Sashe 40
Rabo Ajali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
☆ 2:30am ☆
Lokacin ta idar da sallolin da takeyi ta fara adduo'i tana neman taimakon Allah akan abin da zata aiwatar yanzu,
saida tayi addu'a sosai sannan ta mike ta cire hijab dinta ta rufe Affan dashi ta tofe shi da addu'a,
Saida ta tabbatar ta rufe windows din dakin sosai ta yadda ko kuda bazai iya bi ba bare ido yaga me akeyi a ciki,
da bismillah ta yaye zanin gadon sannan ta daga katifar,
dakyar ta iya cire katakon dake kasan gadon saboda nauyinsu,
a razane ta ja baya saboda hango wani makeken rami a karkashin gadon,
hasbunallahu wa ni'imal wakil kawai take fada saboda ta matukar tsorata da ramin, zuciyarta sai bugawa takeyi saboda tuna ita fa xata sa hannunta cikin ramin,
girgiza kanta tayi ta fara ja baya tana fadin wallhy bazan iya ba,
ji tayi kamar ta daki mutum a bayanta ta juyo a razane taga babu kowa sai muryar kaka liman dake mata yawo cikin kunnuwanta,
"na rokeki karki tsorata ke kadai ce garkuwar bayin Allahn nan,
in kika tsorata babu wanda zai iya,
"in kika gansu Ruwanki ne ki barsu ko ki ciresu ki taimaki mahaifi da kakar abinda ke cikinki""
A hankali ta karaso gurin ramin idonta cike da kwalla tasa hannu ta fara ciro kulle kullen dake ciki,
gumakan dake cikin ramin uku ne, daya an soke kanshi da mashi, biyu kuma an haďe su guri daya an kulle,
saida ta tabbatar ta fitar da komai daga cikin ramin sannan ta maida kayan gadon tana yi tana share zufa,
gaba daya a lokacin ta nemi tsoro ta rasa, kwashesu tayi cikin hijab din da ta rufama Affan ta buďe kofar dakin tayi saurin wucewa dakinta,
kitchen ta wuce cikin dakewar zuciya ta fara warware duk wani kullin garin magani tana zubarwa a cikin zinc tana kwarara mishi ruwa, haka layunma duk tayi musu,
gunkin lakan da aka hade su guri daya ta fara warwarewa ta sa tabarya ta dakeshi ya zama gari sannan ta kwararar dashi cikin zinc,
dauko dayan gunkin tayi wanda akayi shi da roba,
da bismillah ta zare mashin ciki,
tana dauko wuka zata fara yankashi taji wata guguwa mai karfi ta bude windown kitchen din,
hannaye taga an ziro ta cikin windown tayi saurin yar da wukar hannunta ta cilla wannan mashin bayan cabinet,
a hankali taga gangar jikin mutum na shigowa,
da gudu tayi hanyar waje tana addu'a,
tana zuwa kofar taji an datseta da karfi,
ja da baya ta fara yi tana salati tana kiran sunan hajja,
oyizah ta gani muraran ta bullo ta cikin kofar,
zaro ido tayi murya na rawa tace m-u-mm-y,
oyizah ta buga mata wata sanda a bakinta,
rike bakin tayi tana ta nemo addu'a a bakinta ta rasa,
cikin kunan rai oyizah ta fara matsowa fuskar nan babu rahama tace yau sai na kasheki, daga yau kin daina numfashi a doron kasa bare har kiyi yunkurin shiga rayuwata,
da hannuna zan kasheki tunda duk wani abu da nayi akanki bana samun nasara,
ban taba haduwa da abin da ya dameni ba sai a kanki dake da matsyacin saurayinki jabeer,
kamar yadda na kawar da jabeer da mahaifiyar Affan kema haka zan kawar dake kije can ki samesu dan babu wanda ya isa ya shiga gonata ya fita ba tare da yayi noma ba,
tayi wani huci hade da daga wannan sandar zata buga ma Afeeyah, da sauri ta goce ta rike sandar sosai,
nan suka fara dambe sosai har oyizah tayi nasarar kwace sandar,
da karfi ta shiga laftar Afeeyah da ita,
ihu Afeeyah takeyi tana ja da baya saboda azaba,
wani jug ta rarumo a gefenta ta kwaďa ma oyizah akanta,
nan jini ya fara zuba sosai,
