Sashe 80
Huriyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ita kam gaba da ta kai ta ko ba komai zata karya, ba kamar jiya ba, already ta san Momy ko masu aikinta za su ce mata abincin safe ya kare kamar jiya, gashi kuma bata isa ta ce zata shiga kitchen ta girka ba ko ta saka a girka mata. Dan haka ta sauko saman gadon suka fice a dakin tare da Khairy, kamin su isa bangaren Hajiya Kaltume Khairy ta kama hannunta ta rike tana bata labarin guraren da za su da kawayenta da ta kwana biyu bata hadu da su ba. A dinning suka zauna ita Khairy da kanta ta hadawa Hurriya tea ta zuba mata komai na karyawa. Hurriya na tauna wainar kwai zuciyarta na raya mata akwai abun da Khairy take shirya mata, domin a iya saninta Khairy bata tana sonta ba ko na rana daya, idan ma kowa zai raga mata a gidan ban da Khairy amman me yasa take nuna mata kulawa tana janta a jiki yanzu? Anya ba wani abu take shirya mata ba? Ta mike tsaye sai Khairy ta kalleta da sauri.
“Ya aka yi baki sha tea ba fa?”
“Ruwa zan dauko a kitchen”
“Zauna bari na dauko miki”
Ta mike tsaye, Hurriya kuma ta koma ta zauna tana kallonta, Khairy na shiga kitchen ta dauko ruwan da cup ta fito, sai mamaki ya kara rafe Hurriya. Haka dai ta karya ba dan zuciyarta natsu da yadda Khairy take mata ba.
“Yaya Khairy saboda Adam ne?”
Khairy ta kalleta
“Ban gane ba?”
“Kike min haka kuma kike son na rakaki mu fita”
“Haba Hurriya Adam din da Appa yace kar ya sake ganinki da shi, kuma yaya ma yayi gargadi akan haka, shi ne zan hadaku? Na rantse miki da Allah indai ni ce ba zaki taba ganin na kawo miki Adam da idonki biyu ba, haba Hurriya kawai ina kokarin ganin na kyautata miki ne, ni yar'uwarki ce be kamata ace muna samun tsabani ba, kin ga yanzu ni aure zan yi, duk kuwa da ba a saka rana ba, amman ban san ya rayuwata zata zama a gidan auren ba, kuma hausawa suna cewa idan kana son gani da kyau to ka aikata mai kyau, and trust me daga yanzu an fara kenan har gaban abada da yardar Allah sai kin ji cewar baki da wata yar'uwa kamar ni a duniyar nan”
Hurriya ta dan yi murmushi ba dan ta yarda ba.
“Amman ina tsoron wani abun da zai saka Appa yayi fushi ko yayi fada, musamman ma ni na batawa Appa rai da yawa idan an sake ban san abun da zai biyo baya ba”
“Hakan ba na fatan ya faru, komai zai zama labari Hurriya, tashi ki shirya da wuri dan bana son mu yi latti”
“Tou”
Ta tashi cikin sanyi jiki ta fice daga falon, ko da ta dawo bangaren Momy mai aikin gyara dakuna ta gyara mata dakinta ta fitar da plate din da ta ci abinci. Tufafinta kawai ta cire ta fada bandaki ta dauki lokaci a bandakin dakin tana Khairy, bata son zafafawa akan negative mind, dan haka take kyautatawa yar'uwarta zato. Ko da fito wanka wani bachi mai dadi ke ziyartarta haka dai ta murje ido ta hana kanta bachin ta shirya cikin ready-made bata damu da daukar jaka ba ganin bata da kudi ko wayar da zata saka a ciki, ta fito tana tafiya a hankali har ta sauko falon. Gaban Momy dake zaune a falon ta fara risinawa ta gaisheta.
“Momy ina kwana?”
“Lafiya kalau”
Ta amsa mata a takaice.
