Sashe 44
Huriyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta masa banza, a abu mai muhimmanci ma Hurriya bata cika son amsawa ba balle na banza. Ya dan cize baki yayi murmushi.
“Shikenan zauna ba zan sake ba”
Bata zauna ba ta bar masa gurin tana rabon ido ko zata hango wanda ta sani ta zauna a kusa da shi.
“Wani kike nema?”
Wani ne kuma dabam yayi mata magana har kara wacan gayen da wannan domin wannan kansa ma wani kalar aski ne na yan iska. Shi ma dai bata ce masa na ta nufi gaba gaba ta inda Khairi zata hangota ko zata samu su daga mata kafa. Wani gurin ta nufa ta zauna tana kallon yadda yar'uwarta take rangaji kamar ta sha kwaya, gayen da ya fara yi mata iso ta hango ya isa gurin Khairi yana mata magana a kunne, kamin ya nuna gurin da take zaune har Khairiya ta kalleta ita ma ta mayar masa da maganar a kunne. Sannan ya sauko daga gurin ya nufi gurin MC, before she know sunanta ya cika gaba daya hall din.
“Ina Gimbiyar take, Hurriya ki fito kin yi farar tafiya daya daga cikin kananan matasan mu masu ji da kudi dan gidan Alhaji Buba Sarauta yana nemanki ya ce a kira masa kanwar Hajiyar ta mu wato Khairy domin ta taya yayarta murnar wannan birthday da take da kuma na graduation dinta”
Kowa sai ya fara rabon ido ana ta ga wayw Hurriya wacece Hurriya, Khairi kuma ta kasa boye mamakin dake fuskarsa, tambayarta sunan kanwarta da yayi ta fada masa bayan ya nuna mata ita bata dauka abun da zai yi kenan nan ba. Gaban Hurriya kamar zai fado tsabar bugawar da yake domin bata saba ba, irin haka ma be taba faruwa da ita ba. Kasa tashi ta yi ta rasa me zata yi ba zata iya zuwa gurin da aka bukace ba, bata san ma'anarsa na yin haka ba, so she decided to hide herself, tana kokarin janye kujerar ta boya karkashin teburin, gayen ya nufo inda take MC na biye da shi, hakan ya hanata boya sai kallonsa take ta cikin gilashinta tana jin ta ga abun da zai mata, gaba daya sai hankali ya dawo gurinta ita kanta Khairy sai ta sakar musu ido tana son ganin me ke shirin faruwa. Tun kamin ta karaso gurin da Hurriya take zaune ya cire rapper dollars ya fara bararwar har ya isa gurin da take ya tsaya akanta yana ta zuba mata dollars, idan suka kare sai ya dauko wata a aljihunsa ya cigaba da zuba mata, a take gurin ya dauki ihu aka fara daukarsu da manyan wayoyi wasu yan matan da suke crushing akansa kuma suka kasa boye kishinsu. Gaba daya mantawa aka yi da wani birthday party sai ihu ake ana daukar Hurriya, da gayen dake zuba mata kudin kamar be san zafinsu ba. Hurriya ta mike tsaye da sauri tana kallon Namra da sai a lokacin suka ga juna, bata tsaya komai ba ya nufi kofar fita ta fice daga gurin da gudunta, abun da ta yi ya bawa kowa a gurin mamaki domin at first wasu sun dauka ko budurwarsa ce, sai dai guduwar da tayi ya saka shakku a zukatan mutane. Khairy kan ta cika har tana kusan fashewa domin ta san saboda ita ya zo birthday even though ba saurayinta ba ne he's just her friend amman ta san kudin da ya zo da su ita ya kamata yayi ma kari da su gashi be yi ba ya karar da su gurin kanwarta.
Hurriya ta fito da sauri ta biyo hanya tsoro duk ya gama cika ta gaba daya ma a firgice take, hankalinta be kara tashi ba sai da ta iso titi, ko'ina tsit yake kamar babu mutane, arzikinta daya rana ce ba dare ba, wannan ya saka ta dan ji sauki. Juyawa ta yi kamar zata koma sai kuma ta ga ba mafita ba ce, tafiya ta fara yi tana rumgume da hannayenta sai ta ji an mata horn, juyowa ta yi ta kalli motar da bakin gilashi ya hana a ga wanda ke ciki. Ta juya ta cigaba da tafiya kamin ta tsake tsayawa kamakon fakawar da mai motar yayi gefenta ya sauke gilashin motar.