da sauri Afeeyah ta bangajeta ta kama kofar kitchen din tana jijjigawa tana ihu sosai kamar zata tsaga gidan,
ganin kofar taki buduwa yasata daukar wuka ta nuna ma oyizah dake tahowa kusa da ita tace wallhy kina matsowa zan kashe ki,
oyizah ta goge jinin gefen idonta tayi wata irin dariya tace wai gawa ce ke maganar kashe me rai,
cikin kuka Afeeyah ta juya tana faďin ya Allah ka taimakeni,
tana jan kofar taji ta buďu tayi saurin fita ta datso oyizah a ciki,
da mamakinta tana bude kofar parlonta ta tarar da oyizah da wata mata mai gebararran halitta,
runtse idonta tayi ta fara fadin hasbunallahu wa ni'imal wakil, la ila ha illa anta subhanaka inni kuntu minal zalumin,
wukar nan dake hannunta ta ďaga da niyyar buga ma oyizah, nan tayi saurin dukawa ta kamo kafar Afeeyah ta daga ta sama tayi wurgi da ita ta bugu da bango da tiles din dakin,
kara mai karfi ta saki wacce ba alhj basheer kaďai ba har masu gadin gidan saida suka girgiza da jinta,
tun daga wannan karar Afeeyah bata kara sanin inda kanta yake ba,
jin Alhj basheer ya bude kofar dakinshi yasa chummy ta bace,,
da sauri oyizah ta yar da sandar hannunta ta tsuguna tana ihu a gaban Afeeyah,
da gudu Alhj basheer da farida suka karaso gurin, cikin rudewa alhj basheer ya shiga jijjiga ta yana kiran sunanta,
kallon oyizah yayi tana kuka sosai yace safiya me ya sameta, cikin makirci oyizah tace nima fitowa nayi na tarar da ita anan tana dambe da iska, ina matsowa kusa da ita sai naji saukar wannan wukar a goshina,
anya alhj yarinyar nan ba matsafiya bace kuwa,?
alhj basheer ya daka mata tsawa yace kamata mu kaita asibiti muji abin da ke damunta,
oyizah ta share hawayen karya ta kamata a zuciyarta tana murna dan suna zuwa asibiti zata karasa ta acan,
Alhj basheer na tada mota yaji kamar muryar Affan a gefen glass din motar, kallonshi yayi yace Affan ka tashi ne,
Affan ya gyaďa kanshi idonshi jajur yace daddy ina zaku kaita,
alhj basheer yace asibiti zamu kaita yanzu zamu dawo je ka kwanta kaji,
bude motar yayi ya zauna a inda aka kwantar da ita yace muje daddy,
alhj basheer yace kayi hakuri Affan ka je ka kwanta kafin mu dawo, Affan kamar zaiyi kuka yace daddy bazan iya bacci ba,
oyizah cikin fushi tace ka sauka akace ko bakaji abin da aka ce maka bane,
kallonta yayi cikin ido hawaye na sauka cikin nashi yace saidai idan tare da Afeeyah zaku saukemu,
oyizah zata kuma magana alhj basheer ya tada motar yace muje kyaleshi,
oyizah tayi kwafa dan wannan mayen ya rusa mata plan dinta,
har suka kai asibitin idon Affan bai bar zubar da hawaye ba,
janyoshi daddy yayi yana rarrashinshi akan ya daina kuka babu abinda zai sameta,
sun dan dade a tsaye kafin doctor yazo, direct ya wuce dakin da aka kaita,
ya dade yana treatn dinta yiyi dressn ciwukan dake jikinta,,
oyizah ma ta je wata nurse tayi mata dressn sannan ta wuce dakin da Afeeyah take,
zaune ta samu Affan ya kwantar da kanshi akan hannun Afeeyah yana kuka alhj basheer na tsaye a kansu yana rarrashinshi,
tsaki tayi a hankali ta karaso gurin tace alhj ya kamata kuje gida ni sai in kwana anan,
Affan yayi saurin dago kanshi ya noke wuyanshi yace um um nima zan kwana,
oyizah tayi dariya tace ya za'ayi mai jinya yayi jinya, kai da ba wani isashshen lafiya gareka ba ina kai ina jinya,
Affan ya kara fashewa da kuka yace ni babu inda zani,
alhj basheer yace to duk babu inda zamu a nan zamu kwana, oyizah ta ja baya cikin bacin rai ta watsa ma Affan harara a zuciyarta tace shege mayatacce ka kusa daina ganinta kwata2.....