“Zamu fita da Khairy tace na rakata wani gurin”
Nan kam Momy bata ce mata je ko karki je ba, balle ta tambayi inda za su je, a lokacin da Hurriya ta gaji sai ta mike tsaye ta fice daga falon ga bachi ga hawayen da suka cika idonta suna son zubo mata, ba dan komai ba sai dan abin da Momy ta yi mata, ta tabbatar da uwarta ce ba zata bari ta fita ba ba tare da ta tambaye ta me za su je yi ina za su je yaushe za su dawo, ko ma ta hana ta zuwa gaba daya. Amman bata yi ba saboda ita din ba uwarta ba ce
“Na yi marmarinki Amma”
Ta fada tana tsayawa ta kalli bangaren da mahaifinyarta dake zama a da.
“Na yi marmarin rayuwarmu ta baya, a lokacin da kike nan kuma kike cikin koshin lafiya da farinciki, Hamad ma yake nan”
Ta sauke ajiyar zuciya tare da saka hannunsa ta share hawayen da suka zubo mata, sannan ta dauke kai ta shiga bangaren Hajiya Kaltume kamin ta karasa kofar falon Khairy ta bude kofar ta fito da nata shirin tana rike da keys din mota.
“Oh yanzu fa nake cewa zan biya na kiraki na ga kin dade ga garin da hadari”
Hurriya ta daga kai ta kalli sama dake cike da hadari da alama za a iya sako ruwa at any time kuma za a iya yaye hadarin duk cikin ikon Allah ne da abun da ya zo. Ta sauke kai tana hamma.
“Bachi ma nake ji?”
“Bachi yanzu? Ko zaki koma ki kwanta next time sai mu tafi”
“No mu tafi kawai zai sake ni ai”
“Okay”
Suka nufi motar Khairy sai da ta fara shiga ta yi mata key ta juya motar sannan Hurriya ta shiga suka kama hanya. At first Hurriya ta saka ido ne kawai tana sauraren inda Khairy zata kaita duk wani labari da take bata, bata yarda ya dauke mata hankali ba har suka isa gidan dake cike da yan mata suna ganin Khairy suka hau ihu ana rumgume juna irin an dade ba a hadu ba din nan, babu bata lokaci Khairy ta gabatar musu da Hurriya a matsayin kanwarta, Hurriya ta gaishe su sannan ta zauna. Aka kawo abubuwan tabawa ana ci ana hira, ita dai bata yarda ta ci komai ba domin zuciyarta bata natsu da gidan ba, kamar yadda bata gama yarda Khairy ba da sheri take bibiyarta. Tun suna abu tana binsu da kallo har ta kai ta kan yi dariya ko murmushi idan suka fadi wani abun ko suka yi wani abun, daya daga cikin kawayen Khairy ne ta dauko chewing gum ta mikawa kowa ciko har da Hurriya kowa ya karba ya ci, har dayar tana fadar a karo mata daya ba zai isheta ba.
“Zo ki karba idan kina da karfi, daman ke komai aka baki sai kin raina”
“Ni zaki cewa haka kam bala'i”
Suka fara kokawa da juna, Hurriya dai ta yi murmushi sauran kuma suna ta dariya, tana ta kallonsu gwanin burgewa rayuwarsu da alama babu mai wata damuwa a cikinsu sai nishadi suke ba kamar ita ba, tana tunani tana binsu da kallom sai hamma take har bacin ya fara fisgarta tun tana iya daga ido ta kallesu tana jin hayaniyarsu can cikin kamta har bachi ya sace ta gaba daya ta manta da wace duniyar take ma. Bachin da bata farka ba sai La'arsar shi ma kuma Khairy ce ta tashe ta saboda hadarin da ake da iska ruwan zai iya dadewa gashi basa gida.
“Kina ta bachi tashi mu tafi gida an fara ruwa”
Ta mitsintsika idonta kamin ta cire gilashin ta murza idon ta maida.
“Karfe nawa?”
Khairy ta duba agogo hannunta, Hurriya ma ta duba nata sai suka furta a tare.
“4:30pm”
Hurriya ta yunkura da karfi zata tashi sai ta ji jikinta da dan nauyi saboda ta dade kwance gashin kanta ma duk ya sha birjice saboda ta sha murja akan gadon saboda nauyin bachin da ta yi, har zuwa yanzu kuma be gama sakinta ba. Khairy ta mike tsaye tana laka jakarta
“Ya aka yi? Ko zaki ci abinci?”
