← Book details Huriyya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 56 OF 159

Sashe 56

Huriyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Amman mai gadin daya karbo sakon ai cewa yayi yace ga sakon da yace zai aiko miki nan”

“Ban yi da shi zai aiko min da sako ba, Wallahi Allah Hajiya”

Khairi ya yamutsa fuska tana jan tsaki.

“Karya kike munafuka, baki hadu da shi a Mall ba, jiya ai sai da kika saka yayi ta min masifa sai da na kai miki waya kuka gaisa, amman yanzu kin wani narke kina rantsuwa kamar gaske, sannu kitse”

“Ni ba wani abu zan ce miki ba, zo ki dauki kayanki kamin Mahaifinki ma ya gani ace na hadaku”

“Ko dai yayi mistake ne, Wallahi ban yi da shi za a kawo min komai ba, Hajiya ki yarda da ni”

Khairi ta taba hannu.

“Yau ina Yaya yake ya zo ya ga abun da salihar nan take aikatawa ana ganin kamar sai mu kadai ne zamu aikata, gashi nan kin aikata fiye da na mu ma”

Hawaye ya fara saukowa Hurriya jikinta ya hau rawa, domin bata san yadda zata wanke kanta ba idan maganar ta kai ga Yayanta ko Appanta da take tsoro yanzu kamar mutuwa.

“Yaya Namra ma tana tsaye a gurin a kira ta a tambayeta”

Hajiya ta tabe baki.

“Ita da Yasir ai ko rai kika kashe ba zasu fada ba, saboda kin iya kirsa da munafurci da kalailayar mai rai kin bi kin lafe a jikinsu uwa macijiya, ni ba wani abun zan fada ba dauki kayanki ki tafi”

“Aa ni ba nawa ba ne”

“Daukar shi ne rufin asirinki Malam domin Wallahi idan baki dauka ba, Yaya na shigowa zan nuna masa su”

Hurriya ta mike tsaye ta iso gurin ta saka hannu ta dauki kwaton kwalin da aka yi ma kwalliya aka rubuta. From Adam to Hurriya in stylish way. Kuka be kamata ba sai da ta fita daga bangaren na Hajiya Kaltume sai ta zauna a balcony ta fara kuka marar sauti saboda ta san daukar ma zai zame mata laifi ne. Ta yi minti talatin a gurin sannan ta tashi ta nufi bangaren Momy, a bude ta samu kofar falon, a lokacin da ta shiga babu kowa a cikin falon, sai ta maida kofar ta rufe, ta nufi stairs tana jin kamar ace Adam din yana kusa da ita ya yakuta masa fuska ta yaga tufafinsa ta watsa masa ruwa da yawu a jiki da fuska, tana tunanin haka ne iya karshen wulakanci. Maida kofar dakinta ta yi ta rufe ta zauna bakin kofar ta fashe da kuka kuka sosai mai sauti, domin gaba daya ta rasa ma ya zata yi, ta kira Yayanta ta fada masa kamin Hajiya ko Khairi su fada masa ko kuma ta samu Appa da kanta ta yi masa bayani, ko kuma dai ta zauna a gurin har sai an nemeta. Sai da ta ci kukanta ta koshi sannan ta ďa ga daga ta tura kwalin karkashin gadonta bata ma tsaya duba meye a cikinta. Ta shiga bathroom ta wanke fuskarsa ta fito ta kwanta saman gadonta, ana daf da kiran sallah Magariba Momy da Khairi suka dawo gidan, ita dai tana dakinta bata leko ba, abun duniya ya isheta, saurare kawai take ta ji an aiko cewar Appa ko Yayanta yana kiranta.
Immediately after gama Sallah Magariba tana zaune saman carpet din da ta yi sallah, Namra ta turo kofar dakin ta shigo cikin yanayin damuwa.

“Hurriya wa kika bari ya shiga dakin Momy da nawa?”

Hurriya ta dago ta dubeta ta cikin gilashinta.

“Babu wanda ya shiga”

“Tuna dai ko wani shiga?”

“Babu wanda ya shiga Yaya Namra me ya faru?”

Kamin Namra ta amsa mata Momy ta shigo dakin a kufule fuska kamar bakin hadari, ta nufi wardrobe dinta ta fara watsa tufafi tana zubarwa a kasa, kamin ta juyo ta yi gurin gadonta ta daga Bedsheet din, sai kuma ta juyo ta kalli Namra.

“Ke sauka ki kira min masu aikin nan”

Namra da rashin jindadin abun da Momy take yi ya bayyana a fuskarta ta ce.

“Momy dan Allah mu bi abun nan a hankali”

“Zaki sauka ki kira su ko sai na bata miki rai?”

Namra ta juya da sauri, domin ta fi kowa sanin yadda Momy take idan ranta ya bace. Hurriya dai na zaune a gurin da ta yi Sallah faduwar gabanta a yanzu ya fi na kallum, duk wani sake sake da take a ranta na dalilin shigowar Momy a dakin da kuma tambayar da Namra take mata be kawo mata cewar zarginta ake da abun da bata taba aikatawa ba ko a mafarki, har sai da masu aikin har uku suka shigo dakin.

“Ku bincika min ko'ina na dakin nan, ku duba min sarkar Namra da tawa da kuma kudin”

Hurriya ta mike tsaye da sauri irin mikewar nan kamar wanda aka lakawa wutar nepa.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, ni kuma? Momy ni...? Momy ban taba ba, Wallahi ban dauka ba, Momy ban zan miki haka ba”

“To waya aikata? Da zan fita waye na bari a bangaren? Waya shigo ya dauka?”

