin mummy ne fa, bazata bari a fitar dasu ba,
Afeeyah ta fara kakarin amai ta mike ta shiga bayi tana kakarin karya tana kuka kamar zata mutu,
da gudu ya tafi dakin daddy yana fadin daddy kazo Afeeyah zata mutu,
da sauri ya tashi ya fita yace tana ina, Affan yace tana bayi daddy,
da gudu ya shiga dakin ya tarar da ita kofar bayin tana haki kamar da gaske,
karasowa yayi da sauri yace me ya sameki, Affan yace daddy wai kifayen nan ne ke bata tsoro,
Alhj basheer yace wani irin tsoro kuma,
Afeeyah tace wallhy daddy kullum sai nayi mafarkinsu bana iya bacci da daddare,
alhj basheer yace subhanallahi to gaskiya gara a fitar dasu daga gidannan dan kar su shafi lafiyar dan cikin ki,
oyizah da ta shigo dakin dan taci uban Afeeyah akan abinda tayi ma farida tace baka isa ba wallhy, babu wanda zai fitar min da kifi,
ance dole sai kinje gurin ne bare ki gansu,
Afeeyah ta kara narkewa tace amma mummy ay a gidan suke, dan Allah kiyi hakuri a fitar dasu wallahy suna firgitani cikin dare,
oyizah tace to zanga uban da ya isa ya fitar min da kifaye daga cikin gidan nan,
alhj basheer yace haba safiya, ni bansan amfanin kifayen nan ba, ace shekara uku ana kiwon kifaye basa girma saidai su dinga cin abinci kullum, gaskiya yanzu za'a fitar dasu daga gidan nan kije can fili na na Na'ibawa ki cigaba da kiwata su,
oyizah tace haba alhj yanzu saboda yarinyar nan tace bata son abu shin--- yayi saurin katseta yace saboda kar mu shiga hakkinta ita da abin da ke cikinta karki fassara maganar dan Allah yasa kai ya fita..,
oyizah ta kalli Afeeyah ranta a bace ji takeyi kamar ta shaketa ta huta,
mikewa Afeeyah tayi tana gyara jikinta tana murmushi tace mummy bakiji daddy na kiranki bane,
oyizah ta harareta sama da kasa tayi kwafa tace billahil lazi sai kin gane ba'a shiga gonata, tasa kai ta fita,
Afeeyah tace gonarki na nawa kuma,
ta karshen ta rage in shiga in saki nometa da hannunki..
Karashe 54
Ba karamin tataburza akasha da oyizah ba gurin fitar da kifayen nan,
saida alhj basheer ya nuna mata matukar bacin ranshi sannan ta yarda aka kwashesu ruwan ciki na yauki da kyar aka gama kwashewa,
ana sakin ruwan wani irin wari ya gauraye gurin kowa a gurin saida ya toshe hancinshi,
da gudu mati ya ruga ciki ya samu oyizah zaune tayi tagumi yace hajiya an gama kwashewa,
wani irin harara ta sakar mishi cikin tsawa tace dazu saboda ka rik'a shine ka hake flowers din dana hanaku tabawa ko,
mati ya marairaice fuska yace alqur'an hajiya sani akayi,
tace ka fada min abinda ka hako a gurin, yace na rantse da---- babu abinda ya hako mummy, Afeeyah ta katseta, tace a gabana ya gama gyarawa akwai abin da kika binne a gurin ne,
oyizah ta dafe kanta ta dago tace kan ubanki na binne,
Afeeyah tayi gaba tana dariya tace kan ubana tauri gareshi,
oyizah ta kalli mati tace bace min da gani banza shashasha,
da sauri ya mike ya fita yana bata hakuri,
wani irin juyawa taji kanta nayi saboda abin da ke shirin faruwa da ita yau,
farin cikinta daya da mati yace bai hako komai ba,
to ya zatayi da wadanan kifayen tsafin nata da alhj yasa a fitar dasu daga cikin gidan,
duuffffffff taji saukar mutane akanta suna maida numfashi,
da sauri ta hankade farida da Afeeyah ta kalli su tanimu tace lafiya kuka shigo min parlour,
a ruďe farida tace mummy kifayen nan sun bace a cikin kwanon da aka sasu.......
Mrs tijjani shattima.....