Hurriya dake mika yana jin kamar ta kara yin bachi ta ce.
“Jikina yayi tsami”
“Taimaka mata ta tashi mana wanda ya dade kwance ai dole zai ji dabam”
Wata kawar Khairy dake daga zaune kan sofa tana kallon Hurriya da Khairy dake gurin bed ta fada. Khairy ta rika Hurriya ta mike tsaye.
“Baki tashe ni na yi sallah ba”
Ta fada har lokacin tana hamma.
“Bachi naki ne ya ga yayi nauyi shiyasa hala baki yi bachi jiya ba?”
“Na yi”
Ta fara takawa tana jin jikinta kamar ba nata saboda nauyin da yayi mata na bachin da ta sha.
“Kowa fa ya wuce mu kadai muka rage, ita wannan yar iskar gidansu ne bata da matsala”
Budurwa da Khairy ta fadawa haka ta mike tsaye tana dariya.
“Dan Allah yaushe zaku dawo?”
“Wa zai dawo nan yanzu kam ai sai dai a hadu a gidansu wata kuma, Hurriya cira kafa kar ruwan yayi karfi sosai da alama fa zai kai magariba ana yi”
“Eh gaskiya, tun dazun fa hadarin nan yake na dauka ma ma da rana za ayi ruwan”
“Eh Wallahi”
Kawar ta rakosu har Balcony, Khairy ta juya ta kalleta.
“Toh mu kam idan Momy ta zo ki ce muna gaisheta”
“Zata ji, Allah ya kiyaye sai mun yi waya”
Ta koma ciki su kuma suka nufi motarsu, Khairy na hadawa da gudu dan kar ruwan ya jikata Hurriya kam ta tsaya tana tafiyarta a hankali, wata zuciyar na raya abun da be zo mata a rai ba sai yanzu, why take ta jin bachi bayan kuma ita ta san jiya ta yi bachi ko da ma ace bata yi ba chi ba ai be kamata ta rika irin wannan mashalon da nauyin bachin just because of bata ta yi bachi ba na rana daya, balle ma ta yi. Kamin ta shiga motar ta raya ma zuciyarta cewar ba zata sake yarda ta sake raka Khairy wani gurin ba, domin idan wani abun be faru a yau ba, zai iya faruwa wata rana, kuma ta fi kyautata zaton wata kila kwaya ta saka mata ta yi bachi, waya sani ma ko so take ta koya mata shan wani abu, daman ana kishen kishen tana sha kuma ta lura da hakan domin ta ga tarin mutanen da ta tara a birthday ta babu na kwarai, gashi kuma Adam din da ya nuna yana sonta shi ma yana shan shisha.
“Ya aka yi baki sha tea ba fa?”
“Ruwa zan dauko a kitchen”
“Zauna bari na dauko miki”
Ta mike tsaye, Hurriya kuma ta koma ta zauna tana kallonta, Khairy na shiga kitchen ta dauko ruwan da cup ta fito, sai mamaki ya kara rafe Hurriya. Haka dai ta karya ba dan zuciyarta natsu da yadda Khairy take mata ba.
“Yaya Khairy saboda Adam ne?”
Khairy ta kalleta
“Ban gane ba?”
“Kike min haka kuma kike son na rakaki mu fita”
“Haba Hurriya Adam din da Appa yace kar ya sake ganinki da shi, kuma yaya ma yayi gargadi akan haka, shi ne zan hadaku? Na rantse miki da Allah indai ni ce ba zaki taba ganin na kawo miki Adam da idonki biyu ba, haba Hurriya kawai ina kokarin ganin na kyautata miki ne, ni yar'uwarki ce be kamata ace muna samun tsabani ba, kin ga yanzu ni aure zan yi, duk kuwa da ba a saka rana ba, amman ban san ya rayuwata zata zama a gidan auren ba, kuma hausawa suna cewa idan kana son gani da kyau to ka aikata mai kyau, and trust me daga yanzu an fara kenan har gaban abada da yardar Allah sai kin ji cewar baki da wata yar'uwa kamar ni a duniyar nan”
Hurriya ta dan yi murmushi ba dan ta yarda ba.
