Sashe 30
Huriyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana jin haka sai ta saka dayan hannunta ta kwance hannunsa dake rike da nata.
“Tafi zan.... Iya... Shiga... Daga... Nan”
Be san bata gani gaba daya ba, a zatonsa tana gani dishe-dishe kamar da, dan haka be musa mata ba ya bude mata gate ta lalaba ta shiga, ya maida kofar ya rufe sannan ya koma cikin motar ya fice daga unguwar. Hannu Hurriya ta mika tana lalaba hanya, tare da amfani da zuciyarta tana ayyana yadda hanyar take a lokacin da take gani.
“Ke Hurriya...”
Ta ji muryar Rukayya sai wani sanyi ya ziyarceta. Ta karaso kusa da ita ta rika hannunta.
“Waya kawo ki? Mun ji an bude kofar gate ba mu ga an shigo ba shiyasa na fito na duba”
“Yaya Yasir ne ya kawo ni, ya tafi Mama Rukayya kai ni gurin Amma na”
“Me ya same ki Hurriya?”
“Kai ni gurin Amma please, bana gani yanzu bana iya ganin komai sai hudu, gaba daya idon ya rufe, na daina gani dishe-dishen ma”
“Innalillahi”
Rukayya ta fada tare da jan hannunta suka shiga ciki, Amman dake zaune dakin Gwaggo tana kwadon zogale ta aje kwanon zogalen ta yunkura da cikinta wata tara ta mike tsaye da sauri ganin Hurriya da hawaye a fuska kacha-kacha har ya bata gaban hijabinta, gata sanye da uniform din makaranta da bata cire ba kuma babu gilashi a idonta.
“Hurriya me ya same ki?”
Kunne da jikin da yayi kewar uwa ne kadai zai iya fahimtar yadda ruhu yake ji idan ya ji ko yayi arba da uwa.
“Amma ina kike?”
Ta saki hannun Rukayya ta fara lalaben inda take jin muryar Amma. Amma ta mika hannu ta rikota sai Hurriya ta rumgume ta ta kwanta jikinta tana wani irin kuka da ya saka Amma ta kasa rike kanta ita ta fashe da kuka.
“Me ya faru Hurtiya? Me ya same ki? Waya kawo ki? Me ya samu idon naki ina gilashinki”
Har Hurriya ta bude baki ta yi magana, zancen da Yasir yayi a waje ya fado mata a rai. Shi ma kenan ya ce ba zai iya sanar da Amma ba balle kuma ita da take yarta. Kamar an saka allura da zare an dinki bakin Hurriya haka ta zama, ta kasa furta komai kuma ma sai ya koma mata cikin zuciya hawaye kawai take ita yi.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”
Amma ta furta gabanta na bugawa da karfi. Ta san ba lafiya zata kawo yarta a irin wannan yanayin ba, kuma gashi ta kasa fadar komai sai rumgume ta take kamar zata shige jikinta.
“Hurriya yi a hankali mana, kin san akwai kanenki a jikinta, ko kuma ki zo ni na rumgume ki idan rumgumar kike so”
Gwaggo ta fada, sai Hurriya ta girgiza kai tana kara kankame Amma.
“Hurriya dukanki aka yi?”
Ta girgiza kai.
“Wani abu aka watsa miki a ido?”
Ta girgiza kai.
“Fada kika yi da wani?”
Ta girgiza kai.
“Dan Allah ki bude baki ki yi magana mana minene? Ko dai fada kika yi da Hamad? Na san zai iya cewa yayi miki mugun duka saboda bana gidan?”
Maganar da Amma ta yi ta Hamad ta saka Hurriya fashewa da sabon kuka.
“Yasir ya kawo ta, ta fa yi magana dazun yanzu ne dai ta kasa cewa komai”
“Wata kila fadan ta yi da Hamad shiyasa ta kasa fada tana tsoron kar na yi masa fada ya kara mata”
Zuciyar Amma ta fi aminta da fada suka yi da Hamad shi yasa har ta furta hakan, ganin Hurriya ta fashe fa kuka a lokacin da ta ambace shi.
“Kai Hamad yana da matsala Wallahi sai ace baka iya zaman lafiya fa yan'uwarka, ko tausayinta baya ji”
Rukayya ta fada. Sai Gwaggo ta ce.
“Kusan duk mabiyi da mabiyi haka ake, ba kowa ke shiri da juna ba”
“Amman dai shi nashi yayi yawa”
Amma dai ta yi shiru tana ta saurare numfashin Hurriyya dake fita da karfi..
FAMILY HOUSE...
