Sashe 22
Rabo Ajali Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Wurgi Afeeyah tayi da mahmud ta fita da gudu,
duk irin kiran da hajja take mata baisa ta tsaya ba,
da gudu ta shiga gidan ta tarar dasu baba ado zaune da wasu mutane sunyi tagumi a bakin gate, da sauri ta karasa kusa dashi tace baba ado me ya samu yayana?,
baba ado ya kauda kanshi da sauri yana share hawayen dake zuba a idonshi, Afeeyah ta bar gurin da gudu ta shige cikin gidan,
murďa kofar parlon tayi da karfi kamar zata balleta,
tana shiga ta dinga bin mutanen dake parlon da kallo,
ganin mutum kwance cikin jini a kasa yasa zuciyarta bugawa da karfi,
a hankali ta fara motsa kafarta tana tafiya har ta isa gabanshi,
tsugunawa tayi ta yaye abin da aka rufe mishi fuskarshi da shi, gaba ďaya hanyoyin sadarwa na jikin Afeeyah suka daina aiki sakamakon ganin fuskar jabeer,
kallonshi ta tsaya yi bata ko kiftawa,
alhj basheer ya taso ya karaso gurinta ya ďagota dakyar dan jikinta a sake yake kamar wacce bata da rai,
zaunar da ita yayi akan kujera ya fara mata nasiha, ko kaďan bataji abinda yake cewa ba idonta na kan jabeer da alhj bara'u da mahaifinta ke kokarin ďaukarshi suyi mishi wanka,
alhj basheer ya girgizata yace Afeeyah kina jina,
lumshe idonta tayi lokacin da aka fita da gawar,
alhj basheer zaiyi magana hajja ta shigo da gudu tana faďin innalillahi wa inna ilaihir rajiun, me yasamu jabeer alhj, na shiga uku na lalace, alhj basheer yace dan Allah hajja kiyi shuru kar gidan ya rikice adduarmu jabeer yake bukata ba kuka,
hajja ta zauna tana kuka tana fadin kukan ne babu mai iya hana shi fita alhj,
ta kalli Afeeyah da idonta ke lumshe har lokacin ta riketa sosai ta kira sunanta har sau uku taji shuru,
ta girgizata da karfi tace ki bude idonki Afeeyah, nasan abinda kikeji dan Allah kiyi tawakkali, kar wata cutar ta kama ki,
dan Allah Afeey--- Afeeyah tace hajja me kika gani yanzu, kuka nakeyi ko me, ba tawakkalin nayi ba,
me kukeso inyi, ku faďa min me zanyi yanzu hajja,, kome kukace inyi zanyi walhy,
alhj basheer ya fita da sauri saboda kukan da yaci karfinshi yasan sam Afeeyah bata cikin hayyacinta,
hajja cikin kuka tace addu'a zakiyi Afeeyah, addu'a jabeer yake bukata,
Afeeyah ta bude idonta sosai tace hajja a ina zanyi adduar,
hajja ta rungumeta tana sheshshekar kuka tace a bakinki zakiyi ta,
Afeeyah tayi yake tace hajja kunce kar inyi kuka, kuma ku gashi kuna yi dan Allah kiyi shuru bari in shiga gurin ummi,
hajja ta rike hannunta suka shiga gurin Abida inda makota suka kewayeta,
tana ganin Afeeyah ta sunkuyar da kanta kasa sai a lokacin wasu hawaye masu zafi suka fito daga idonta,
Afeeyah tace ummi kuka kikeyi, daddy yace kar muyi kuka,