[15/12 09:37] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 5⃣5⃣ By Aysha Ya'u Kurah
Zaro ido oyizah tayi tace kamar yaya sun bace,
Afeeyah ta kalli alhj basheer da ya fito yana gyara hula tayi saurin cewa wallahi bacewa sukayi mummy,
haba shiyasa suke tsorata ni cikin dare ashe ba kifaye bane,
alhj basheer ya karaso da sauri yace kifayen ne suka bace,
oyizah ta galla ma su Tanimu harara sum sum suka fice ta juyo ta kalli alhj basheer tace iskancin su ne ni nace ma wanda ya kwashe kifin ya dauka na bashi shine dan basu gansu ba suke tunanin sun bace, to ina zasu,
Fareeeda tace wallhy tall--- oyizah tayi saurin katseta tace dalla rufe mana baki, shekarun su nawa a gidannan kin taba ganin sun bace, dallah ku wuce ku ba mutane guri,
Afeeyah ta ja hannun Affan da jikinshi ke kyarma suka wuce daki a zuciyarta tace 99days 4 the thief muje zuwa, Allah dai ya kara bani sa'a...
Tun karfe hudu na yamma oyizah ke gurin chummy cikin matsananciyar damuwa tana faďa mata anyi destroying fishpond dinta na tsafi,
dariya chummy tayi sannan ta buga kasa nan take ya tsage ruwa haďe da kifaye suka fara fitowa daga ciki, saida suka gama fitowa tsaff sannan suka haďe kansu guri ďaya,
oyizah tayi murmushin jin dadi tace ashe suna nan,
har hankali na ya kwanta, bacewarsu ba karamin daga hankali na yayi ba dan ba karamin taimako na sukeyi ba,
chummy tayi dariya mai karfi tace fitarsu a gidanki tonan asirinki ne saboda haka kisan duk yadda zakiyi ki mayar dasu gidan nan Affan ya dinga ganinsu kullum,
oyizah tayi tagumi tace ta yaya zan mayar dasu bayan alhj da kanshi yace a fitar dasu,
yanzu ina komawa dasu zai fara zargin wani abu,
chummy tace karki damu, akwai abun da zan baki kisa mishi a abinci daga yaci shikenan ko yagansu hankalinshi bazai kawo su bane,
oyizah tayi dariyar jin daďi tana faďin thank u my lord,,
mikewa oyizah tayi ta shigo da wani yaron da zasu sha jininshi a gurin meeting,
da ganin yaron kasan mugun takadiri ne dan ko gezau baiyi ba idonshi a soye babu alamar hawaye,
dakyar ya tsuguna a gabansu,
chummy ta harareshi sannan ta umurceshi da ya miko mata kafafuwanshi,
tirjewa yayi yaki mikowa, babu yadda batayi ba akan ya miko kafafuwanshi tayi wani aikin dasu yaron nan yaki,
kwala kiran BULADUNA tayi nan suka shigo shida abokin aikinshi,
cikin isa ta umurcesu da su kamo yaron su kawoshi gabanta,
da karfinsu suka fara kokarin kama shi yana tirje musu yana tokarinsu da hannu, sai sun daukeshi sunyi sama dashi sai yasa iya karfinshi ya zille ya fado kasa,
daukar da sukayi mishi na karshe ne yasashi wani irin kukan kura ya hankaďe buladuna yayi baya,
tartsasssssss sukaji dukansu suka duba gurin da sauri,
glass din da fanne da fanna ke ciki ne yayi tarwatse ya bullo tun daga bayan buladuna har cikinshi, nan take ya fadi kasa matacce, da sauri su chummy suka yo kanshi suna kiran sunanshi,
su kuwa su fanne cikin azama suka fito cikin glass suka nufi gurin yaron da aka kamo da niyyar taimaka mishi ya gudu,
cikin tausayawa yace ku meyasa bazaku zo mu tafi tare ba,
fanne cikin sauri tace mu matattune gawar mu ta dade a rami kai kuwa ba'a riga an birne gangar jikinka ba kayi saurin komawa gida,
da sauri yace waye ya kawo ku nan,
fanna tace mahaifin mu ne Alhj sambo ministern Abuja na yanzu,
kafin yaron yayi magana ya hango su chummy sun doso su suna kokarin kama su fanne,
da sauri kurwar yaron tabi ta inda su fanne suka nuna mai ya bace daga gurin,
cikin kunan rai chummy ta ciro sandar tsafinta ta fara nuna su fanne dashi,
zagayen dakin suka farayi har suka kai inda kwalbar gunkin zeenatu take,
da sauri fanne tasa hannu ta dauki kwalbar,
wani irin ihu oyizah tasa tace karki fasa, karki fasa,
zan taimakeku in maida ku gidan ku, fanna tace fanne fasa da sauri saboda mu dama a mace muke gurin wa zata maida mu,
kafin chummy ta cimma fanne har ta fasa wannan kwalbar ta karya gunkin ciki,
zama oyizah tayi a gurin tana girgiza kanta tana fadin shikenan, shikenan my lord,
sai da nace miki mu gama da yaran nan saboda nasan zasu iya zame mana matsala, yanzu nasan duk inda zeenatu take ta farfado,
chummy bata ba oyizah amsa ba saida ta tabbatar ta kwantar da fanne da fanna sannan tace yau dinnan zan gama dasu, ki kwantar da hankakinki dan sun fasa kwalbar a banza dan babu wanda yake tunata bare har yayi mata adduar da zaisa ta gama dawowa hayyacinta,,
yanzun nan zan kara yin aikin da yafi wancan akanta,
oyizah ta saki ajiyar zuciya tace nagode my lord..