“Saboda na miki karin kudi zaki gudu? Idan ni ne ki koma ba zan sake ba”
Ta kalleta ta dauke kai ta cigaba da tafiya, shi ma tafiyar yake slowly cikin motar yana kallonta..
“Idan kuma gida kike son zuwa shigo na kai ki, you're not safe hare”
Kalmarsa ta karshe ta saka tsoron dake cikinta ya karu, ta dan karkato kadan ta kalleshi sai ya kai hannu ya bude mata front seat. Tsayawa ta yi kamar mai tunani shi ma sai ya tsaya daidai ita.
“Gida zan kai ki, shigo”
Ta kalli abun da ke aje a kasan inda mutum zai dora kafafuwansa idan ya shiga, sai yayi saurin kai hannu ya dauke ya jefata baya.
“Shisha ce please shigo”
Ita dai tun da take bata taba ganin tukunyar shisha a fili ba sai yau, tana dai ganinta a fina fina kuma ta san abun da ake yi da ita domin wadanda ake nunawa rike da ita sha suke suna fitar da hayaki.
“I'm Adam by name, please ki shigo mana Hurriya”
“Na gode zan kira yayana ya zo ya kai ni gida”
“So you get phone please saka min number ki a nan”
Yayi picking latest IPhone dinsa dake cikin motar ya cire key ya mika mata. Ta kalli wayar ta sake kallo sannan ta kai hannu ta karba without saying anything ta saka number yayanta daman daga numbersa sai ta Appa da Ammanta ta haddace a kai. Kara wayar ta yi a kunne
“Hello Yayana.. Ka zo ka dauke ni please ina jin tsoro kuma ina bakin titin gurin Event din ba kowa”
“Me ya fito dake to?”
“Ni na gaji ne bana son zama ciki gida nake so, kuma su ba su gama bikin ba babu wanda zai kawo ni”
“Okay ki koma ciki gani nan zuwa”
“Toh Yayana ka yi sauri ance I'm not safe here”
“Waya ce haka?”
Ta kalli mutumen dake jiran ta ba shi wayarta.
“Adam”
“Wane Adam”
“Ni ma ban san shi ba, yanzu na hadu da shi”
“Okay ina kusa da gurin koma ciki zan zo na dauke ki”
“Toh”
Ya kashe ya mika masa wayarsa.
“Thank You”
Ta juya ta cigaba da tafiyarta har ta koma ciki, wannan karon masu gadin ba su hanata ba domin sun gane ita ce ta dazun. Ciki ta koma ta samu gurin inda ba za a ganta ba ta zauna ta zubawa kofar shigowa ido Yayanta kawai take son gani. Tana hango Adam ya shigo ta kara boya kamar ta san ita zai fara nema, sai ko ya hau rabon ido yana neman inda zai ganta, gaba daya ta tafi da shi, a gurinsa duk abun da take tana masa yanga ne saboda ta ga tana da kyau. Ta yi rabin awa a gurin sannan ta tashi ta nufi kofa kamar mai shirin sata ta fice tana duddubawa ko Yayanta ya zo, aikuwa ta yi sa'a tana fitowa motarsa na shigowa harabar da sauri ta nufi shi yana fakawa ta bude front seat ta shiga.
“A tsorace kike Hurriya me ya faru?”
Ya tambaya yana kokarin kashe motar.
“Ba komai ni gida nake so”
“Ina Khairi ita da waye a gurin cikin yan gida?”
“Yaya Namra kawai na gani, sauran duk kawayenta ne ban sansu ba”
Ya duba agogo hannunsa.
“Su ma ai ya kamata ace kowa ya tafi gida yanzu, Je ki kirata”
“Yaya ba zata fito ba, kuma zata ce na bata mata birthday fa”
Ta saka mishi kuka domin ta san halin Khairy ko a banza ta dora mata laifi balle kuma da dalili.
“Karki ce ni nake kiranta, ki ce wani ne yake kiranta, idan ba haka ke ma sai na bata miki rai”
Ta fita motar ba dan ta so ba sai dan Yasir yayi mata dole, ciki ta koma ta isa har gurin da Khairi take tana rawa ana zuba mata kudi ta rikota ta kai bakinta kunneta.