ta kalli Amirah tace Amirah dan Allah ki faďa min yadda zanyi hawaye su fito a idona, Amirah ta fada jikinta tana kuka sosai, Afeeyah tace dan Allah ku fadamin yadda zanyi, zuciyata zata buga ku taimakeni inyi kuka ko zan samu saukin nauyin da zuciyata tayi,
Alhj bara'u ne ya shigo ďakin shima idonshi jajur yace Abida kuzo kuyi mishi addu'a an gama shiryashi,
Abida kanta a kasa tace kuje kawai rahamar ubangiji ita kadai nake mishi fatan samu a kabarinshi, Afeeya ta mike ta fita da gudu a tsakar gida taga gawar an shiryata cikin likkafani,
da gudu ta karasa bata lura da mutanen da sukayi dafifi a gurin ba ta faďa kan gawar tana shafawa,
a hankali tace yaya jabeer alkawarin da kayi min kenan, meyasa zaka tafi ka barni, saida nace maka mu tafi tare kaki yarda ka tafi kai kadai yanzu ka faďamin yadda za'ayi in cigaba da rayuwa babu kai, meyasa bakayi tunanin abin da mutuwarka zata haifar a cikin zuciyata ba, dan girman Allah yaya jabeer ka tashi karka tafi ka barni, kai kaďai gareni,
malam atiku ya matso kusa da ita ya dafata yace Afeeyah Allah baya barin wani dan wani yaji daďi, Allah ba ruwanshi da duba shakuwarku,
Allah ya kaddara--- ta katseshi ta hanyar bige hannunshi tace wace irin kaddarace wannan, meyasa bata daukeshi tun kafin inzo duniya ba, sai yanzu zata zo ta dauke min shi a lokacin da nake bukatarshi,
ta mike tsaye tace abba dan Allah ka fadamin yadda zan iya cigaba da rayuwa, kasan dai bazai yiwu ba,
malam atiku ya rungume yarshi yana kuka sosai, yace Afeeyah nasan yadda kikeji,
ta sakeshi tana girgiza kai tace wallhy abba babu wanda yasan yadda nakeji sai yaya jabeer,
ta kankameshi tace kai kadai kasan yadda nakeji, dan Allah ka tashi,
duk rashin imaninka sai ka zubar ma da Afeeyah hawaye, babu yadda ba'ayi a banbareta jikin gawar ba amma abin ya faskara tana kwance kanshi tana sambatu babu ko ďigon hawaye a idonta,
dago kanta tayi saboda ganin mutum yayi kneel down a gefenta yana shafa tun daga kafar jabeer har kanshi,
kallonta yayi yana kaďa kanshi hawaye na fitowa a idonshi yace barbie yau kwana 9 banga abokina ba, yanzu kuma naga sun rufeshi da fararen kaya ina zasu kaishi,
kice mishi ya buďe idonshi inason muyi magana, I missd him so much,
sai a lokacin Afeeyah ta kara maida kanta kan jabeer ta fara kuka mai tsanani tana fadin maganganun da ita kanta bata san suna fitowa daga bakinta ba,
Affan ma duk da baya cikin hankalinshi yaji a jikinshi wani mummunan abu ya samu abokinshi,
da kyar aka iya banbare Afeeyah jikin gawar jabeer,
ana sashi cikin makara ta kara fashewa da kuka tana faďin dan Allah ku dawo min dashi wallahi zai dawo gareni, dan Allah karku fita dashi, ta dinga fisge2 jikin wadanda suka riketa tana fadin a dawo dashi ko ya mutu a bar mata gawarshi,
suna shashi a mota Afeeyah ta saki wani gigitaccen ihu ta faďi kasa sumammiya....
Mrs tijjani shattima....
