← Book details Huriyya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 159

Sashe 34

Huriyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Ai daman wani abun haka yake, kin manta yadda muka yi na auren Iyami? Shi ma ai sai da kika fara korafin be yi be yi ba, har ya ce kin yi gajin hakuri, yanzu ba gashi ta tafi ta bar miki idan ba”

“Na yarda, tabbas ni kuwa zan saka masa da sakamako mai kyau, sai yayi alfahari da ni”

“Ni ma ai na fada masa idan yayi abun da zai raba auren Fadeel da Afrah sai na masa kyauta mai tsoka da sai ya kasa mantawa da ni, kuma ya ce zai yi, sai dai ta inda lamarin ya sanyaya min guiwa cewar da yayi idan yayi mata aika dawo masa ake da ita”

Hajiya Kaltume ta rike baki. “Ai kin san bata tsawaya kanta ba, ita ma shigen shigen take”

“Ai na sani, shiyasa ta mallake min da komai sai Afrah gaba daya baya jin maganar kowa sai nata, kuma bana da ikon zaginta a gabansa sai ya fara masifa, ni daman tun farko bana son aurenta da yaron nan Wallahi, Allah dai ya riga da kaddara ne kawai”

“Ki sa ido ki yi kallo kamar yadda Iyami ta bar gidana, Afrah ma sai ta bar gidan danki da yardar Allah”

“Haka nake fata Hajiya Allah ya amsa”

“Ameen”

Hajiya Kaltume ta aje wayar tana murmushi kamar wadda aka yi ma bushara.

“Hmmmm Iyami.... Lallai kin zama labari a gidan nan, yaranki ma da yardar Allah sai sun zama su da babu duk daya a gidan nan”

Ta nufi bakin gadonta ta zauna tana kokarin sake yin wani kiran Khairi ta shigo dakin ta zauna kusa da ita ta kwanta jikinta.

“Hajiya yaushe Ruma zata dawo ne?”

Hajiya ta yi saurin saka wayar key tare da gefenta.

“Babu jimawa Khairi, mahaifinki ne yace a bashi lokaci zai nemi ragi, kuma kin ga ai ana neman ragi a komai”

“Toh Hajiya da zai yarda da sai ya bada kudin ya karbo Ruma, albashi Hamad din a barsa sai an shirya daman ya fitini kowa a gidan nan”

“Ai kin san ba zai yarda ba, kuma mutane ma sai su saka mana ido, ace saboda uwarsa bata gidan ne, kara dai a karbo su tare gaba daya”

“Allah sarki Ruma, Allah dai ya tsare ta”

“Ya ma tsare In Shaa Allah ba za su mata komai ba, ai yarinya ce kuma kin ga ba ita kadai suka dauka ba ko dan ganin idon Hamad za su raga mata tun da dan'uwanta ne”

“Allah yasa”

“Ameen tashi kuje ku karya, ni wanka zan yi yanzu”

“Na karya ai”

“Yayi kyau Maama da Salma duk sun karya? Yayanki fa?”

“Ban sani ba gaskiya”

“Je ki fada masa ya fito ya karya”

Khairi ta tashi ta fice daga dakin, sai da Hajiya Kaltume ta tabbatar ta rufe kofar dakin sannan ta fiddo wayarta ta fara danne danne. Misalin sha daya na safe Bappa da Gwaggo suka dira a gidan, Bappa ya faka a harabar da ya saba fakawa duk lokacin da wani abu mai muhimmanci ya kawo shi gidan, duk kuwa da kasancewar Iyami bata gidan. Shi ya fara fita sannan Gwaggo ta fito tana sanye fa farin hijabinta.

“Ki fara shiga ki yi magana da Hajiya Kaltume a sallamo mana Alhaji mu yi magana da shi”

“Ko kuma dai ayi mana iso ba”

Gwaggo ta gyara masa domin a ganinta ba bara ko roko suka zo gurinsa ba da za ace a sallamo musu shi. Bappa dai be sake cewa komai ba domin be shirya musu da Gwaggo a yanzu ba, ya san duk gyaran da zai mata ba zata fahimta ba. Gwaggo ta daga kai ta kalli apartment din Amma da kyau sai ta ji ranta ya bace, domin a yanzu yarta bata cikin gidan ba kamar da ba. Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta fito ta nufi bangaren Hajiya Kaltume, ba dan zuwan ya zame musu na dole ba ba za su zo a gidan ba, musamman ma ita da Hajiya Kaltume har Hajiya Nafisa basa girmamawa, Hajiya Nafisa na yi musu kallon matalauta masu kwadayi Hajiya Kaltume kuma na yi musu kallon maciya amana wadanda suka hanata zaman lafiya da kwanciyar hankali, Appa ne mai girmamata idan yaje mata ko kuma ita ta zo gidan ya rasa ina zai dauke ta ya dora tsabar farinciki da girmamawa. Ta murda kofar falon ta shiga da sallama fuskarta dauke da damuwar data kasa boyuwa.

Salma da Maama suka amsa mata ba dan sun ga fuskarta ba, domin su ma ba girma suke bata ba. Yasir ya aje cup din hannunsa da sauri ya baro dinning din ya nufota yana mata sannu da zuwa har da dan risinawa.

“Sannu Yasir ya hakurin lamarin nan?”

“Alhamdulillah Gwaggo Bismillahi zauna”

Ya nufi kujerar da sauri ya dauke pillows din da suke kai ya mata mazauni.

“Ya gida ina Rukayya?”

“Gida Lafiya kalau, Rukayya ta tafi makaranta tun safe”

“Ya Hurriya da Amma?”

“Toh Alhamdulillah Hajiya Kaltume na ciki? Tare muke da Malam ai”

“Oh... Ya tsaya a waje?”

