Sashe 24
Rabo Ajali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washe gari tun asuba oyizah taje gurin alhj basheer ido luhu2 saboda kuka da rashin bacci,
gaba ďaya ta rasa abinda zata yi a wannan daren saboda bata san ta inda zata fara ba tunda Affan baya gabanta,
alhj basheer ya ďago ya kalleta cikin bacci yace safiya lafiya, tace alhj naga kai baccinka ma kakeyi baka damu da yaron nan ba, ko bacci banyi ba saboda nasan da kyar in ya iya yin bacci,
alhj basheer yayi mika haďe da salati yace lafiyarshi kalau safiya yau a masallaci ma na samesu tare da kaka mahaifin alhj bara'u, rike ciki oyizah tayi hankali tashe tace a masallacin suka kwana?
Alhj basheer yace a'a sallahr asuba suka je, oyizah ta zauna dabass a kan gadon ta marairaice tace alhj inda zaka san irin missing din Affan da nakeyi da baka barshi ya kwana a wani guri ba, wallhy jiya banyi bacci ba dan daga na rufe ido shi kaďai nake gani,
kasan yadda na shaku dashi kuma nake jin tausayinshi, dan Allah ka tashi kaje ka dawo min dashi,
alhj basheer ya tausaya mata dan yasan tana iya kokarinta akanshi yace to bari in yi wanka zanje in dawo miki dashi,
ta saki wata dariyar murna tace nagode alhj bari in je in shirya mishi favourite break dinshi,
alhj basheer yayi dariya ya koma ya kwanta,
Daki oyizah ta koma cikin murna tace wannan karan mai gaba ďaya zanyi akan yaronnan dan bazai yiwu su dinga daga min hankali ba, gara in kashe shi ya bi abokinshi in huta da zulumi,
wata zuciyar ta haneta da sauri tace in kika kasheshi yanzu tayaya zaki samu dukiyoyin da alhj ya mallaka mishi, sannan in kika kasheshi hankalin mutane zai dawo kanki su zarge ki, gara kibi komai a hankali ki kara tsaurarawa akanshi ki maida shi mara amfani,
da wannan tunanin tayi yan tsaface tsafacenta na gaďo sannan ta wuce kitchen shiryawa Affan break...
Karfe 9 da kwata alhj basheer ya iso gidan rasuwar,
zaune ya samesu a cikin parlor sunyi shuru sai muryar Affan kadai akeji yana ma kaka liman hirar shirme,
dariya kawai kaka liman keyi yana tausayawa halin da Affan ke ciki,
da sallama alhj basheer ya shigo parlon ya tsuguna ya gaida kaka liman sannan suka gaisa da alhj bara'u,
alhj basheer ya kalli Affan yace ka tashi lafy,
Affan ya gyaďa mishi kai yace sosai ma tare da kaka mukayi bacci shi ya tashe ni yasa nayi wanka ya bani abinci ko kaka?,
kaka liman yayi murmushi yace kwarai dan kaka,
alhj basheer yace kace yau kai ďan gata ne, to tashi mu tafi gida mummynka na can tana missing dinka,
Affan ya noke wuya yace ni bazan je gida ba, alhj basheer yayi murmushi yace meyasa? Affan yace saboda har yanzu abokina bai dawo ba,
alhj basheer yace ay yana can gida yana jiranka kuyi wasa, Affan ya waro ido waje yace dagaske daddy, alhj basheer ya gyaďa kanshi yace dagaske nake,
Affan ya kalli kaka liman yace wai haka kaka, kaka liman yayi dariya yace haka ne,
Affan ya tashi da sauri yace muje daddy,
alhj basheer ya mike ya rike hannunshi yayi sallama da su kaka liman suka fito tare da alhj bara'u,
a bakin gate suka haďu da hajja rike da katuwar kular abincin sadaka,
da gudu Affan yaje gurin ta yana kokarin karbar kular hannunta, kauda kular tayi tana dariya tace bazaka iya ba Affan,
su alhj basheer suna dariya suka tsuguna suka gaisheta ta amsa haďe da kara yi musu gaisuwa,
alhj Bara'u yace ina Afeeyah dafatan jikin nata da sauki,
Hajja tace hmm sai dai addu'a tana can tun jiya take abu ďaya yanzu na baro mahaifinta yana mata rubutu,
alhj basheer yace kuka fa dole ne hajja shakuwar zaku duba, kai mutuwa, mutuwa mai yankan kauna,
Affan yace daddy Afeeyah ce ke kuka, alhj basheer ya gyada mishi kai,
Affan ya bata rai kamar zaiyi kuka yace daddy tun jiya fa take kuka kaje ka rarrasheta kace tazo muje gidanmu taga abokina muyi wasa tare,
alhj basheer yace to yanzu dai muje gida anjima zan je in rarrasheta sai in kawo maka ita gidan kaji,
Affan yayi dariya sosai yace gaba daya zata dawo gidan mu ko?, dama jabeer yace zai bani ita in ya aureta kuma kaima kace zaka aura min ita ay ko,?