“Wani yana kiranki a waje”
“Waye?”
“Ban san shi ba”
“Je ki ce masa ya shigo ciki”
Hurriya ta juyo, ita dai bata san yadda aka yi masu gadin suka bar Yasir ya shigo ba, sai hangon shi ta yi ya kankance ido yana kallon mutanen dake ta kai da kawo a gurin. Ta nufi shi ma ya nufo gurin Khairy da bata san me ke faruwa ba sai rawarta take ana zuba mata kudi. Galala Hurriya ta yi tana kallonsa ganin ya wuce ta ya nufi gurin Yayarta, yana isa be tsaya komai ba ya dauke Khairy da mari ya fara dukanta kamar an zugoshi.
“Wannan iskacin ne birthday? Kin mai da kanki kamar yar kafirai? Babu mutum daya mai mutumci a nan kim hada maza da mata ana shashanci ki cw birthday? Daman sai na hana Hajiya ta ce sai an yi saboda kawai ku ja mana zagi”
Dukanta yake ta ko'ina wadanda suka san yayanta suka fara ficewa da sauri, wasu suka suka fara kai mata dauki ciki har da ma'aikatan gurin.
HAJIYA KALTUME.
“Hello”
Hajiya Fatee ta amsa daga dayan bangaren.
“Hajiya ina ta kira baki daga ba”
“Yanzu na shigo dakin, kin gan ni garin sauri har faduwa na yi kamar an turo ni”
“Subhanallahi, sannu daman ina ta kira na ce miki Fadeel zai zo”
“Ya ma zo har ya tafi, ya ce wai kin ce ya zo ya kai Khairi bata samu mota ba”
“Eh haka na ce masa saboda na samu ya zo, wato Hajiya akwai abun da nake tunani sai dai gan gama yanke shawara ba sai kin zo, shiyasa da kika fada min zata birthday na fara da wannan”
Hajiya Kaltume ta yi murmushi tana murza kafarta dake zogi.
“Toh Hajiya Fatee kenan wato idan hagu ta ki a koma dama”
“Kwarai kuwa, idan ba zai iya rabuwa da wacan bakar karyar ba da ta dafa ta ba shi ya shanye, to ya karo wata idan ya auro wanda nake so ko da bakinciki ai sai ta bar gidan”
“Shikenan zauna ba zan sake ba”
Bata zauna ba ta bar masa gurin tana rabon ido ko zata hango wanda ta sani ta zauna a kusa da shi.
“Wani kike nema?”
Wani ne kuma dabam yayi mata magana har kara wacan gayen da wannan domin wannan kansa ma wani kalar aski ne na yan iska. Shi ma dai bata ce masa na ta nufi gaba gaba ta inda Khairi zata hangota ko zata samu su daga mata kafa. Wani gurin ta nufa ta zauna tana kallon yadda yar'uwarta take rangaji kamar ta sha kwaya, gayen da ya fara yi mata iso ta hango ya isa gurin Khairi yana mata magana a kunne, kamin ya nuna gurin da take zaune har Khairiya ta kalleta ita ma ta mayar masa da maganar a kunne. Sannan ya sauko daga gurin ya nufi gurin MC, before she know sunanta ya cika gaba daya hall din.