“Amman ina tsoron wani abun da zai saka Appa yayi fushi ko yayi fada, musamman ma ni na batawa Appa rai da yawa idan an sake ban san abun da zai biyo baya ba”
“Hakan ba na fatan ya faru, komai zai zama labari Hurriya, tashi ki shirya da wuri dan bana son mu yi latti”
“Tou”
Ta tashi cikin sanyi jiki ta fice daga falon, ko da ta dawo bangaren Momy mai aikin gyara dakuna ta gyara mata dakinta ta fitar da plate din da ta ci abinci. Tufafinta kawai ta cire ta fada bandaki ta dauki lokaci a bandakin dakin tana Khairy, bata son zafafawa akan negative mind, dan haka take kyautatawa yar'uwarta zato. Ko da fito wanka wani bachi mai dadi ke ziyartarta haka dai ta murje ido ta hana kanta bachin ta shirya cikin ready-made bata damu da daukar jaka ba ganin bata da kudi ko wayar da zata saka a ciki, ta fito tana tafiya a hankali har ta sauko falon. Gaban Momy dake zaune a falon ta fara risinawa ta gaisheta.
“Momy ina kwana?”
“Lafiya kalau”
Ta amsa mata a takaice.
“Zamu fita da Khairy tace na rakata wani gurin”
Nan kam Momy bata ce mata je ko karki je ba, balle ta tambayi inda za su je, a lokacin da Hurriya ta gaji sai ta mike tsaye ta fice daga falon ga bachi ga hawayen da suka cika idonta suna son zubo mata, ba dan komai ba sai dan abin da Momy ta yi mata, ta tabbatar da uwarta ce ba zata bari ta fita ba ba tare da ta tambaye ta me za su je yi ina za su je yaushe za su dawo, ko ma ta hana ta zuwa gaba daya. Amman bata yi ba saboda ita din ba uwarta ba ce
“Na yi marmarinki Amma”
Ta fada tana tsayawa ta kalli bangaren da mahaifinyarta dake zama a da.
“Na yi marmarin rayuwarmu ta baya, a lokacin da kike nan kuma kike cikin koshin lafiya da farinciki, Hamad ma yake nan”
Ta sauke ajiyar zuciya tare da saka hannunsa ta share hawayen da suka zubo mata, sannan ta dauke kai ta shiga bangaren Hajiya Kaltume kamin ta karasa kofar falon Khairy ta bude kofar ta fito da nata shirin tana rike da keys din mota.
“Oh yanzu fa nake cewa zan biya na kiraki na ga kin dade ga garin da hadari”
Hurriya ta daga kai ta kalli sama dake cike da hadari da alama za a iya sako ruwa at any time kuma za a iya yaye hadarin duk cikin ikon Allah ne da abun da ya zo. Ta sauke kai tana hamma.
“Bachi ma nake ji?”
“Bachi yanzu? Ko zaki koma ki kwanta next time sai mu tafi”
“No mu tafi kawai zai sake ni ai”
“Okay”
Suka nufi motar Khairy sai da ta fara shiga ta yi mata key ta juya motar sannan Hurriya ta shiga suka kama hanya. At first Hurriya ta saka ido ne kawai tana sauraren inda Khairy zata kaita duk wani labari da take bata, bata yarda ya dauke mata hankali ba har suka isa gidan dake cike da yan mata suna ganin Khairy suka hau ihu ana rumgume juna irin an dade ba a hadu ba din nan, babu bata lokaci Khairy ta gabatar musu da Hurriya a matsayin kanwarta, Hurriya ta gaishe su sannan ta zauna. Aka kawo abubuwan tabawa ana ci ana hira, ita dai bata yarda ta ci komai ba domin zuciyarta bata natsu da gidan ba, kamar yadda bata gama yarda Khairy ba da sheri take bibiyarta. Tun suna abu tana binsu da kallo har ta kai ta kan yi dariya ko murmushi idan suka fadi wani abun ko suka yi wani abun, daya daga cikin kawayen Khairy ne ta dauko chewing gum ta mikawa kowa ciko har da Hurriya kowa ya karba ya ci, har dayar tana fadar a karo mata daya ba zai isheta ba.