sukayi dariya dukkansu alhj basheer yace eh zan aura maka ita wuce muje, ya fita yana tsallen murna,
sun kusa karasawa gidan ya rungume daddy yace daddy ka goyani kar inga lions, alhj basheer yace babu abinda zaka gani buďe idonka nasa an cire su, a hankali ya buďe idon yaga babu abubuwan da ya saba gani a kofar gidan, a tsorace ya shiga gidan yana zazzare ido,
jiki na rawa oyizah ta fito ta rungumeshi tana faďin oyoyo Affan ďina, nayi missing dinka ďana,
alhj basheer yayi dariya yace ai da kyar ya yarda ya biyo ni saida na ce mishi jabeer na nan gidan sannan,
oyizah tayi murmurshin mugunta tace muje ciki kaci abinci sai in nuna maka abokin naka, Affan yayi dariya ya bita suka shiga ciki,
Special break ta haďa mishi wanda yaji magunguna,
zaunar dashi tayi ta cika gabanshi da abinci ta diba a cokali zata fara bashi ya kauda kanshi yana rike ciki yace mummy munci abinci sosai tare da kaka har da kosai ma mai dadi, oyizah ta ajiye cokalin ta saci kallon alhj basheer da hankalinshi ke kan TV sannan ta kalli Affan tace haba baby na, baka so kaga abokin naka kenan Affan da sauri yace inaso mummy, tace oya open ur mouth kayi ko 1bs ne,
ya buďe bakinshi ta ďebo zata zuba mishi ya kara kauda kanshi da sauri yace ina zuwa mummy kaka liman yace in zanci abinci in dinga yin bismillah, da karfi yace "bismillah", oyizah ta buge bakinshi da karfi ba tare da tasan tayi ba,
washhhh Affan ya faďi da karfi yana kallonta idonshi ya fara kawo ruwa yace mummy me na miki,
ta dafe kanta tace Affan wadannan mutanen sun koya maka abubuwan da zai kasheka,
Affan ya fito da ido waje yace "kasheni" mummy?
Ta rage murya tace yess,
kaga wannan bismillahr da yace kayi, to daga ka kuma yinta zaka mutu,
Affan yace to ai jiya munyi sosai harda wani karatu ma duk munyi kuma ban mutu ba,
oyizah ta mike ta riko hannunshi tace zo muje in fada maka wata magana,
ya mike ya bita daki ta zaunar dashi gefen gado ta fara tsoratar dashi sosai akan sallah da wasu abubuwan da kaka liman ya koya mishi sannan tace mishi kasan inda abokinka yake, ya girgiza mata kai cikin tsoro tace to ya mutu kaga irin mutuwar da akeyi a cikin film mutum ya fadi ya daina motsi, Affan yace ehh, tace to shima ya tafi bazai kara dawowa ba saboda halin shi bashi da kyau, mugu ne so yakeyi ya kasheka shiyasa yake yawan zuwa yace kuje kuyi sallah,
Affan yayi narai narai da ido yace mummy ba mugu bane, yana kawo min cwts, baya dukana kuma baya min ihu kamar yadda su anty salma suke min,
oyizah tace muguntar kenan ay saboda yanaso ya kasheka wata rana shiyasa yake maka haka, amma kaga saboda am wit u gashi yanzu ya mutu har an kaishi rami, ka manta dashi kaji Affan din daddy,
Affan ya gyaďa kanshi hawaye suka sauka a kuncinshi wanda shi kanshi baisan yanda akayi suka fito ba, maganganu ta cigaba da yi mishi tana kara tsoratar dashi har saida ta tabbatar ya tsorata sannan ta kaishi ďaki ya kwanta tababbiyar zuciyarshi na karyata maganganunta akan jabeer,,
Daki ta koma tana sauke ajiyar zuciya dan ba karamin yaki tayi gurin sanyawa Affan tsoro a ranshi ba, a zuciyarta tace tabbas sai tayi da gaske dan mutuwar jabeer na neman karya duk wasu alkadarinta.....
Mrs tijjani shattima......