“Ina Gimbiyar take, Hurriya ki fito kin yi farar tafiya daya daga cikin kananan matasan mu masu ji da kudi dan gidan Alhaji Buba Sarauta yana nemanki ya ce a kira masa kanwar Hajiyar ta mu wato Khairy domin ta taya yayarta murnar wannan birthday da take da kuma na graduation dinta”
Kowa sai ya fara rabon ido ana ta ga wayw Hurriya wacece Hurriya, Khairi kuma ta kasa boye mamakin dake fuskarsa, tambayarta sunan kanwarta da yayi ta fada masa bayan ya nuna mata ita bata dauka abun da zai yi kenan nan ba. Gaban Hurriya kamar zai fado tsabar bugawar da yake domin bata saba ba, irin haka ma be taba faruwa da ita ba. Kasa tashi ta yi ta rasa me zata yi ba zata iya zuwa gurin da aka bukace ba, bata san ma'anarsa na yin haka ba, so she decided to hide herself, tana kokarin janye kujerar ta boya karkashin teburin, gayen ya nufo inda take MC na biye da shi, hakan ya hanata boya sai kallonsa take ta cikin gilashinta tana jin ta ga abun da zai mata, gaba daya sai hankali ya dawo gurinta ita kanta Khairy sai ta sakar musu ido tana son ganin me ke shirin faruwa. Tun kamin ta karaso gurin da Hurriya take zaune ya cire rapper dollars ya fara bararwar har ya isa gurin da take ya tsaya akanta yana ta zuba mata dollars, idan suka kare sai ya dauko wata a aljihunsa ya cigaba da zuba mata, a take gurin ya dauki ihu aka fara daukarsu da manyan wayoyi wasu yan matan da suke crushing akansa kuma suka kasa boye kishinsu. Gaba daya mantawa aka yi da wani birthday party sai ihu ake ana daukar Hurriya, da gayen dake zuba mata kudin kamar be san zafinsu ba. Hurriya ta mike tsaye da sauri tana kallon Namra da sai a lokacin suka ga juna, bata tsaya komai ba ya nufi kofar fita ta fice daga gurin da gudunta, abun da ta yi ya bawa kowa a gurin mamaki domin at first wasu sun dauka ko budurwarsa ce, sai dai guduwar da tayi ya saka shakku a zukatan mutane. Khairy kan ta cika har tana kusan fashewa domin ta san saboda ita ya zo birthday even though ba saurayinta ba ne he's just her friend amman ta san kudin da ya zo da su ita ya kamata yayi ma kari da su gashi be yi ba ya karar da su gurin kanwarta.
Hurriya ta fito da sauri ta biyo hanya tsoro duk ya gama cika ta gaba daya ma a firgice take, hankalinta be kara tashi ba sai da ta iso titi, ko'ina tsit yake kamar babu mutane, arzikinta daya rana ce ba dare ba, wannan ya saka ta dan ji sauki. Juyawa ta yi kamar zata koma sai kuma ta ga ba mafita ba ce, tafiya ta fara yi tana rumgume da hannayenta sai ta ji an mata horn, juyowa ta yi ta kalli motar da bakin gilashi ya hana a ga wanda ke ciki. Ta juya ta cigaba da tafiya kamin ta tsake tsayawa kamakon fakawar da mai motar yayi gefenta ya sauke gilashin motar.
“Saboda na miki karin kudi zaki gudu? Idan ni ne ki koma ba zan sake ba”
Ta kalleta ta dauke kai ta cigaba da tafiya, shi ma tafiyar yake slowly cikin motar yana kallonta..
“Idan kuma gida kike son zuwa shigo na kai ki, you're not safe hare”
Kalmarsa ta karshe ta saka tsoron dake cikinta ya karu, ta dan karkato kadan ta kalleshi sai ya kai hannu ya bude mata front seat. Tsayawa ta yi kamar mai tunani shi ma sai ya tsaya daidai ita.
“Gida zan kai ki, shigo”
Ta kalli abun da ke aje a kasan inda mutum zai dora kafafuwansa idan ya shiga, sai yayi saurin kai hannu ya dauke ya jefata baya.
“Shisha ce please shigo”
Ita dai tun da take bata taba ganin tukunyar shisha a fili ba sai yau, tana dai ganinta a fina fina kuma ta san abun da ake yi da ita domin wadanda ake nunawa rike da ita sha suke suna fitar da hayaki.
“I'm Adam by name, please ki shigo mana Hurriya”
“Na gode zan kira yayana ya zo ya kai ni gida”
“So you get phone please saka min number ki a nan”
Yayi picking latest IPhone dinsa dake cikin motar ya cire key ya mika mata. Ta kalli wayar ta sake kallo sannan ta kai hannu ta karba without saying anything ta saka number yayanta daman daga numbersa sai ta Appa da Ammanta ta haddace a kai. Kara wayar ta yi a kunne
“Hello Yayana.. Ka zo ka dauke ni please ina jin tsoro kuma ina bakin titin gurin Event din ba kowa”
“Me ya fito dake to?”
“Ni na gaji ne bana son zama ciki gida nake so, kuma su ba su gama bikin ba babu wanda zai kawo ni”
“Okay ki koma ciki gani nan zuwa”
“Toh Yayana ka yi sauri ance I'm not safe here”
“Waya ce haka?”
Ta kalli mutumen dake jiran ta ba shi wayarta.