“Eh ai ba jimawa za mu yi ba, magana kawai za mu yi da Mahaifinku”

“Okay Salma shiga ki kira Hajiya bari na tafi gurin Bappa”

Salma ta motsa hanci ta mike tsaye ba tare da ta gaishe da Gwaggo ba ta nufi upstairs, Maama tun da ta kalli Gwaggo sau daya bata sake juyowa ba balle har ta gaishe ta. Ba abun mamaki ba ne a gurin Gwaggo domin sun saba yi mata haka kishi suke taya uwarsu. Daga kiran Hajiya Salma bata sauko ba balle Gwaggo ta san halin da ake ciki haka ta zauna a gurin har kusan minti ashiri sannan Hajiya Kaltume ta sauko tana sanye da wata gizna mai fari da baki irin ta mutanen nijar ta irin aikinsu a gaban rigar da ta sauko mata har guiwa.

“Gwaggo ce yau a gidan na mu”

“Ni ce, halan Salma bata fada miki na zo ba Hajiya Kaltume”

“Ta fada min ba shi na sauko ba? Ina dan abu ne shiyasa Allah yasa dai lafiya”

Gwaggo ta tabe baki ta girgiza kai.

“Ba lafiya ba kan, tun da kowa ya san abun da ya faru, tare muke da Malam muna son magana da Alhaji ne”

Hajiya Kaltume ta zauna tana yamutsa fuska irin an takura musu din nan, kamin ta fara magana da izza.

“Oh Allah sarki, dazun ma ai na ga Bappa ya kira Iyamin ma ta kira, Alhaji sai fada yake Gwaggo ba a haka, ku baku san shirinsa ba, kuna son daga masa hankalin ne kawai shi ma fa ya damu da yaran nan kuna neman ku daga masa hankali”

Gwaggo ta nuna Hajiya Kaltume da yatsa.

“Ke Kaltume ke kin sani ko ban haife ki ba, na yi kanwa da ke, dan haka na cancanci girmamawa a gareki ko dan Iyami”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi da ya fi kama da yar siririyar dariya.

“Wannan kuma ai da ne Gwaggo, yanzu babu wannan alakar, kuma da kuke neman daga mana hankali ni ma fa tawa yar tana can tare da Hamad aka sace su, ko kuma ita ba mutum ba ce?”

Gwaggo ta mike tsaye.

“Kwarai kuwa mutum ce, shiyasa ai na ganki kin sha wanka kina ta far'a da jindadi an sace miki auta, gashi nan ai ya nuna a fuskarki”

“Gwaggo karki gayan magana, to faduwa zan yi na yi birgima? Ko kuma an fada miki ni din kamar yarki ce Iyami da bata yarda da kaddara ba? Ai ma dai da kunya Wallahi ku tako gidan nan da sunan ganin Alhaji shi be nemu ba ku za su neme sa, abu dai kamar ba Fulani ba”

“Ba rokonsa muka zo akan ya ba mu wani abu ba, kuma ba zuwa muka yi akan ya maida Iyami ba, shi ne abun kunya, mun zo ne saboda Hamad, ai kin san ko an rabu idan akwai yaya kamar ba a rabu ba ne, sai hakuri Hajiya Kaltume Iyami dai ta zama murucin kan dutse, ta zama kadangaren bakin tulu, kuma ta zama ƙashin wuya bata haɗuwa bata amayuwa”

Maama ta juyo tare da tasowa daga dinning din zata fadawa Gwaggo magana Hajiya Kaltume ta yi saurin daga mata hannu.

“Babu ruwanki Maama je ki cigaba da cin abincinki, Allah dai baya baci zalinci da kuka min sai ya saka min macuta kawai masu abun kunya”

Hankali kwance Gwaggo ta ce.

“Ba mu da abun kunya, da muna da abun kunya mijinki ba zan lallaba ya nemi hada iri da mu ba, kuma Alhamdulillah ko yanzu kasuwa ta watse ɗan koli mai rabo ya ci riba, tun da ga ƴaƴa nan Allah ha raya su ya saka musu albarka”

Gwaggo na kaiwa nan ta kabe Hijabinta ta fice daga falon ta bar Hajiya Kaltume da ciwon rai. Ko da Gwaggo ta iso gurin Bappa na nasa masifar Yasir na bashi hakuri.

“Bappa ka yi hakuri Wata kila ransa ne a bace”

“Idan ransa ne a bace be san waye ni ba da zai fada min maganar banza?”

Gwaggo ta dubi Yasir ta dubi Bappa.

“Malam lafiya?”

“Yasir ya shiga ya kira min Alhaji Haruna, daker mutumen ya fito, kuma abun da yake fada min shi be da miliyan dari biyu da zai bada yanzu, kuma ina damunsa da kira ban san damuwarsa ba, ai ba Hamad kadai aka dauka ba har da yarsa amman mun daga masa hankali kamar Hamad ne kadai ďa, idan muna da kudin mu ba su mu karbo Hamad din har da rubuto min number mutanen ya turo min, wai shi ba zai bada kudi ba police sun ce za su karbo su”

“Hmmm Allah ya kyauta, tun da ya baka Number mu tafi Malam”

Yasir ya nufi Gwaggo cikin rashin jindadin abun da ya faru yana bata hakuri

“Gwaggo dan Allah ku yi hakuri, maybe damuwa ce ta yi ma Appa yawa, dan Allah ku yi hakuri ba halinsa ba ne Wallahi”

“Karka damu Yasir babu komai”

Gwaggo ta fada sannan ta bude motar ta shiga, Bappa yaja motar sai masifa yake ta yi domin yau Alhaji Haruna yayi masa abun da be taba masa ba.
Chapter 34 · 0% Book details