A rikice Appa ya fito motar tun kamin direban sa ya gama fakin, ya nufi hanyar Falon Hajiya Kaltume cikin tashin hankali, hausawa suka ce ba a saka masa rana. Gaba daya kuka suke cikin falon har Namra da ta shigo. Hajiya Kaltume na ganin Appa ta kara mulmulawa a kasa tana dafa kai ta tashi zaune ta koma ta kwanta kamar wata bayarba...
“Eyyyy Eyyyy Eyyyy ni Kaltume yau na shiga uku yata, wayyo Umm Ruman, Alhaji ina cikin matsala da bala'i sun sace min yar auta, wai ni mi na yi ma mutane ne ne? Wayyo Allah na”
“Haba Hajiya ki yi hakuri mana, idan ke kina haka su kuma yara waye zai rarrashensu? Dan Allah ki tashi”
“Alhaji wasu sun tare mota sun tafi da Ruma”
“Hamad ma yana can hannunsu ai, ba ita kadai ba, kuma In Shaa Allahu zaku dawo lafiya”
“Mutanen nan ba su da imani shi Hamad ai namiji ne, ita kuma mace ce yarinyar yar shawalwala”
Appa ya zauna a kujera ya cire hular kansa duk sanyin ac falon gumi ne ke keto masa ta ko'ina. Salma da Khairi suka fara fada masa abun da ya faru suna kuka ba tare da ya tambaya ba, Kamin ya dago ya bi kowa da kallo.
“Ku daina mana kuka tun da ba mutuwa aka yi ba, ku yi ta addu'a, idan ma wani abun suke so ai dole za su kira. Ina Hurriya?”
Appa na rufe baki Yasir da shigowar falon kenan ya amsa masa.
“Yanzu na kaita gida?”
Appa ya masa wani kallo.
“Gida ina?”
“Gurin Amma tana ta kuka ta ce a kaita can, shiyasa na kaita amman ban shiga gidan ba”
Appa ya dafe kai cike da takaici kamin ya dago ya kalli Yasir yana jin kamar ya mareshi.
“Ban taba sanin baka da hankali ba, sai yau Yasir ka kaita ta fadawa Iyami abun da ya faru kamar baka san halin da Iyami take ciki ba? Ciki ne fa a jikinta kuma tsohon ciki idan ta fadi ta rikice wani abu ya same ta ko ya samu abun da ke cikinta kai zaka mata magani? Wani irin shashanci ne wannan?”
Yasir yayi shiru sai a lokacin shi ma yake ganin abun da yayi na kai Hurriya a irin wannan lokacin be dace ba. Hajiya Kaltume ta fashe da kuka.
“Haba Alhaji wake da Iyami yanzu an dauke min yar shawalwalar yarinyar, mace ce fa, al kara ma Hamad namiji ne”
Appa ya tashi ya fice, Yasir ya bi bayansa, daga gidan station suka nufa daman kamin su isa Appa ya kira CP ya fada masa abun da ya faru, suna isa ya saka aka shigar da report kamin yan sanda da suke sashen kidnapping su tafi gidan aka kwaso duka yaran, ana tambayarsu yadda abun ya faru suna fada. Babban cikin su dake tambayar ya kalli Namra da ta kare nata bayanin ya ce.
“Wacece Hurriya? Ina ita Huriyyar take?”
“Tana gidansu”
“Okay ita ba yar'uwarku ba ce?”
Appa yayi gyaran murya dan ya san Namra zata iya wata kwabar.
“Yata ce, ni na haifeta amma yanzu tana gurin mahaifiyarta da ta koma gida haihuwa”
“To zamu iya ganin ita Huriyyar? Domin ga dukan alama ita aka zo dauka, ita da Ruma din a yadda na fahimta Hamad din tsautsayi ne ya rutsa da shi, rashin samun Hurriyya sai suka dauke Hamad din, dole akwai tambayoyin da nake son yi mata”
“Ni ma na yi wannan tunanin duba da irin labarin da suka ba ni, zan je na zo da ita”
Appa ya fada sannan ya kalli Yasir.
“Idan an gama ka maida su gida, ni zan je na taho da Huriyya”
“To Appa”
Yasir ya amsa cikin ladabi da biyayya, Appa ya ma Officer sallama ya fice. Tare da direbansa suka isa gidan Gwaggo, a waje suka faka motar direban ya fito ya bude masa mota ya fito. A ransa yana son shiga amman jin hake kamar ana tsikara masa allura a zuciya saboda ya doso gurin da Amma take.