“Adam”
“Wane Adam”
“Ni ma ban san shi ba, yanzu na hadu da shi”
“Okay ina kusa da gurin koma ciki zan zo na dauke ki”
“Toh”
Ya kashe ya mika masa wayarsa.
“Thank You”
Ta juya ta cigaba da tafiyarta har ta koma ciki, wannan karon masu gadin ba su hanata ba domin sun gane ita ce ta dazun. Ciki ta koma ta samu gurin inda ba za a ganta ba ta zauna ta zubawa kofar shigowa ido Yayanta kawai take son gani. Tana hango Adam ya shigo ta kara boya kamar ta san ita zai fara nema, sai ko ya hau rabon ido yana neman inda zai ganta, gaba daya ta tafi da shi, a gurinsa duk abun da take tana masa yanga ne saboda ta ga tana da kyau. Ta yi rabin awa a gurin sannan ta tashi ta nufi kofa kamar mai shirin sata ta fice tana duddubawa ko Yayanta ya zo, aikuwa ta yi sa'a tana fitowa motarsa na shigowa harabar da sauri ta nufi shi yana fakawa ta bude front seat ta shiga.
“A tsorace kike Hurriya me ya faru?”
Ya tambaya yana kokarin kashe motar.
“Ba komai ni gida nake so”
“Ina Khairi ita da waye a gurin cikin yan gida?”
“Yaya Namra kawai na gani, sauran duk kawayenta ne ban sansu ba”
Ya duba agogo hannunsa.
“Su ma ai ya kamata ace kowa ya tafi gida yanzu, Je ki kirata”
“Yaya ba zata fito ba, kuma zata ce na bata mata birthday fa”
Ta saka mishi kuka domin ta san halin Khairy ko a banza ta dora mata laifi balle kuma da dalili.
“Karki ce ni nake kiranta, ki ce wani ne yake kiranta, idan ba haka ke ma sai na bata miki rai”
Ta fita motar ba dan ta so ba sai dan Yasir yayi mata dole, ciki ta koma ta isa har gurin da Khairi take tana rawa ana zuba mata kudi ta rikota ta kai bakinta kunneta.
“Wani yana kiranki a waje”
“Waye?”
“Ban san shi ba”
“Je ki ce masa ya shigo ciki”
Hurriya ta juyo, ita dai bata san yadda aka yi masu gadin suka bar Yasir ya shigo ba, sai hangon shi ta yi ya kankance ido yana kallon mutanen dake ta kai da kawo a gurin. Ta nufi shi ma ya nufo gurin Khairy da bata san me ke faruwa ba sai rawarta take ana zuba mata kudi. Galala Hurriya ta yi tana kallonsa ganin ya wuce ta ya nufi gurin Yayarta, yana isa be tsaya komai ba ya dauke Khairy da mari ya fara dukanta kamar an zugoshi.
“Wannan iskacin ne birthday? Kin mai da kanki kamar yar kafirai? Babu mutum daya mai mutumci a nan kim hada maza da mata ana shashanci ki cw birthday? Daman sai na hana Hajiya ta ce sai an yi saboda kawai ku ja mana zagi”
Dukanta yake ta ko'ina wadanda suka san yayanta suka fara ficewa da sauri, wasu suka suka fara kai mata dauki ciki har da ma'aikatan gurin.
HAJIYA KALTUME.
“Hello”
Hajiya Fatee ta amsa daga dayan bangaren.
“Hajiya ina ta kira baki daga ba”
“Yanzu na shigo dakin, kin gan ni garin sauri har faduwa na yi kamar an turo ni”
“Subhanallahi, sannu daman ina ta kira na ce miki Fadeel zai zo”
“Ya ma zo har ya tafi, ya ce wai kin ce ya zo ya kai Khairi bata samu mota ba”
“Eh haka na ce masa saboda na samu ya zo, wato Hajiya akwai abun da nake tunani sai dai gan gama yanke shawara ba sai kin zo, shiyasa da kika fada min zata birthday na fara da wannan”
Hajiya Kaltume ta yi murmushi tana murza kafarta dake zogi.
“Toh Hajiya Fatee kenan wato idan hagu ta ki a koma dama”
“Kwarai kuwa, idan ba zai iya rabuwa da wacan bakar karyar ba da ta dafa ta ba shi ya shanye, to ya karo wata idan ya auro wanda nake so ko da bakinciki ai sai ta bar gidan”