Afeeyah na zaune tana lazumi, tunda ta idar da sallar la'asar bata tashi daga kan daddumar ba sai gurin biyar,
shafa addu'ar tayi ta mike ta nade daddumar sannan ta zauna a kasa a gefen gadonta ta tura hannunta karkashin gadon ta zaro zanin da ta kunshe damon nan a ciki,
a hankali ta warwareshi ta nade hannunta da leda cikin dakewar zuciya ta fara kakkabe kasar tana kokarin bude bakin damon,
cikin sa'a ta budeshi sai wari yakeyi ta karkatar da bakin ta girgizah shi, nan wata katuwar laya ta faďo kasa,
da sauri ta ajiye wannan damon ta naďeshi cikin zanin ta dauki layar ta warwareta,
babu abinda ta gane a cikin rubutun sai sunan zeenatu,
nade layar tayi ta mike ta fita da wannan damon ta kulleshi a leda takai main bolar gidan sannan ta dawo ta kona layar ta tattara tokar ta zubata a magudanar ruwa...
★ Magaryah Nijar★
runtse idonta tayi saboda tuno mafarkin da tayi,
da sauri ta mike tayi hanyar ďaki tsigar jikinta sai tashi takeyi,
da sauri ya biyota dakin yana tambayarta me ya faru,
a hankali take maida numfashi tace wallhy na tsani ganin kifayen nan,
dan Allah muje gurin daddy yasa a fitar dasu daga gidan nan,
Affan ya bata rai yace kifin mummy ne fa, bazata bari a fitar dasu ba,
Afeeyah ta fara kakarin amai ta mike ta shiga bayi tana kakarin karya tana kuka kamar zata mutu,
da gudu ya tafi dakin daddy yana fadin daddy kazo Afeeyah zata mutu,
da sauri ya tashi ya fita yace tana ina, Affan yace tana bayi daddy,
da gudu ya shiga dakin ya tarar da ita kofar bayin tana haki kamar da gaske,
karasowa yayi da sauri yace me ya sameki, Affan yace daddy wai kifayen nan ne ke bata tsoro,
Alhj basheer yace wani irin tsoro kuma,
Afeeyah tace wallhy daddy kullum sai nayi mafarkinsu bana iya bacci da daddare,
alhj basheer yace subhanallahi to gaskiya gara a fitar dasu daga gidannan dan kar su shafi lafiyar dan cikin ki,
oyizah da ta shigo dakin dan taci uban Afeeyah akan abinda tayi ma farida tace baka isa ba wallhy, babu wanda zai fitar min da kifi,
ance dole sai kinje gurin ne bare ki gansu,
Afeeyah ta kara narkewa tace amma mummy ay a gidan suke, dan Allah kiyi hakuri a fitar dasu wallahy suna firgitani cikin dare,
oyizah tace to zanga uban da ya isa ya fitar min da kifaye daga cikin gidan nan,
alhj basheer yace haba safiya, ni bansan amfanin kifayen nan ba, ace shekara uku ana kiwon kifaye basa girma saidai su dinga cin abinci kullum, gaskiya yanzu za'a fitar dasu daga gidan nan kije can fili na na Na'ibawa ki cigaba da kiwata su,
oyizah tace haba alhj yanzu saboda yarinyar nan tace bata son abu shin--- yayi saurin katseta yace saboda kar mu shiga hakkinta ita da abin da ke cikinta karki fassara maganar dan Allah yasa kai ya fita..,
oyizah ta kalli Afeeyah ranta a bace ji takeyi kamar ta shaketa ta huta,
mikewa Afeeyah tayi tana gyara jikinta tana murmushi tace mummy bakiji daddy na kiranki bane,
oyizah ta harareta sama da kasa tayi kwafa tace billahil lazi sai kin gane ba'a shiga gonata, tasa kai ta fita,
Afeeyah tace gonarki na nawa kuma,
ta karshen ta rage in shiga in saki nometa da hannunki..