[15/12 09:37] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 3⃣6⃣ By Aysha Ya'u Kurah
Da sassafe alhj basheer ya shigo dakin ya tarar da Affan zaune a lallausan gadonshi yayi tagumi, a hankali ya cire hannun da yayi tagumin dashi yace me ya sameka dan daddy,
Affan ya kwanta kan cinyar daddy yace daddy Afeeyah tana can a gida tana kuka, ya ďago kanshi da ya ciko da kwalla yace daddy abokina ya zo yace in je in rarrasheta,
alhj basheer yayi murmurshi dan ya dauki maganarshi shirme yace in ji wa yace maka tana kuka,
Affan yace jabeer ne ya faďa min,
alhj basheer yace a ina kaga jabeer din,
Affan yace ana ruwan sama na ganshi a window na,
alhj basheer ya shafa kanshi cikin mamakin yadda akayi kwakwalwar Affan ta fara rike mafarki yace tashi kaje kayi wanka zan je in rarrasheta anjima,
Affan yace to daddy yaushe zata dawo nan gidan sai in dinga rarrashinta,
Alhj basheer yayi hanyar waje yace kayi wankan kazo ka karya tukunna,
Affan ya mike yayi hanyar bayi yana kallon window inda yaga jabeer cikin baccinshi amma shi ya kasa gane mafarki yayi dan ya hakikance a zahiri yaga jabeer,
bayi ya shiga yayi wanka ya jika ko ina kamar yadda ya saba har ya bude pampo zaiyi alwala kamar yadda kaka liman ya nuna mishi sai kuma ya fasa saboda tuno kalaman oyizah,
da sauri ya fito daga bayin ya shirya cikin matsatsun kaya...
Alamarin Affan ya fara bawa alhj basheer tsoro saboda kullum sai yayi mishi magana akan ya dawo mishi da Afeeyah gidansu, abinda yake fin bashi tsoro bai wuce yadda yake haddace mafarkan da yakeyi akan jabeer ba, yawan mafarkin da yakeyi ne ma yake hanashi tambayar inda abokinshi yake saboda yana ganin kamar a zahiri yake ganinshi,,, duk wannan mafarkin da Affan yakeyi bai taba faďa ma oyizah ba dan ko yazo zai faďa mata sai ya fasa ya kama harkar, daga shi sai mahaifinshi kadai suka sani...
gaba ďaya ta rasa abinda zata yi a wannan daren saboda bata san ta inda zata fara ba tunda Affan baya gabanta,
alhj basheer ya ďago ya kalleta cikin bacci yace safiya lafiya, tace alhj naga kai baccinka ma kakeyi baka damu da yaron nan ba, ko bacci banyi ba saboda nasan da kyar in ya iya yin bacci,
alhj basheer yayi mika haďe da salati yace lafiyarshi kalau safiya yau a masallaci ma na samesu tare da kaka mahaifin alhj bara'u, rike ciki oyizah tayi hankali tashe tace a masallacin suka kwana?
Alhj basheer yace a'a sallahr asuba suka je, oyizah ta zauna dabass a kan gadon ta marairaice tace alhj inda zaka san irin missing din Affan da nakeyi da baka barshi ya kwana a wani guri ba, wallhy jiya banyi bacci ba dan daga na rufe ido shi kaďai nake gani,
kasan yadda na shaku dashi kuma nake jin tausayinshi, dan Allah ka tashi kaje ka dawo min dashi,
alhj basheer ya tausaya mata dan yasan tana iya kokarinta akanshi yace to bari in yi wanka zanje in dawo miki dashi,
ta saki wata dariyar murna tace nagode alhj bari in je in shirya mishi favourite break dinshi,
alhj basheer yayi dariya ya koma ya kwanta,
Daki oyizah ta koma cikin murna tace wannan karan mai gaba ďaya zanyi akan yaronnan dan bazai yiwu su dinga daga min hankali ba, gara in kashe shi ya bi abokinshi in huta da zulumi,
wata zuciyar ta haneta da sauri tace in kika kasheshi yanzu tayaya zaki samu dukiyoyin da alhj ya mallaka mishi, sannan in kika kasheshi hankalin mutane zai dawo kanki su zarge ki, gara kibi komai a hankali ki kara tsaurarawa akanshi ki maida shi mara amfani,
da wannan tunanin tayi yan tsaface tsafacenta na gaďo sannan ta wuce kitchen shiryawa Affan break...