[15/12 09:34] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 3⃣3⃣ By Aysha Ya'u Kurah
A hankali ta fara buďe idonta da yayi mata nauyi sosai,
dishi2 take gani tayi saurin mayar dasu ta runtsesu tana fitar da wani irin wahalallen numfashi,
muryar Anty Asiya ce yasa ta kara bude su ta kalleta,
anty Asiya ta shafa kanta idonta cike da kwalla tace sannu Afeeyah, babu inda yake miki ciwo,
ta lumshe idonta tana girgiza kai hawaye na zuba a gefen idonta, anty Asiya ta fara yi mata nasihar da daga ji itama na karfin hali ne,
saida ta daďe tana mata nasiha sannan ta tashi ta fita,
da sauri safnah ta dawo gefenta ta rike hannunta tana zubar da hawaye tace Afee,
Afeeyah ta kara runtse idonta hawaye na gangarorowa cikinsu kamar an saki ruwan pampo,
Safnah ta kwanta a jikinta cikin muryar kuka tace don't stop dis tears Afee let it flow nasan yadda kikeji, cry as much as u can,
Afeeyah ta kara fashewa da kuka, suka dinga yi ita da safnah dake jin mutuwar ta ko ina a cikin jikinta,
sun daďe suna kuka kafin safnah tayi shuru ta mike tana kallon Afee,
safnah tace Afee tashi kiyi sallah kinsan fa bakiyi azhar ba gashi har la'asar ta wuce, dakyar Afeeyah ta gyaďa mata kai tace shikenan safnah sun kaishi sun birne min shi ko,
shikenan ni yanzu bani da wani sauran gata a duniya ko, dan Allah safnah ki roka min Allah in mutu in bi shi dan wallhy bazan iya rayuwa ba,
Goggon daura ce ta shigo cikin dakin ta zauna gefensu tace zaki iya rayuwa Afeeyah,
wannan kukan da kikeyi babu wanda zai hanaki yinshi domin shine kadai ne zai rage miki raďađin da kikeji, ki sani jabeer yayi mutuwar da ko wane musulmi zaiso yayita, ya mutu a daren alhamis aka kaishi ranar jumma,a, ya mutu a hanyarshi ta ziyara kuma da kyakykyawar niyya a zuciyarshi,
ko wannan muka tuna ya isa yasa mu ji dadi saboda yayi mutuwar da akeso,
tashi maza kije kiyi sallah ki karfafa zuciyarki kiyi mishi adduar samun rahama wannan ita kaďai ce hanyar da zaki nuna tsantsar soyayyarki gareshi yanzu,
Afeeyah ta gyaďa kanta ta mike dakyar ta shiga bayi..
duk irin kiran da hajja take mata baisa ta tsaya ba,
da gudu ta shiga gidan ta tarar dasu baba ado zaune da wasu mutane sunyi tagumi a bakin gate, da sauri ta karasa kusa dashi tace baba ado me ya samu yayana?,
baba ado ya kauda kanshi da sauri yana share hawayen dake zuba a idonshi, Afeeyah ta bar gurin da gudu ta shige cikin gidan,
murďa kofar parlon tayi da karfi kamar zata balleta,
tana shiga ta dinga bin mutanen dake parlon da kallo,
ganin mutum kwance cikin jini a kasa yasa zuciyarta bugawa da karfi,
a hankali ta fara motsa kafarta tana tafiya har ta isa gabanshi,
tsugunawa tayi ta yaye abin da aka rufe mishi fuskarshi da shi, gaba ďaya hanyoyin sadarwa na jikin Afeeyah suka daina aiki sakamakon ganin fuskar jabeer,
kallonshi ta tsaya yi bata ko kiftawa,
alhj basheer ya taso ya karaso gurinta ya ďagota dakyar dan jikinta a sake yake kamar wacce bata da rai,
zaunar da ita yayi akan kujera ya fara mata nasiha, ko kaďan bataji abinda yake cewa ba idonta na kan jabeer da alhj bara'u da mahaifinta ke kokarin ďaukarshi suyi mishi wanka,
alhj basheer ya girgizata yace Afeeyah kina jina,