Karashe 54
Ba karamin tataburza akasha da oyizah ba gurin fitar da kifayen nan,
saida alhj basheer ya nuna mata matukar bacin ranshi sannan ta yarda aka kwashesu ruwan ciki na yauki da kyar aka gama kwashewa,
ana sakin ruwan wani irin wari ya gauraye gurin kowa a gurin saida ya toshe hancinshi,
da gudu mati ya ruga ciki ya samu oyizah zaune tayi tagumi yace hajiya an gama kwashewa,
wani irin harara ta sakar mishi cikin tsawa tace dazu saboda ka rik'a shine ka hake flowers din dana hanaku tabawa ko,
mati ya marairaice fuska yace alqur'an hajiya sani akayi,
tace ka fada min abinda ka hako a gurin, yace na rantse da---- babu abinda ya hako mummy, Afeeyah ta katseta, tace a gabana ya gama gyarawa akwai abin da kika binne a gurin ne,
oyizah ta dafe kanta ta dago tace kan ubanki na binne,
Afeeyah tayi gaba tana dariya tace kan ubana tauri gareshi,
oyizah ta kalli mati tace bace min da gani banza shashasha,
da sauri ya mike ya fita yana bata hakuri,
wani irin juyawa taji kanta nayi saboda abin da ke shirin faruwa da ita yau,
farin cikinta daya da mati yace bai hako komai ba,
to ya zatayi da wadanan kifayen tsafin nata da alhj yasa a fitar dasu daga cikin gidan,
duuffffffff taji saukar mutane akanta suna maida numfashi,
da sauri ta hankade farida da Afeeyah ta kalli su tanimu tace lafiya kuka shigo min parlour,
a ruďe farida tace mummy kifayen nan sun bace a cikin kwanon da aka sasu.......
Mrs tijjani shattima.....
[15/12 09:37] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 5⃣5⃣ By Aysha Ya'u Kurah
Zaro ido oyizah tayi tace kamar yaya sun bace,
Afeeyah ta kalli alhj basheer da ya fito yana gyara hula tayi saurin cewa wallahi bacewa sukayi mummy,
haba shiyasa suke tsorata ni cikin dare ashe ba kifaye bane,
alhj basheer ya karaso da sauri yace kifayen ne suka bace,
oyizah ta galla ma su Tanimu harara sum sum suka fice ta juyo ta kalli alhj basheer tace iskancin su ne ni nace ma wanda ya kwashe kifin ya dauka na bashi shine dan basu gansu ba suke tunanin sun bace, to ina zasu,
Fareeeda tace wallhy tall--- oyizah tayi saurin katseta tace dalla rufe mana baki, shekarun su nawa a gidannan kin taba ganin sun bace, dallah ku wuce ku ba mutane guri,
Afeeyah ta ja hannun Affan da jikinshi ke kyarma suka wuce daki a zuciyarta tace 99days 4 the thief muje zuwa, Allah dai ya kara bani sa'a...