Mrs tijjani shattima....
[15/12 09:38] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 5⃣8⃣ By Aysha Ya'u Kurah
A tsaye suka kwana a kanta babu wanda ya runtsa,
oyizah taki runtsawa ne saboda tana jiran su alhj basheer su rufe idonsu ta ida mugun nufinta akan Afeeyah,
alhj basheer kuwa yaki runtsawa ne saboda ganin Affan bai runtsa ba kuka kawai yakeyi wanda babu wanda a cikin su yasan dalilin yinshi har ni da nake dauko muku rahoto,
karfe 6 doctor ya iso, dakin Afeeyah ya shiga suka gaisa da alhj basheer yace bata farfado ba har yanxu,
alhj basheer yace ko motsi bata yi ba doctor da fatan dai ba wata gagarumar matsala bace,
doctor musah ya bude idonta a hankali yace buguwa ce kawai tayi sai wadannan ciwukan,
ya akayi ta samu wadannan raunin haka alhj,
alhj basheer cikin damuwa yace ina ganin gamo tayi cikin dare dan ni ihunta kawai naji na fito na sameta a sume ina fatan dai bai taba lafiyar cikinta ba ko doctor,
doctor musah yace dakyar ne alhj dan buguwar a kai tayi amma anjima zanyi scanning dan tabbatar da lafiyar shi,
alhj basheer yace Allah yasa muji alkhairi, doctor musa yace Ameen alhj sannan ya fita,
oyizah tace alhj ya kamata ku tafi gida kuje kuyi wanka sai ku kawo mana abin kari ko,
alhj basheer ya dafa kan Affan yace tashi muje gida ka dan yi bacci ka huta anjima sai mu dawo,
Affan ya ďago idonshi da ya kumbura ya girgiza kanshi yace kaje daddy,
alhj basheer yace haba Affan baka ganin yadda idonka yayi nasan ka gaji kuma bacci kakeji, kayi hakuri kazo muje kaji,
Affan ya mike yana murza idonshi ya fita ba tare da ya kalle su ba,
saida alhj ya dan dade a ciki sannan ya fito ya samu Affan a mota ya daura kanshi kan murfin kofar,
shiga yayi ya tada motar suka wuce...
Lokacin ta idar da sallolin da takeyi ta fara adduo'i tana neman taimakon Allah akan abin da zata aiwatar yanzu,
saida tayi addu'a sosai sannan ta mike ta cire hijab dinta ta rufe Affan dashi ta tofe shi da addu'a,
Saida ta tabbatar ta rufe windows din dakin sosai ta yadda ko kuda bazai iya bi ba bare ido yaga me akeyi a ciki,
da bismillah ta yaye zanin gadon sannan ta daga katifar,
dakyar ta iya cire katakon dake kasan gadon saboda nauyinsu,
a razane ta ja baya saboda hango wani makeken rami a karkashin gadon,
hasbunallahu wa ni'imal wakil kawai take fada saboda ta matukar tsorata da ramin, zuciyarta sai bugawa takeyi saboda tuna ita fa xata sa hannunta cikin ramin,
girgiza kanta tayi ta fara ja baya tana fadin wallhy bazan iya ba,
ji tayi kamar ta daki mutum a bayanta ta juyo a razane taga babu kowa sai muryar kaka liman dake mata yawo cikin kunnuwanta,
"na rokeki karki tsorata ke kadai ce garkuwar bayin Allahn nan,
in kika tsorata babu wanda zai iya,
"in kika gansu Ruwanki ne ki barsu ko ki ciresu ki taimaki mahaifi da kakar abinda ke cikinki""
A hankali ta karaso gurin ramin idonta cike da kwalla tasa hannu ta fara ciro kulle kullen dake ciki,
gumakan dake cikin ramin uku ne, daya an soke kanshi da mashi, biyu kuma an haďe su guri daya an kulle,
saida ta tabbatar ta fitar da komai daga cikin ramin sannan ta maida kayan gadon tana yi tana share zufa,
gaba daya a lokacin ta nemi tsoro ta rasa, kwashesu tayi cikin hijab din da ta rufama Affan ta buďe kofar dakin tayi saurin wucewa dakinta,