lumshe idonta tayi lokacin da aka fita da gawar,
alhj basheer zaiyi magana hajja ta shigo da gudu tana faďin innalillahi wa inna ilaihir rajiun, me yasamu jabeer alhj, na shiga uku na lalace, alhj basheer yace dan Allah hajja kiyi shuru kar gidan ya rikice adduarmu jabeer yake bukata ba kuka,
hajja ta zauna tana kuka tana fadin kukan ne babu mai iya hana shi fita alhj,
ta kalli Afeeyah da idonta ke lumshe har lokacin ta riketa sosai ta kira sunanta har sau uku taji shuru,
ta girgizata da karfi tace ki bude idonki Afeeyah, nasan abinda kikeji dan Allah kiyi tawakkali, kar wata cutar ta kama ki,
dan Allah Afeey--- Afeeyah tace hajja me kika gani yanzu, kuka nakeyi ko me, ba tawakkalin nayi ba,
me kukeso inyi, ku faďa min me zanyi yanzu hajja,, kome kukace inyi zanyi walhy,
alhj basheer ya fita da sauri saboda kukan da yaci karfinshi yasan sam Afeeyah bata cikin hayyacinta,
hajja cikin kuka tace addu'a zakiyi Afeeyah, addu'a jabeer yake bukata,
Afeeyah ta bude idonta sosai tace hajja a ina zanyi adduar,
hajja ta rungumeta tana sheshshekar kuka tace a bakinki zakiyi ta,
Afeeyah tayi yake tace hajja kunce kar inyi kuka, kuma ku gashi kuna yi dan Allah kiyi shuru bari in shiga gurin ummi,
hajja ta rike hannunta suka shiga gurin Abida inda makota suka kewayeta,
tana ganin Afeeyah ta sunkuyar da kanta kasa sai a lokacin wasu hawaye masu zafi suka fito daga idonta,
Afeeyah tace ummi kuka kikeyi, daddy yace kar muyi kuka,
ta kalli Amirah tace Amirah dan Allah ki faďa min yadda zanyi hawaye su fito a idona, Amirah ta fada jikinta tana kuka sosai, Afeeyah tace dan Allah ku fadamin yadda zanyi, zuciyata zata buga ku taimakeni inyi kuka ko zan samu saukin nauyin da zuciyata tayi,
Alhj bara'u ne ya shigo ďakin shima idonshi jajur yace Abida kuzo kuyi mishi addu'a an gama shiryashi,
Abida kanta a kasa tace kuje kawai rahamar ubangiji ita kadai nake mishi fatan samu a kabarinshi, Afeeya ta mike ta fita da gudu a tsakar gida taga gawar an shiryata cikin likkafani,
da gudu ta karasa bata lura da mutanen da sukayi dafifi a gurin ba ta faďa kan gawar tana shafawa,
a hankali tace yaya jabeer alkawarin da kayi min kenan, meyasa zaka tafi ka barni, saida nace maka mu tafi tare kaki yarda ka tafi kai kadai yanzu ka faďamin yadda za'ayi in cigaba da rayuwa babu kai, meyasa bakayi tunanin abin da mutuwarka zata haifar a cikin zuciyata ba, dan girman Allah yaya jabeer ka tashi karka tafi ka barni, kai kaďai gareni,
malam atiku ya matso kusa da ita ya dafata yace Afeeyah Allah baya barin wani dan wani yaji daďi, Allah ba ruwanshi da duba shakuwarku,
Allah ya kaddara--- ta katseshi ta hanyar bige hannunshi tace wace irin kaddarace wannan, meyasa bata daukeshi tun kafin inzo duniya ba, sai yanzu zata zo ta dauke min shi a lokacin da nake bukatarshi,
ta mike tsaye tace abba dan Allah ka fadamin yadda zan iya cigaba da rayuwa, kasan dai bazai yiwu ba,
malam atiku ya rungume yarshi yana kuka sosai, yace Afeeyah nasan yadda kikeji,
ta sakeshi tana girgiza kai tace wallhy abba babu wanda yasan yadda nakeji sai yaya jabeer,
ta kankameshi tace kai kadai kasan yadda nakeji, dan Allah ka tashi,