Tun karfe hudu na yamma oyizah ke gurin chummy cikin matsananciyar damuwa tana faďa mata anyi destroying fishpond dinta na tsafi,
dariya chummy tayi sannan ta buga kasa nan take ya tsage ruwa haďe da kifaye suka fara fitowa daga ciki, saida suka gama fitowa tsaff sannan suka haďe kansu guri ďaya,
oyizah tayi murmushin jin dadi tace ashe suna nan,
har hankali na ya kwanta, bacewarsu ba karamin daga hankali na yayi ba dan ba karamin taimako na sukeyi ba,
chummy tayi dariya mai karfi tace fitarsu a gidanki tonan asirinki ne saboda haka kisan duk yadda zakiyi ki mayar dasu gidan nan Affan ya dinga ganinsu kullum,
oyizah tayi tagumi tace ta yaya zan mayar dasu bayan alhj da kanshi yace a fitar dasu,
yanzu ina komawa dasu zai fara zargin wani abu,
chummy tace karki damu, akwai abun da zan baki kisa mishi a abinci daga yaci shikenan ko yagansu hankalinshi bazai kawo su bane,
oyizah tayi dariyar jin daďi tana faďin thank u my lord,,
mikewa oyizah tayi ta shigo da wani yaron da zasu sha jininshi a gurin meeting,
da ganin yaron kasan mugun takadiri ne dan ko gezau baiyi ba idonshi a soye babu alamar hawaye,
dakyar ya tsuguna a gabansu,
chummy ta harareshi sannan ta umurceshi da ya miko mata kafafuwanshi,
tirjewa yayi yaki mikowa, babu yadda batayi ba akan ya miko kafafuwanshi tayi wani aikin dasu yaron nan yaki,
kwala kiran BULADUNA tayi nan suka shigo shida abokin aikinshi,
cikin isa ta umurcesu da su kamo yaron su kawoshi gabanta,
da karfinsu suka fara kokarin kama shi yana tirje musu yana tokarinsu da hannu, sai sun daukeshi sunyi sama dashi sai yasa iya karfinshi ya zille ya fado kasa,
daukar da sukayi mishi na karshe ne yasashi wani irin kukan kura ya hankaďe buladuna yayi baya,
tartsasssssss sukaji dukansu suka duba gurin da sauri,
glass din da fanne da fanna ke ciki ne yayi tarwatse ya bullo tun daga bayan buladuna har cikinshi, nan take ya fadi kasa matacce, da sauri su chummy suka yo kanshi suna kiran sunanshi,
su kuwa su fanne cikin azama suka fito cikin glass suka nufi gurin yaron da aka kamo da niyyar taimaka mishi ya gudu,
cikin tausayawa yace ku meyasa bazaku zo mu tafi tare ba,
fanne cikin sauri tace mu matattune gawar mu ta dade a rami kai kuwa ba'a riga an birne gangar jikinka ba kayi saurin komawa gida,
da sauri yace waye ya kawo ku nan,
fanna tace mahaifin mu ne Alhj sambo ministern Abuja na yanzu,
kafin yaron yayi magana ya hango su chummy sun doso su suna kokarin kama su fanne,
da sauri kurwar yaron tabi ta inda su fanne suka nuna mai ya bace daga gurin,
cikin kunan rai chummy ta ciro sandar tsafinta ta fara nuna su fanne dashi,
zagayen dakin suka farayi har suka kai inda kwalbar gunkin zeenatu take,
da sauri fanne tasa hannu ta dauki kwalbar,
wani irin ihu oyizah tasa tace karki fasa, karki fasa,
zan taimakeku in maida ku gidan ku, fanna tace fanne fasa da sauri saboda mu dama a mace muke gurin wa zata maida mu,
kafin chummy ta cimma fanne har ta fasa wannan kwalbar ta karya gunkin ciki,
zama oyizah tayi a gurin tana girgiza kanta tana fadin shikenan, shikenan my lord,
sai da nace miki mu gama da yaran nan saboda nasan zasu iya zame mana matsala, yanzu nasan duk inda zeenatu take ta farfado,
chummy bata ba oyizah amsa ba saida ta tabbatar ta kwantar da fanne da fanna sannan tace yau dinnan zan gama dasu, ki kwantar da hankakinki dan sun fasa kwalbar a banza dan babu wanda yake tunata bare har yayi mata adduar da zaisa ta gama dawowa hayyacinta,,
yanzun nan zan kara yin aikin da yafi wancan akanta,
oyizah ta saki ajiyar zuciya tace nagode my lord..
Afeeyah na zaune tana lazumi, tunda ta idar da sallar la'asar bata tashi daga kan daddumar ba sai gurin biyar,
shafa addu'ar tayi ta mike ta nade daddumar sannan ta zauna a kasa a gefen gadonta ta tura hannunta karkashin gadon ta zaro zanin da ta kunshe damon nan a ciki,
a hankali ta warwareshi ta nade hannunta da leda cikin dakewar zuciya ta fara kakkabe kasar tana kokarin bude bakin damon,
cikin sa'a ta budeshi sai wari yakeyi ta karkatar da bakin ta girgizah shi, nan wata katuwar laya ta faďo kasa,
da sauri ta ajiye wannan damon ta naďeshi cikin zanin ta dauki layar ta warwareta,
babu abinda ta gane a cikin rubutun sai sunan zeenatu,
nade layar tayi ta mike ta fita da wannan damon ta kulleshi a leda takai main bolar gidan sannan ta dawo ta kona layar ta tattara tokar ta zubata a magudanar ruwa...
★ Magaryah Nijar★