← Book details Rabo Ajali Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 48

Sashe 15

Rabo Ajali Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Tun asuba jabeer ke neman wayar Affan ba'a dauka ba,
daga karshe ma jin wayar yayi akashe,
gurin karfe 8 yaso shiga ya dubashi sai wani muhimmin aiki ya taso mishi a office ya wuce,
bai dawo gida ba sai bayan magriba, saida ya fara shiga gurin Afeeyah suka dan taba hirah sama2 sukaci abinci tare kamar yadda suka saba sannan ya mike jikinshi a sanyaye saboda rashin jin muryar amininshi yau tru out,
abinda bai taba faruwa ba tun tasowarsu dan ko tafiya daya yayi to suna manne a waya, sallama yayi ma hajja da afeeyah ya fita ya isa kofar gidan su Affan,
tun a gate mai gadi ya sanar dashi abinda yake faruwa,
kiriss ya rage jabeer ya faďi saboda tashin hankali, da kyar ya daidaita kanshi ya karasa cikin gidan, babu wanda ya samu a ciki sai farida dake waya tana kyakyata dariya,
murya na rawa yace Fa-re-da- wani asibiti aka kwantar da Affan, sai da ta kalleshi sama da kasa sannan ta ajiye wayarta, cikin masifa tace haddar sunan asibitoci aka kawo ni yi duniya,
cikin bacin rai jabeer yace "oops" na manta fa da'kikiya kamarki wacce bazata iya haddar sunanta ba bare asibitin da aka rubuta shi da turanci saboda masu ilimi su gane, farida ta mike a fusace zata fara bala'i karar bugun kofa ya hanata,
jabeer ya kalli daddy suka gaisa sama2 yace daddy wani asibiti affan yake, daddy yace muje jabeer nima can zanje nan "Arewa surgery" ne,
jabeer ya harari fareeda ta gefen ido yayi kwafa ya bi bayan daddy....

Mrs tijjani shattima....
[15/12 09:34] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 2⃣3⃣ By Aysha Ya'u Kurah

Kuka sosai jabeer yayi da yaga yadda Affan ya koma,
zama yayi gefenshi yasa hannunshi cikin nashi yana karanto adduo'i yana tofa mishi,
oyizah ta harareshi tace dan Allah malam ya isa haka kar miyan ka ya jikashi ya farka lokacin farkawarshi baiyi ba,
daddy yace addu'a fa yake mishi safiya,
oyizah ta marairaice tace doctors ne suka hana alhj nima dazu ina mishi addu'a suka hana ni,
jabeer ya waigo ya kalli daddy idonshi a kumbure yace daddy ina umma,?
alhj basheer yayi jugum sannan ya fada ma jabeer komai game da zeenatu,
a rude jabeer ya mike yace daddy shine ba'a dauki mataki ba tun dazu,
innalillahi wa inna ilaihir rajiun,
alhj basheer yace nasan bazata wuce gida ba gobe da sassafe zan tafi,
jabeer yace da nan ya kamata a fara daddy, in har bata nan sai a tafi can,
oyizah ta harareshi ta wutsiyar ido sannan tace hakane alhj kai kaje cameroon din mu sai mu fara nemanta anan ko jabeer,
jabeer bai kalleta ba yasa kai ya fita zuciyarshi kamar zata buga saboda tashin hankali..

Washe gari tun asuba jabeer ya bar asibitin ya isa gida,
nan suka shiga binciken duk gidajen aminansu na kusa da na nesa shi da Abida da tun jiya bata runtsa ba da jabeer ya faďa mata wannan mummunan labarin,
babu inda basu shiga ba amma babu labari,
jabeer ya zarce gurin yan sanda ya sanar musu sannan ya koma asibiti,,

yana shiga ya tarar da oyizah zaune gefen Affan tana shaka mishi turare a hancinshi, tana ganin jabeer ta mike da sauri tace jabeer ka dawo,
kaga turare ne aka bani ance yana healing ciwon kwakwalwa in ana shakawa mutum shine nake gwada mishi,
jabeer yace uhum kawai ya zauna gefenshi yana kallonshi yana mishi addu'ar da oyizah ta tsani ganin ana mishi,
a zuciyarta tace tabbas in bata katange Affan daga adduo'in mutane ba wata rana tana zaune adduar zatayi tasiri akanshi,, ta kalli Affan tayi kwafa ta maida turaren jaka ta fita daga asibitin..

A can cameroon kuwa tashin hankalin da suka shiga bazai misaltu ba,
dan kuka sunci shi da aka gama duba guraren dangi ba'a sameta ba,
alhj basheer kanshi kasa tsayar da kukanshi yayi yanata kiran sunanta kamar zautacce yana fađin ina kika shiga ne zeenatu,
da kyar Baffan zeenatu ya rarrasheshi da bashi baki akan suyi ta addu'a, ko gawarta ne Allah ya bayyana,

Washe gari tare da su yadikko aka taho duba Affan,
sun jima tsaye akanshi cikin tausayawa amma fa babu wanda a cikinsu ya iya budar baki yayi mishi addu'a,
"saidai kawai suce sannu Affan cuta ba mutuwa bane, wata rana sai labari sai kuga kamar baiyi ciwon ba,"
wadannan kalmomin su kadai duk wanda yaji Affan baida lafiya yake iya faďi,
JABEER BARA'U DAURA shi kaďaine yake yin addu'a sosai akan Affan,
hakan ba karamin ďaga hankalin oyizah yakeyi ba dan tayi duk wani abun da zatayi na tsafi akan jabeer amma ta kasa,
tabbas tasan jinin jabeer ya fi karfinta dan haka ta kudira a ranta Affan na komawa gida zata hana duk wani mahaluki zuwa dubashi bare har ya samu damar yi mishi addu'a,
sannan shima Affan din zata san yadda zatayi ta daure kafarshi a cikin gida ya zamana ko wajen gate bazai iya taka kafarshi ba,
da wannan tunanin oyizah ta ďan samu relief...