“Zo ki karba idan kina da karfi, daman ke komai aka baki sai kin raina”
“Ni zaki cewa haka kam bala'i”
Suka fara kokawa da juna, Hurriya dai ta yi murmushi sauran kuma suna ta dariya, tana ta kallonsu gwanin burgewa rayuwarsu da alama babu mai wata damuwa a cikinsu sai nishadi suke ba kamar ita ba, tana tunani tana binsu da kallom sai hamma take har bacin ya fara fisgarta tun tana iya daga ido ta kallesu tana jin hayaniyarsu can cikin kamta har bachi ya sace ta gaba daya ta manta da wace duniyar take ma. Bachin da bata farka ba sai La'arsar shi ma kuma Khairy ce ta tashe ta saboda hadarin da ake da iska ruwan zai iya dadewa gashi basa gida.
“Kina ta bachi tashi mu tafi gida an fara ruwa”
Ta mitsintsika idonta kamin ta cire gilashin ta murza idon ta maida.
“Karfe nawa?”
Khairy ta duba agogo hannunta, Hurriya ma ta duba nata sai suka furta a tare.
“4:30pm”
Hurriya ta yunkura da karfi zata tashi sai ta ji jikinta da dan nauyi saboda ta dade kwance gashin kanta ma duk ya sha birjice saboda ta sha murja akan gadon saboda nauyin bachin da ta yi, har zuwa yanzu kuma be gama sakinta ba. Khairy ta mike tsaye tana laka jakarta
“Ya aka yi? Ko zaki ci abinci?”
Hurriya dake mika yana jin kamar ta kara yin bachi ta ce.
“Jikina yayi tsami”
“Taimaka mata ta tashi mana wanda ya dade kwance ai dole zai ji dabam”
Wata kawar Khairy dake daga zaune kan sofa tana kallon Hurriya da Khairy dake gurin bed ta fada. Khairy ta rika Hurriya ta mike tsaye.
“Baki tashe ni na yi sallah ba”
Ta fada har lokacin tana hamma.
“Bachi naki ne ya ga yayi nauyi shiyasa hala baki yi bachi jiya ba?”
“Na yi”
Ta fara takawa tana jin jikinta kamar ba nata saboda nauyin da yayi mata na bachin da ta sha.
“Kowa fa ya wuce mu kadai muka rage, ita wannan yar iskar gidansu ne bata da matsala”
Budurwa da Khairy ta fadawa haka ta mike tsaye tana dariya.
“Dan Allah yaushe zaku dawo?”
“Wa zai dawo nan yanzu kam ai sai dai a hadu a gidansu wata kuma, Hurriya cira kafa kar ruwan yayi karfi sosai da alama fa zai kai magariba ana yi”
“Eh gaskiya, tun dazun fa hadarin nan yake na dauka ma ma da rana za ayi ruwan”
“Eh Wallahi”
Kawar ta rakosu har Balcony, Khairy ta juya ta kalleta.
“Toh mu kam idan Momy ta zo ki ce muna gaisheta”
“Zata ji, Allah ya kiyaye sai mun yi waya”
Ta koma ciki su kuma suka nufi motarsu, Khairy na hadawa da gudu dan kar ruwan ya jikata Hurriya kam ta tsaya tana tafiyarta a hankali, wata zuciyar na raya abun da be zo mata a rai ba sai yanzu, why take ta jin bachi bayan kuma ita ta san jiya ta yi bachi ko da ma ace bata yi ba chi ba ai be kamata ta rika irin wannan mashalon da nauyin bachin just because of bata ta yi bachi ba na rana daya, balle ma ta yi. Kamin ta shiga motar ta raya ma zuciyarta cewar ba zata sake yarda ta sake raka Khairy wani gurin ba, domin idan wani abun be faru a yau ba, zai iya faruwa wata rana, kuma ta fi kyautata zaton wata kila kwaya ta saka mata ta yi bachi, waya sani ma ko so take ta koya mata shan wani abu, daman ana kishen kishen tana sha kuma ta lura da hakan domin ta ga tarin mutanen da ta tara a birthday ta babu na kwarai, gashi kuma Adam din da ya nuna yana sonta shi ma yana shan shisha.