Karfe 9 da kwata alhj basheer ya iso gidan rasuwar,
zaune ya samesu a cikin parlor sunyi shuru sai muryar Affan kadai akeji yana ma kaka liman hirar shirme,
dariya kawai kaka liman keyi yana tausayawa halin da Affan ke ciki,
da sallama alhj basheer ya shigo parlon ya tsuguna ya gaida kaka liman sannan suka gaisa da alhj bara'u,
alhj basheer ya kalli Affan yace ka tashi lafy,
Affan ya gyaďa mishi kai yace sosai ma tare da kaka mukayi bacci shi ya tashe ni yasa nayi wanka ya bani abinci ko kaka?,
kaka liman yayi murmushi yace kwarai dan kaka,
alhj basheer yace kace yau kai ďan gata ne, to tashi mu tafi gida mummynka na can tana missing dinka,
Affan ya noke wuya yace ni bazan je gida ba, alhj basheer yayi murmushi yace meyasa? Affan yace saboda har yanzu abokina bai dawo ba,
alhj basheer yace ay yana can gida yana jiranka kuyi wasa, Affan ya waro ido waje yace dagaske daddy, alhj basheer ya gyaďa kanshi yace dagaske nake,
Affan ya kalli kaka liman yace wai haka kaka, kaka liman yayi dariya yace haka ne,
Affan ya tashi da sauri yace muje daddy,
alhj basheer ya mike ya rike hannunshi yayi sallama da su kaka liman suka fito tare da alhj bara'u,
a bakin gate suka haďu da hajja rike da katuwar kular abincin sadaka,
da gudu Affan yaje gurin ta yana kokarin karbar kular hannunta, kauda kular tayi tana dariya tace bazaka iya ba Affan,
su alhj basheer suna dariya suka tsuguna suka gaisheta ta amsa haďe da kara yi musu gaisuwa,
alhj Bara'u yace ina Afeeyah dafatan jikin nata da sauki,
Hajja tace hmm sai dai addu'a tana can tun jiya take abu ďaya yanzu na baro mahaifinta yana mata rubutu,
alhj basheer yace kuka fa dole ne hajja shakuwar zaku duba, kai mutuwa, mutuwa mai yankan kauna,
Affan yace daddy Afeeyah ce ke kuka, alhj basheer ya gyada mishi kai,
Affan ya bata rai kamar zaiyi kuka yace daddy tun jiya fa take kuka kaje ka rarrasheta kace tazo muje gidanmu taga abokina muyi wasa tare,
alhj basheer yace to yanzu dai muje gida anjima zan je in rarrasheta sai in kawo maka ita gidan kaji,
Affan yayi dariya sosai yace gaba daya zata dawo gidan mu ko?, dama jabeer yace zai bani ita in ya aureta kuma kaima kace zaka aura min ita ay ko,?
sukayi dariya dukkansu alhj basheer yace eh zan aura maka ita wuce muje, ya fita yana tsallen murna,
sun kusa karasawa gidan ya rungume daddy yace daddy ka goyani kar inga lions, alhj basheer yace babu abinda zaka gani buďe idonka nasa an cire su, a hankali ya buďe idon yaga babu abubuwan da ya saba gani a kofar gidan, a tsorace ya shiga gidan yana zazzare ido,
jiki na rawa oyizah ta fito ta rungumeshi tana faďin oyoyo Affan ďina, nayi missing dinka ďana,
alhj basheer yayi dariya yace ai da kyar ya yarda ya biyo ni saida na ce mishi jabeer na nan gidan sannan,
oyizah tayi murmurshin mugunta tace muje ciki kaci abinci sai in nuna maka abokin naka, Affan yayi dariya ya bita suka shiga ciki,
Special break ta haďa mishi wanda yaji magunguna,
zaunar dashi tayi ta cika gabanshi da abinci ta diba a cokali zata fara bashi ya kauda kanshi yana rike ciki yace mummy munci abinci sosai tare da kaka har da kosai ma mai dadi, oyizah ta ajiye cokalin ta saci kallon alhj basheer da hankalinshi ke kan TV sannan ta kalli Affan tace haba baby na, baka so kaga abokin naka kenan Affan da sauri yace inaso mummy, tace oya open ur mouth kayi ko 1bs ne,
ya buďe bakinshi ta ďebo zata zuba mishi ya kara kauda kanshi da sauri yace ina zuwa mummy kaka liman yace in zanci abinci in dinga yin bismillah, da karfi yace "bismillah", oyizah ta buge bakinshi da karfi ba tare da tasan tayi ba,
washhhh Affan ya faďi da karfi yana kallonta idonshi ya fara kawo ruwa yace mummy me na miki,
ta dafe kanta tace Affan wadannan mutanen sun koya maka abubuwan da zai kasheka,
Affan ya fito da ido waje yace "kasheni" mummy?