Sati biyu suka wuce babu zeenatu babu labarinta,
haka Affan bai farfaďo ba kullum yana kwance cikin oxygen,

Oyizah ta kalli alhj basheer da yake cikin damuwa har yanxu, tace ranka ya ďade ya kamata ka cire duk wata damuwa aranka, duk inda zeenatu take--- yayi saurin katseta yace na manta da batun zeenatu a wayewar garin yau saboda zeenatu ba yarinya bace duk inda take zata iya kula da kanta koda kuwa saceta akayi,
ni yanzu ciwon Affan ne kaďai ke damuna day nd nyt,
oyizah tayi murmushi a zuciyarta tace aiki yayi, ta tuno sanda zata tura layar cikin bakin gawar "Damo" saida ta tsorata taso ta bar aikin, ashe nasara ne ya hanata barinshi,,
ta kalli alhj basheer idonta ya ciko da kwalla, tace karka damu alhj Affan zai samu sauki tunda yana karkashin kulawar likitoci, zeenatu fa babu wanda yasan inda take,
tsawa mai karfi ya daka mata yace nace ki daina kawo min maganar zeenatu nan gurin,
oyizah ta mike sum2 ta wuce ďaki tana kukan munafurci..

Tsalle ta dingayi da ta shiga ďaki murna kamar zai kasheta, yanzu abinda ya rage mata shine tasan inda Affan ya ajiye kadarorin da alhj ya mallaka mishi....

Mrs tijjani shattima....
[15/12 09:34] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 2⃣4⃣ By Aysha Ya'u Kurah

Ranar wata jumma'a bayan an sauko daga sallah jabeer asibiti ya wuce saboda nan ne gurin zama da kwananshi,
duk da irin kyarar da oyizah ke mishi hakan bai hanashi zuwa ba,, addu'a sosai yayi ma Affan a masallaci,
yana shiga cikin asibitin ya tarar babu kowa gurinshi kuma yaga kamar bakinshi na motsawa,
da sauri jabeer ya naďe carbin hannunshi ya karasa kusa dashi, ya rike hannunshi yasa kunnenshi saitin bakinshi,
R-u-w-a yaji yana fada muryarshi na rawa,
jabeer ya mike da azama yaje ya kira doctor suka shigo tare da sauri,
doctor ya gama duba Affan sannan ya kalli jabeer yace dan bashi ruwa kaďan,
jabeer jiki na rawa ya balle murfin Faro ya tsiyaya kadan a ciki saida yayi addu'a sosai a cikin ruwan sannan ya matsa kusa da Affan da har lokacin bai bude ido ba sai kiran ruwa da yakeyi, buďe bakinshi yayi zai fara zuba ruwan aciki oyizah ta shigo da sauri ta kabe glass cup din ya fadi ya fashe,
cikin masifa tace baka da hankali ne zaka bashi wannan ruwan daga cewa a bashi,
doctr musah yace hajiya ruwan is pure ni nace ya bashi,
oyizah ta fito da wani ruwa a cikin gora tace wannan ruwan alhj ya bani kafin ya tafi yace duk sanda ya farfaďo a tabbatar shi ya fara sha saboda ruwan addu'a ne da ya amsoshi daga cameroon,
jabeer da ya cika yayi famm yaja dogon tsaki ya fita ya bar asibitin gaba ďaya,
doctr musa ya ba oyizah da ke sharar kwallar munafurci hakuri yace bamu san akwai adduar da za'a bashi bane da bamuyi gangancin bashi ruwa ba,
tace babu komai doctor, yanzu zan iya bashi kenan,
doctr musah yace eh hajiya, nan oyizah tayi murmushi ta gefe ta zauna ta bude bakin Affan ta tsirara mishi ruwan da yasa shi sakin razananen ihu, da sauri ta mike da ta tabbatar da ya hadiye ta matsa baya tana kuka tana fadin doctr dubashi,
da kyar doctor musah ya samu yayi mishi allurar da tasashi bacci ihun ya lafa,
ya waigo ya kalli oyizah yace hajiya I think ruwan adduar nan yasashi ya farfado gaba daya saidai kuma yanzu ne za'a fara jinyar, yasa kai ya fita..

Oyizah tayi dariya sosai tace ba dole ya farfado ba, na daďe ina jiran wannan ranar, ta kalli ruwan sosai tace nasan har yakai inda nakeso yakai,
ta harari affan ta fara shafa mishi ruwan a fuska tace kai da samun sauki har abada Affan..

Tun daga ranar ciwo ya dawo sabo, saboda kullum da ihu yake farkawa sai an mishi allurah ake samun saukin abun,
ciwon kanshi kuwa ya fara warkewa, dan gurin da yayi rami ya ciko sosai,
saida yayi sati ďaya kullum ya farka da ihu yake farkawa, daga ya farka kafin ayi mishi allura oyizah zata bashi maganin da tace ruwan addu'a ne,
Chapter 15 · 0% Book details