duk rashin imaninka sai ka zubar ma da Afeeyah hawaye, babu yadda ba'ayi a banbareta jikin gawar ba amma abin ya faskara tana kwance kanshi tana sambatu babu ko ďigon hawaye a idonta,
dago kanta tayi saboda ganin mutum yayi kneel down a gefenta yana shafa tun daga kafar jabeer har kanshi,
kallonta yayi yana kaďa kanshi hawaye na fitowa a idonshi yace barbie yau kwana 9 banga abokina ba, yanzu kuma naga sun rufeshi da fararen kaya ina zasu kaishi,
kice mishi ya buďe idonshi inason muyi magana, I missd him so much,
sai a lokacin Afeeyah ta kara maida kanta kan jabeer ta fara kuka mai tsanani tana fadin maganganun da ita kanta bata san suna fitowa daga bakinta ba,
Affan ma duk da baya cikin hankalinshi yaji a jikinshi wani mummunan abu ya samu abokinshi,
da kyar aka iya banbare Afeeyah jikin gawar jabeer,
ana sashi cikin makara ta kara fashewa da kuka tana faďin dan Allah ku dawo min dashi wallahi zai dawo gareni, dan Allah karku fita dashi, ta dinga fisge2 jikin wadanda suka riketa tana fadin a dawo dashi ko ya mutu a bar mata gawarshi,
suna shashi a mota Afeeyah ta saki wani gigitaccen ihu ta faďi kasa sumammiya....
Mrs tijjani shattima....
[15/12 09:34] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 3⃣3⃣ By Aysha Ya'u Kurah
A hankali ta fara buďe idonta da yayi mata nauyi sosai,
dishi2 take gani tayi saurin mayar dasu ta runtsesu tana fitar da wani irin wahalallen numfashi,
muryar Anty Asiya ce yasa ta kara bude su ta kalleta,
anty Asiya ta shafa kanta idonta cike da kwalla tace sannu Afeeyah, babu inda yake miki ciwo,
ta lumshe idonta tana girgiza kai hawaye na zuba a gefen idonta, anty Asiya ta fara yi mata nasihar da daga ji itama na karfin hali ne,
saida ta daďe tana mata nasiha sannan ta tashi ta fita,
da sauri safnah ta dawo gefenta ta rike hannunta tana zubar da hawaye tace Afee,
Afeeyah ta kara runtse idonta hawaye na gangarorowa cikinsu kamar an saki ruwan pampo,
Safnah ta kwanta a jikinta cikin muryar kuka tace don't stop dis tears Afee let it flow nasan yadda kikeji, cry as much as u can,
Afeeyah ta kara fashewa da kuka, suka dinga yi ita da safnah dake jin mutuwar ta ko ina a cikin jikinta,
sun daďe suna kuka kafin safnah tayi shuru ta mike tana kallon Afee,
safnah tace Afee tashi kiyi sallah kinsan fa bakiyi azhar ba gashi har la'asar ta wuce, dakyar Afeeyah ta gyaďa mata kai tace shikenan safnah sun kaishi sun birne min shi ko,
shikenan ni yanzu bani da wani sauran gata a duniya ko, dan Allah safnah ki roka min Allah in mutu in bi shi dan wallhy bazan iya rayuwa ba,
Goggon daura ce ta shigo cikin dakin ta zauna gefensu tace zaki iya rayuwa Afeeyah,
wannan kukan da kikeyi babu wanda zai hanaki yinshi domin shine kadai ne zai rage miki raďađin da kikeji, ki sani jabeer yayi mutuwar da ko wane musulmi zaiso yayita, ya mutu a daren alhamis aka kaishi ranar jumma,a, ya mutu a hanyarshi ta ziyara kuma da kyakykyawar niyya a zuciyarshi,
ko wannan muka tuna ya isa yasa mu ji dadi saboda yayi mutuwar da akeso,
tashi maza kije kiyi sallah ki karfafa zuciyarki kiyi mishi adduar samun rahama wannan ita kaďai ce hanyar da zaki nuna tsantsar soyayyarki gareshi yanzu,
Afeeyah ta gyaďa kanta ta mike dakyar ta shiga bayi..