“Bala, ka sallamo Hurriyya”
“Toh ranka ya dade”
Malam Bala ya wuce cikin gidan, Appa kuma ya jingina da mota, Malam Bala be dade ba ya dawo yana sanar masa Gwaggo tace ya shigo tana son magana da shi. Rasa yayi me zai ce, shi dai be isa ya juya yayi tafiyarsa ba, kuma yana jin kunyar hada ido da iyayenta ita kanta Amma a yanzu kunyarta yake ji. Haka dai ya daure ya danne duk wani abun azabar da yake ji ya shiga cikin gidan, sai da ya hada da addu'a sannan ya samu courage din shiga har cikin falon Gwaggo. Be zauna ba sai da ya risina ya gaishe da ita kamar yadda ya saba, ba dan ta girme shi ba, sai dai ma shi ya girme ta, yana bata girmata ne tun a lokacin da ta zama sukurukarsa a yanzu ma be yada girmanawarba, domin har a yanzu sun din suna da kima da daraja a idonsa.
“Hurriya ta shigo tana ta kuka, amman bata yi magana ba har yanzu ta kasa fadar abun da ya faru, a baki Rukayya muka ji cewar Yasir ne ya kawo ta ma, kuma da kayan makaranta ta shigo, babu gilashi a idonta, yanzu kuma sai ga Malam Bala ya shigo wai kana kiran Hurriya shiyasa na ce ya shigo da kai ciki mu ji abun da ya faru domin mu ma hankalinmu duk a tashe yake”
“Gwaggo, ni ma kaina ban san abun da ya faru ba. Shiyasa na kira Hurriyar na ji ta bakinta”
“Can gida ba su fada maka komai ba.?”
Appa ya ki yarda su hada ido.
“Ba su fada min ba, Hurriya tana kusa?”
“Eh tana dakin mahaifiyarta, bari a kirata”
Gwaggo ta tashi ta fita. Bata jima ba Iyami ta shigo falo tana sanye da digon Hijab har kasa Hurriya na rike da hannunta. Appa na kallonsa sai gashi ya mike tsaye yana kallon cikin dake jikinta cikin wani yanayi na rashin jindadi.
“Na fada maka babu uwar da zata so yayan wasu kamar nata, yanzu wannan tashin hankali duk na minene? Ba komawa gidanka nake bukata ba kwanciyar hankalin yayana kawai nake bukata a yanzu...”
“Iyami zauna”
“Tafi zan.... Iya... Shiga... Daga... Nan”
Be san bata gani gaba daya ba, a zatonsa tana gani dishe-dishe kamar da, dan haka be musa mata ba ya bude mata gate ta lalaba ta shiga, ya maida kofar ya rufe sannan ya koma cikin motar ya fice daga unguwar. Hannu Hurriya ta mika tana lalaba hanya, tare da amfani da zuciyarta tana ayyana yadda hanyar take a lokacin da take gani.
“Ke Hurriya...”
Ta ji muryar Rukayya sai wani sanyi ya ziyarceta. Ta karaso kusa da ita ta rika hannunta.
“Waya kawo ki? Mun ji an bude kofar gate ba mu ga an shigo ba shiyasa na fito na duba”
“Yaya Yasir ne ya kawo ni, ya tafi Mama Rukayya kai ni gurin Amma na”
“Me ya same ki Hurriya?”
“Kai ni gurin Amma please, bana gani yanzu bana iya ganin komai sai hudu, gaba daya idon ya rufe, na daina gani dishe-dishen ma”
“Innalillahi”
Rukayya ta fada tare da jan hannunta suka shiga ciki, Amman dake zaune dakin Gwaggo tana kwadon zogale ta aje kwanon zogalen ta yunkura da cikinta wata tara ta mike tsaye da sauri ganin Hurriya da hawaye a fuska kacha-kacha har ya bata gaban hijabinta, gata sanye da uniform din makaranta da bata cire ba kuma babu gilashi a idonta.
“Hurriya me ya same ki?”
Kunne da jikin da yayi kewar uwa ne kadai zai iya fahimtar yadda ruhu yake ji idan ya ji ko yayi arba da uwa.
“Amma ina kike?”
Ta saki hannun Rukayya ta fara lalaben inda take jin muryar Amma. Amma ta mika hannu ta rikota sai Hurriya ta rumgume ta ta kwanta jikinta tana wani irin kuka da ya saka Amma ta kasa rike kanta ita ta fashe da kuka.