Hawaye ya fara mata zuba.

“Ban sani ba Wallahi amman ban dauka ba, ban taba sata ba Momy ko tsintuwa ban taba yi ba, balle har na shiga dakinki na dauki kudi ko sarkar zinari, dan Allah karku min haka, idan baku son zama na a gidan nan ku kure ni amman dan Allah karku laka min abun da ban yi ba”

Namra ta ta yi saurin rika Hurriya dake kuka kamar zata narke.

“Momy da dai an zafafa bincike Hurriya bata taba daukar abu ba, kuma a jininmu babu barawo”

“To waya dauka? Shekarata nawa da masu aikin nan balle har ace su suka yi”

“Haba Momy taya zaki shaidi bari ki bar na gida, Wallahi Hurriya ba zata dauka ba”

“Ke fice ki ba ni guri, ba ke da bakinki kika fada min Hurriya ta tambaye ki kudi ba? Kuma su ma sai na saka an duba dakunansu ai sai an bincika ko'ina na gidan nan”

“Eh amman bana jin Hurriya zata aikata haka Wallahi, kuma wannan ai na dabam ne, a maganar da na yi miki na ni na fi zaton ko zata siye anko ne ko wani abu dabam”

Momy ta watsawa Namra wata kalar harara da ke karantar da ita ranta yayi kololuwar baci, ita kuma zata iya bata nata rai a take. Ganin haka ya saka Namra sauka ta kira masu aikin, Momy na tsaye aka fara binciken dakin Hurriya tana ta kuka, sai da aka daga komai aka bincike har kwalin da Adam ya kawo mata sai da aka bude ba aga kudi ko sarka ba.

“Wato har da soyayya kike da wani a boye ko?”

“Aa aa aa sako ya kawo min, na je bangaren Hajiya na karbo kuma ban san zai aiko da sakon ba”

Ta amsa daker tana kuka sosai.

“Oh to ke kika bar min kofar daki a bude kenan aka dauka min sata, ko kuma kika sata”

“Na ga kofar a bude lokacin da na dawo kuma ban ga kowa a falon ba, amman Wallahi ban dauka ba”

Still Momy bata yarda da ita ba saboda tana ganin ita ma ai talaka ce kuma mabukaciya saboda halin da Amma take ciki, kuma gashi Appa ya daina kula da ita.

*I know littafin nan zai fito, i know zai yi yawo har ya iso gareki. Na fada kuma zan saki repeating Wallahi duk wanda ya karanta min littafi ba tare da ya biya ba, na barshi da mai mafaɗar rana da fitowarta. Daga masu sharing har masu karantawa ba tare da biya ba na barku da Allah...!*

Yadda Momy ta saka aka bincike dakin Hurriya haka ta saka aka bincike, dakunan masu aikinta, a nan ma ba a samu sarka ba, ba a samu kudi ba. Daga nan kuma sai labari ya canja Momy ta fara zargi ko Hajiya Kaltume ce ta aiko aka shigar mata daki saboda ta aiko kiran Hurriya, a karfin hali da nuna isa irin na Momy ta aika da masu aikinta kai tsaye a bangaren Hajiya Kaltume wai su bincike mata komai na bangaren saboda an dauke mata sarkar zinari mai tsada da kudi mai kauri, a nan Hajiya Kaltume ta fara nata masifar ta inda take shiga ba ta nan take fita ba, ita da Khairi, har Yasir abun be masa dadi ba ganin an lakawa mahaifiyarsa sata. All this while kuma Hurriya na dakinta tana rusar kuka abun ya zame mata biyu ta rasa gurin jin sanyi, domin ta san a yadda mahaifinsa ya tsane ta yanzu zai iya yarda ta dauki kudin, gashi bata san yadda zata yi ta fidda kanta ba, secondly ga gift din da Adam ya aiko mata ta san Khairi sai ta fadawa Appanta. Kuka take sosai kamar ranta zai fita gaba daya ta gama fita daga hayyacinta tunani ma ta rasa wanne zata yi.

9:30pm Appa ya aiko kiranta bayan kowa ya hallara a falonsa, cikin matukar tsoro da firgici ta fito daga bangaren Momy tana tafiya kafafuwanta na yin kamar za su zameta. Hankalinta be kara tashi ba sai da ta shiga falon ta ga kowa yana nan ciki har da Yayanta da Hajiya Kaltume mai karawa miya gishiri, ga kuma Momy da ta rumgume hannaye ta hakimce babu alamar sassauci a tare da ita, sanin kanta ne a yanzu babu wanda zai wanketa domin babu mai kaunarta a gidan, kuma bata da tabbacin za su shaideta, dan haka ta bi shawarar dake karya mata zuciya. Idonta yana a gurin mahaifinta tana kallonsa zuciyarta na rawa kalaman da za su fito daga bakinsa kawai take saurare. Sai da ta zauna kusa da Ruma sannan Appa ya dubeta duba na tsanaki ya ce.

“Hurriya ina son ki fada min gaskiya, na san baki taba min karya ba, kin shiga dakin Nafisa a lokacin da ta fita ko dakin Namra”

“App...”

Ta kasa karasa furta sunansa ma saboda kukan da ya ci karfinta, hawaye kam ko kai waye sai ka tausaya mata yadda take zubar da su.

“Kin shiga”

“Ta girgiza kai”

Sai Hajiya Kaltume ta kada baki ta ce.
Chapter 56 · 0% Book details