kitchen ta wuce cikin dakewar zuciya ta fara warware duk wani kullin garin magani tana zubarwa a cikin zinc tana kwarara mishi ruwa, haka layunma duk tayi musu,
gunkin lakan da aka hade su guri daya ta fara warwarewa ta sa tabarya ta dakeshi ya zama gari sannan ta kwararar dashi cikin zinc,
dauko dayan gunkin tayi wanda akayi shi da roba,
da bismillah ta zare mashin ciki,
tana dauko wuka zata fara yankashi taji wata guguwa mai karfi ta bude windown kitchen din,
hannaye taga an ziro ta cikin windown tayi saurin yar da wukar hannunta ta cilla wannan mashin bayan cabinet,
a hankali taga gangar jikin mutum na shigowa,
da gudu tayi hanyar waje tana addu'a,
tana zuwa kofar taji an datseta da karfi,
ja da baya ta fara yi tana salati tana kiran sunan hajja,
oyizah ta gani muraran ta bullo ta cikin kofar,
zaro ido tayi murya na rawa tace m-u-mm-y,
oyizah ta buga mata wata sanda a bakinta,
rike bakin tayi tana ta nemo addu'a a bakinta ta rasa,
cikin kunan rai oyizah ta fara matsowa fuskar nan babu rahama tace yau sai na kasheki, daga yau kin daina numfashi a doron kasa bare har kiyi yunkurin shiga rayuwata,
da hannuna zan kasheki tunda duk wani abu da nayi akanki bana samun nasara,
ban taba haduwa da abin da ya dameni ba sai a kanki dake da matsyacin saurayinki jabeer,
kamar yadda na kawar da jabeer da mahaifiyar Affan kema haka zan kawar dake kije can ki samesu dan babu wanda ya isa ya shiga gonata ya fita ba tare da yayi noma ba,
tayi wani huci hade da daga wannan sandar zata buga ma Afeeyah, da sauri ta goce ta rike sandar sosai,
nan suka fara dambe sosai har oyizah tayi nasarar kwace sandar,
da karfi ta shiga laftar Afeeyah da ita,
ihu Afeeyah takeyi tana ja da baya saboda azaba,
wani jug ta rarumo a gefenta ta kwaďa ma oyizah akanta,
nan jini ya fara zuba sosai,
da sauri Afeeyah ta bangajeta ta kama kofar kitchen din tana jijjigawa tana ihu sosai kamar zata tsaga gidan,
ganin kofar taki buduwa yasata daukar wuka ta nuna ma oyizah dake tahowa kusa da ita tace wallhy kina matsowa zan kashe ki,
oyizah ta goge jinin gefen idonta tayi wata irin dariya tace wai gawa ce ke maganar kashe me rai,
cikin kuka Afeeyah ta juya tana faďin ya Allah ka taimakeni,
tana jan kofar taji ta buďu tayi saurin fita ta datso oyizah a ciki,
da mamakinta tana bude kofar parlonta ta tarar da oyizah da wata mata mai gebararran halitta,
runtse idonta tayi ta fara fadin hasbunallahu wa ni'imal wakil, la ila ha illa anta subhanaka inni kuntu minal zalumin,
wukar nan dake hannunta ta ďaga da niyyar buga ma oyizah, nan tayi saurin dukawa ta kamo kafar Afeeyah ta daga ta sama tayi wurgi da ita ta bugu da bango da tiles din dakin,
kara mai karfi ta saki wacce ba alhj basheer kaďai ba har masu gadin gidan saida suka girgiza da jinta,
tun daga wannan karar Afeeyah bata kara sanin inda kanta yake ba,
jin Alhj basheer ya bude kofar dakinshi yasa chummy ta bace,,
da sauri oyizah ta yar da sandar hannunta ta tsuguna tana ihu a gaban Afeeyah,
da gudu Alhj basheer da farida suka karaso gurin, cikin rudewa alhj basheer ya shiga jijjiga ta yana kiran sunanta,
kallon oyizah yayi tana kuka sosai yace safiya me ya sameta, cikin makirci oyizah tace nima fitowa nayi na tarar da ita anan tana dambe da iska, ina matsowa kusa da ita sai naji saukar wannan wukar a goshina,
anya alhj yarinyar nan ba matsafiya bace kuwa,?