“Me ya faru Hurtiya? Me ya same ki? Waya kawo ki? Me ya samu idon naki ina gilashinki”
Har Hurriya ta bude baki ta yi magana, zancen da Yasir yayi a waje ya fado mata a rai. Shi ma kenan ya ce ba zai iya sanar da Amma ba balle kuma ita da take yarta. Kamar an saka allura da zare an dinki bakin Hurriya haka ta zama, ta kasa furta komai kuma ma sai ya koma mata cikin zuciya hawaye kawai take ita yi.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”
Amma ta furta gabanta na bugawa da karfi. Ta san ba lafiya zata kawo yarta a irin wannan yanayin ba, kuma gashi ta kasa fadar komai sai rumgume ta take kamar zata shige jikinta.
“Hurriya yi a hankali mana, kin san akwai kanenki a jikinta, ko kuma ki zo ni na rumgume ki idan rumgumar kike so”
Gwaggo ta fada, sai Hurriya ta girgiza kai tana kara kankame Amma.
“Hurriya dukanki aka yi?”
Ta girgiza kai.
“Wani abu aka watsa miki a ido?”
Ta girgiza kai.
“Fada kika yi da wani?”
Ta girgiza kai.
“Dan Allah ki bude baki ki yi magana mana minene? Ko dai fada kika yi da Hamad? Na san zai iya cewa yayi miki mugun duka saboda bana gidan?”
Maganar da Amma ta yi ta Hamad ta saka Hurriya fashewa da sabon kuka.
“Yasir ya kawo ta, ta fa yi magana dazun yanzu ne dai ta kasa cewa komai”
“Wata kila fadan ta yi da Hamad shiyasa ta kasa fada tana tsoron kar na yi masa fada ya kara mata”
Zuciyar Amma ta fi aminta da fada suka yi da Hamad shi yasa har ta furta hakan, ganin Hurriya ta fashe fa kuka a lokacin da ta ambace shi.
“Kai Hamad yana da matsala Wallahi sai ace baka iya zaman lafiya fa yan'uwarka, ko tausayinta baya ji”
Rukayya ta fada. Sai Gwaggo ta ce.
“Kusan duk mabiyi da mabiyi haka ake, ba kowa ke shiri da juna ba”
“Amman dai shi nashi yayi yawa”
Amma dai ta yi shiru tana ta saurare numfashin Hurriyya dake fita da karfi..
FAMILY HOUSE...
A rikice Appa ya fito motar tun kamin direban sa ya gama fakin, ya nufi hanyar Falon Hajiya Kaltume cikin tashin hankali, hausawa suka ce ba a saka masa rana. Gaba daya kuka suke cikin falon har Namra da ta shigo. Hajiya Kaltume na ganin Appa ta kara mulmulawa a kasa tana dafa kai ta tashi zaune ta koma ta kwanta kamar wata bayarba...
“Eyyyy Eyyyy Eyyyy ni Kaltume yau na shiga uku yata, wayyo Umm Ruman, Alhaji ina cikin matsala da bala'i sun sace min yar auta, wai ni mi na yi ma mutane ne ne? Wayyo Allah na”
“Haba Hajiya ki yi hakuri mana, idan ke kina haka su kuma yara waye zai rarrashensu? Dan Allah ki tashi”
“Alhaji wasu sun tare mota sun tafi da Ruma”
“Hamad ma yana can hannunsu ai, ba ita kadai ba, kuma In Shaa Allahu zaku dawo lafiya”
“Mutanen nan ba su da imani shi Hamad ai namiji ne, ita kuma mace ce yarinyar yar shawalwala”
Appa ya zauna a kujera ya cire hular kansa duk sanyin ac falon gumi ne ke keto masa ta ko'ina. Salma da Khairi suka fara fada masa abun da ya faru suna kuka ba tare da ya tambaya ba, Kamin ya dago ya bi kowa da kallo.
“Ku daina mana kuka tun da ba mutuwa aka yi ba, ku yi ta addu'a, idan ma wani abun suke so ai dole za su kira. Ina Hurriya?”
Appa na rufe baki Yasir da shigowar falon kenan ya amsa masa.
“Yanzu na kaita gida?”
Appa ya masa wani kallo.
“Gida ina?”
“Gurin Amma tana ta kuka ta ce a kaita can, shiyasa na kaita amman ban shiga gidan ba”
Appa ya dafe kai cike da takaici kamin ya dago ya kalli Yasir yana jin kamar ya mareshi.
“Ban taba sanin baka da hankali ba, sai yau Yasir ka kaita ta fadawa Iyami abun da ya faru kamar baka san halin da Iyami take ciki ba? Ciki ne fa a jikinta kuma tsohon ciki idan ta fadi ta rikice wani abu ya same ta ko ya samu abun da ke cikinta kai zaka mata magani? Wani irin shashanci ne wannan?”