Ta rage murya tace yess,
kaga wannan bismillahr da yace kayi, to daga ka kuma yinta zaka mutu,
Affan yace to ai jiya munyi sosai harda wani karatu ma duk munyi kuma ban mutu ba,
oyizah ta mike ta riko hannunshi tace zo muje in fada maka wata magana,
ya mike ya bita daki ta zaunar dashi gefen gado ta fara tsoratar dashi sosai akan sallah da wasu abubuwan da kaka liman ya koya mishi sannan tace mishi kasan inda abokinka yake, ya girgiza mata kai cikin tsoro tace to ya mutu kaga irin mutuwar da akeyi a cikin film mutum ya fadi ya daina motsi, Affan yace ehh, tace to shima ya tafi bazai kara dawowa ba saboda halin shi bashi da kyau, mugu ne so yakeyi ya kasheka shiyasa yake yawan zuwa yace kuje kuyi sallah,
Affan yayi narai narai da ido yace mummy ba mugu bane, yana kawo min cwts, baya dukana kuma baya min ihu kamar yadda su anty salma suke min,
oyizah tace muguntar kenan ay saboda yanaso ya kasheka wata rana shiyasa yake maka haka, amma kaga saboda am wit u gashi yanzu ya mutu har an kaishi rami, ka manta dashi kaji Affan din daddy,
Affan ya gyaďa kanshi hawaye suka sauka a kuncinshi wanda shi kanshi baisan yanda akayi suka fito ba, maganganu ta cigaba da yi mishi tana kara tsoratar dashi har saida ta tabbatar ya tsorata sannan ta kaishi ďaki ya kwanta tababbiyar zuciyarshi na karyata maganganunta akan jabeer,,
Daki ta koma tana sauke ajiyar zuciya dan ba karamin yaki tayi gurin sanyawa Affan tsoro a ranshi ba, a zuciyarta tace tabbas sai tayi da gaske dan mutuwar jabeer na neman karya duk wasu alkadarinta.....
Mrs tijjani shattima......
[15/12 09:37] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 3⃣6⃣ By Aysha Ya'u Kurah
Da sassafe alhj basheer ya shigo dakin ya tarar da Affan zaune a lallausan gadonshi yayi tagumi, a hankali ya cire hannun da yayi tagumin dashi yace me ya sameka dan daddy,
Affan ya kwanta kan cinyar daddy yace daddy Afeeyah tana can a gida tana kuka, ya ďago kanshi da ya ciko da kwalla yace daddy abokina ya zo yace in je in rarrasheta,
alhj basheer yayi murmurshi dan ya dauki maganarshi shirme yace in ji wa yace maka tana kuka,
Affan yace jabeer ne ya faďa min,
alhj basheer yace a ina kaga jabeer din,
Affan yace ana ruwan sama na ganshi a window na,
alhj basheer ya shafa kanshi cikin mamakin yadda akayi kwakwalwar Affan ta fara rike mafarki yace tashi kaje kayi wanka zan je in rarrasheta anjima,
Affan yace to daddy yaushe zata dawo nan gidan sai in dinga rarrashinta,
Alhj basheer yayi hanyar waje yace kayi wankan kazo ka karya tukunna,
Affan ya mike yayi hanyar bayi yana kallon window inda yaga jabeer cikin baccinshi amma shi ya kasa gane mafarki yayi dan ya hakikance a zahiri yaga jabeer,
bayi ya shiga yayi wanka ya jika ko ina kamar yadda ya saba har ya bude pampo zaiyi alwala kamar yadda kaka liman ya nuna mishi sai kuma ya fasa saboda tuno kalaman oyizah,
da sauri ya fito daga bayin ya shirya cikin matsatsun kaya...
Alamarin Affan ya fara bawa alhj basheer tsoro saboda kullum sai yayi mishi magana akan ya dawo mishi da Afeeyah gidansu, abinda yake fin bashi tsoro bai wuce yadda yake haddace mafarkan da yakeyi akan jabeer ba, yawan mafarkin da yakeyi ne ma yake hanashi tambayar inda abokinshi yake saboda yana ganin kamar a zahiri yake ganinshi,,, duk wannan mafarkin da Affan yakeyi bai taba faďa ma oyizah ba dan ko yazo zai faďa mata sai ya fasa ya kama harkar, daga shi sai mahaifinshi kadai suka sani...