alhj basheer ya daka mata tsawa yace kamata mu kaita asibiti muji abin da ke damunta,
oyizah ta share hawayen karya ta kamata a zuciyarta tana murna dan suna zuwa asibiti zata karasa ta acan,
Alhj basheer na tada mota yaji kamar muryar Affan a gefen glass din motar, kallonshi yayi yace Affan ka tashi ne,
Affan ya gyaďa kanshi idonshi jajur yace daddy ina zaku kaita,
alhj basheer yace asibiti zamu kaita yanzu zamu dawo je ka kwanta kaji,
bude motar yayi ya zauna a inda aka kwantar da ita yace muje daddy,
alhj basheer yace kayi hakuri Affan ka je ka kwanta kafin mu dawo, Affan kamar zaiyi kuka yace daddy bazan iya bacci ba,
oyizah cikin fushi tace ka sauka akace ko bakaji abin da aka ce maka bane,
kallonta yayi cikin ido hawaye na sauka cikin nashi yace saidai idan tare da Afeeyah zaku saukemu,
oyizah zata kuma magana alhj basheer ya tada motar yace muje kyaleshi,
oyizah tayi kwafa dan wannan mayen ya rusa mata plan dinta,
har suka kai asibitin idon Affan bai bar zubar da hawaye ba,
janyoshi daddy yayi yana rarrashinshi akan ya daina kuka babu abinda zai sameta,
sun dan dade a tsaye kafin doctor yazo, direct ya wuce dakin da aka kaita,
ya dade yana treatn dinta yiyi dressn ciwukan dake jikinta,,
oyizah ma ta je wata nurse tayi mata dressn sannan ta wuce dakin da Afeeyah take,
zaune ta samu Affan ya kwantar da kanshi akan hannun Afeeyah yana kuka alhj basheer na tsaye a kansu yana rarrashinshi,
tsaki tayi a hankali ta karaso gurin tace alhj ya kamata kuje gida ni sai in kwana anan,
Affan yayi saurin dago kanshi ya noke wuyanshi yace um um nima zan kwana,
oyizah tayi dariya tace ya za'ayi mai jinya yayi jinya, kai da ba wani isashshen lafiya gareka ba ina kai ina jinya,
Affan ya kara fashewa da kuka yace ni babu inda zani,
alhj basheer yace to duk babu inda zamu a nan zamu kwana, oyizah ta ja baya cikin bacin rai ta watsa ma Affan harara a zuciyarta tace shege mayatacce ka kusa daina ganinta kwata2.....
Mrs tijjani shattima....
[15/12 09:38] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 5⃣8⃣ By Aysha Ya'u Kurah
A tsaye suka kwana a kanta babu wanda ya runtsa,
oyizah taki runtsawa ne saboda tana jiran su alhj basheer su rufe idonsu ta ida mugun nufinta akan Afeeyah,
alhj basheer kuwa yaki runtsawa ne saboda ganin Affan bai runtsa ba kuka kawai yakeyi wanda babu wanda a cikin su yasan dalilin yinshi har ni da nake dauko muku rahoto,
karfe 6 doctor ya iso, dakin Afeeyah ya shiga suka gaisa da alhj basheer yace bata farfado ba har yanxu,
alhj basheer yace ko motsi bata yi ba doctor da fatan dai ba wata gagarumar matsala bace,
doctor musah ya bude idonta a hankali yace buguwa ce kawai tayi sai wadannan ciwukan,
ya akayi ta samu wadannan raunin haka alhj,
alhj basheer cikin damuwa yace ina ganin gamo tayi cikin dare dan ni ihunta kawai naji na fito na sameta a sume ina fatan dai bai taba lafiyar cikinta ba ko doctor,
doctor musah yace dakyar ne alhj dan buguwar a kai tayi amma anjima zanyi scanning dan tabbatar da lafiyar shi,
alhj basheer yace Allah yasa muji alkhairi, doctor musa yace Ameen alhj sannan ya fita,
oyizah tace alhj ya kamata ku tafi gida kuje kuyi wanka sai ku kawo mana abin kari ko,
alhj basheer ya dafa kan Affan yace tashi muje gida ka dan yi bacci ka huta anjima sai mu dawo,
Affan ya ďago idonshi da ya kumbura ya girgiza kanshi yace kaje daddy,
alhj basheer yace haba Affan baka ganin yadda idonka yayi nasan ka gaji kuma bacci kakeji, kayi hakuri kazo muje kaji,
Affan ya mike yana murza idonshi ya fita ba tare da ya kalle su ba,
saida alhj ya dan dade a ciki sannan ya fito ya samu Affan a mota ya daura kanshi kan murfin kofar,
shiga yayi ya tada motar suka wuce...