Yasir yayi shiru sai a lokacin shi ma yake ganin abun da yayi na kai Hurriya a irin wannan lokacin be dace ba. Hajiya Kaltume ta fashe da kuka.
“Haba Alhaji wake da Iyami yanzu an dauke min yar shawalwalar yarinyar, mace ce fa, al kara ma Hamad namiji ne”
Appa ya tashi ya fice, Yasir ya bi bayansa, daga gidan station suka nufa daman kamin su isa Appa ya kira CP ya fada masa abun da ya faru, suna isa ya saka aka shigar da report kamin yan sanda da suke sashen kidnapping su tafi gidan aka kwaso duka yaran, ana tambayarsu yadda abun ya faru suna fada. Babban cikin su dake tambayar ya kalli Namra da ta kare nata bayanin ya ce.
“Wacece Hurriya? Ina ita Huriyyar take?”
“Tana gidansu”
“Okay ita ba yar'uwarku ba ce?”
Appa yayi gyaran murya dan ya san Namra zata iya wata kwabar.
“Yata ce, ni na haifeta amma yanzu tana gurin mahaifiyarta da ta koma gida haihuwa”
“To zamu iya ganin ita Huriyyar? Domin ga dukan alama ita aka zo dauka, ita da Ruma din a yadda na fahimta Hamad din tsautsayi ne ya rutsa da shi, rashin samun Hurriyya sai suka dauke Hamad din, dole akwai tambayoyin da nake son yi mata”
“Ni ma na yi wannan tunanin duba da irin labarin da suka ba ni, zan je na zo da ita”
Appa ya fada sannan ya kalli Yasir.
“Idan an gama ka maida su gida, ni zan je na taho da Huriyya”
“To Appa”
Yasir ya amsa cikin ladabi da biyayya, Appa ya ma Officer sallama ya fice. Tare da direbansa suka isa gidan Gwaggo, a waje suka faka motar direban ya fito ya bude masa mota ya fito. A ransa yana son shiga amman jin hake kamar ana tsikara masa allura a zuciya saboda ya doso gurin da Amma take.
“Bala, ka sallamo Hurriyya”
“Toh ranka ya dade”
Malam Bala ya wuce cikin gidan, Appa kuma ya jingina da mota, Malam Bala be dade ba ya dawo yana sanar masa Gwaggo tace ya shigo tana son magana da shi. Rasa yayi me zai ce, shi dai be isa ya juya yayi tafiyarsa ba, kuma yana jin kunyar hada ido da iyayenta ita kanta Amma a yanzu kunyarta yake ji. Haka dai ya daure ya danne duk wani abun azabar da yake ji ya shiga cikin gidan, sai da ya hada da addu'a sannan ya samu courage din shiga har cikin falon Gwaggo. Be zauna ba sai da ya risina ya gaishe da ita kamar yadda ya saba, ba dan ta girme shi ba, sai dai ma shi ya girme ta, yana bata girmata ne tun a lokacin da ta zama sukurukarsa a yanzu ma be yada girmanawarba, domin har a yanzu sun din suna da kima da daraja a idonsa.
“Hurriya ta shigo tana ta kuka, amman bata yi magana ba har yanzu ta kasa fadar abun da ya faru, a baki Rukayya muka ji cewar Yasir ne ya kawo ta ma, kuma da kayan makaranta ta shigo, babu gilashi a idonta, yanzu kuma sai ga Malam Bala ya shigo wai kana kiran Hurriya shiyasa na ce ya shigo da kai ciki mu ji abun da ya faru domin mu ma hankalinmu duk a tashe yake”
“Gwaggo, ni ma kaina ban san abun da ya faru ba. Shiyasa na kira Hurriyar na ji ta bakinta”
“Can gida ba su fada maka komai ba.?”
Appa ya ki yarda su hada ido.
“Ba su fada min ba, Hurriya tana kusa?”
“Eh tana dakin mahaifiyarta, bari a kirata”
Gwaggo ta tashi ta fita. Bata jima ba Iyami ta shigo falo tana sanye da digon Hijab har kasa Hurriya na rike da hannunta. Appa na kallonsa sai gashi ya mike tsaye yana kallon cikin dake jikinta cikin wani yanayi na rashin jindadi.
“Na fada maka babu uwar da zata so yayan wasu kamar nata, yanzu wannan tashin hankali duk na minene? Ba komawa gidanka nake bukata ba kwanciyar hankalin yayana kawai nake bukata a yanzu...”
“Iyami zauna”