Sashe 40
Huriyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Lafiya kika tsaya nan kika zuba min ido? Mahaifinki ma baki da amfani a gurinsa yanzu balle kuma ni, wuce ki tafi dakinki tun da an kawo min kaya ya zan yi, Iyami ta haifa mana ta tafi ta bari”
Huriyya ta dauke kai da sauri ta fara tafiya, sai kuma Momy ta kirata.
“Hurriya”
Ta juyo a hankali ta kalleta ta kasa amsawa har lokacin hawaye take.
“Zo ki zauna yi hakuri kinji”
Hurriya ta dawo ta zauna saman kujerar dake dama da Momy.
“Gaskiya dai Alhaji ya ci amanarki Wallahi, ni ai ko da bala'i sai na karbi yayana, ko da yake Iyami ba zata iya ja da Alhaji ba, ta ina talauci zai ja da arziki, amman dai gaskiya be dace ya rabaki da Iyami yanzu ba, ai sai tunanin ya hade miki ga na dan'uwa ki kamu da hawan jini da kurciyarki, kai Kaltume bata da imani, haka fa ta raba Sapna da ubanta, Sapna bata isa ta tako garin nan ta ce zata zo gurin ubanta ba, tana can kauye cikin talauci shi kuma ya kyaleta... Hmmmm”
Ta mike tsaye tana kwalawa mai aikinta kira.
“Bilki”
Tsohuwar ta fito da gudu daga kitchen, daman haka take da yan aiki idan tana falo sai dai su boya a wani guri bata zama daki daya da su, idan har ka gansu a falo to tana dakinta ne ko kuma ta fita.
“Hajiya ga ni”
“A dauke plate din nan kuma ga yar Iyami nan idan zata ci abinci a zuba mata”
“Toh Hajiya”
Tsohuwar ta dauke plate din sannan ta kalli Hurriya dake zaune.
“Hurriya a zuba miki abinci?”
Hurriya ta girgiza kai alamar aa, Momy tabe baki ta dauki wayarta.
“Dan kan masa in ji sure, cikinki ko na wani, kin san dai ba rarrashinki zan yi dan ki daina kuka ko ki ci abinci ba, ina da tausayi da zuciyar imani amman laisa son dan wani kamar nawa kam karya haram babu boye boye ba munafurci, shiyasa ni na fi sha'awar uwarku ta dawo ta rike yayanta”
Tana fadan tana hawa sama har ta haye ta shige dakinta, Mai aikinta kam tuni ta san inda dare yayi mata. Hurriya ta bi ta kallo har ta haye stairs din, ji ta yi kamar ace wani na nan ta fada jikinsa ya rumgume ta yi kuka ammab babu wannan damar, saukowa ta yi daga saman kujera ta zauna kasa sai ta dora kanta sama kujera ta takure guri daya. Ta rufe ido hawaye na sauko mata. After like 30min ta ji an zungureta sai ta farka da sauri gilashin idonta ya fadi da sauri ta dauka ta saka ta gyara mayafin abayarta ta kalli Musib dake tsaye kanta.
“Miye na yi ma mutane bachi a kujera kin wani takure salon wani ya shigo ace ke ce marar gata a gidan ke ga munafuka, wato kin dawo babu zaman lafiya, mun rabu da Hamad ke kuma zaki kirkiri mugun abu ko?”
Kamar wani mace haka yake fada da ita yana gautsina fuska, gently ta mike tsaye domin ita ma bata san bacci ya dauke ta sai da ya tasheta. Tafiya ta fara yi ta haye sama ta dade a tsaye tana kallon kofar dakin Hamad tana jin kamar idan ta tura zata ganshi kwance ya ba kofar baya kamar yadda ya saba kwanciya. Wani hawayen ya sake cika idonta wani abu mai kama da dutse ya tsaya mata a tsakiyar zuciya ya mata nauyi. Cikin karfin hali ta kai hannu ta tura kofar dakinta ta shiga sai da maida kofar ta rufe ta jingina jikin kofar ta rumgume hannayenta not knowing what to do ita dai ba kuka take ji ba a yanzu, hawaye ne kawai ke mata zuba, tunanin dake mabanbantan duniyoyi ya hade mata guri daya, idan ta tuna Hamad ta tuna Amma, ta tuna Appa. Jin ta yi an yi knocking kofar dakin wani abu mai kama da tsoro ya fisgeta ta tashi tsaye da sauri jikinta na rawa ta yi baya tana kallon kofar, Namra ce ta turo kofar ta shigo da far'arta.
“Hurriya kin dawo”
Kamin ta rufe baki Yasir ya shigo cikin yanayi na damuwa yana kallonta.
“Hurriya”
Ta kasa amsawa Namra balle Yasir da ya shigo bayanta, ta hade yawu da karfi tana kallonsu. Yasir ya nufi gadonta ya zauna ya rasa me zai ce mata shi kansa be jin dawowarta gidan a yanzu mafita ne a gareta, babu yadda be yi ba wajen ganin ya fahintar da Hajiya Kaltume akan ta hana Appa dauko ta amman ta kasa fahimtarshi.
“Hurriya zauna”
Ta zauna a gurin kamar wata wadda tunani ya birkicewa kwakwalwa. Namra dai ta tsaya jikin kofar ita ma tara ran duk babu dadin ganin yar'uwarta cikin damuwa.
“Hurriya ki yi hakuri dan Allah, idan kina kukan nan sai ki saka kanki a damuwa”
Yasir ya daga ma Namra hannu alamar ta daina maganar sai ta yi shuru ta juya ta fice daga dakin, dan zumudin da ta zo da shi na murnar dawowar Hurriya sai ya gushe.
“Hurriya kina son zama nan ko kin fi son zama gurin Amma? Idan gurin Amma kike so zan mu tafi tare da ni dake mu yi ma Appa magana, idan be amince ba sai mu fadawa Hajiya Binta”
Ta girgiza kai alamar bata aa.
“Kina son zama nan din?”
Ta daga masa kai.
“Shi ke nan zo ki kwanta, kin yi sallah ko?”
Ta amsa masa da kai sannan ta nufi gadon ta kwanta shi kuma ta tashi ya fice, kai tsaye bangaren mahaifinsa ya nufa sai dai yayi rashin sa'a be tararda shi ba, domin tuni ya fita after ya kai Hurriya bangaren Momy daman ita kawai yake jiran a dawo da ita gidan ya fita, saboda Hajiya Kaltume ta fada masa idan be yi da gaske ba Amma ba zata ba shi Hurriya ba.
Hurriya bata tabbatar da mahaifinta ya daina yayinta ba sai da ya canja mata makaranta ya saka ta makarantar government, yayinda sauran yan'uwanta da suke ajin karshen a private school suke can suna karatu. Ita kuma aka bata direba daya da zai rika kaita makaranta yana daukota ita kadai, ba karama ta kaddama aka yi ba kamin Appa ya saka ta government school, domin malaman dake karantar da ita a private school suna sonta sosai saboda kokarin da take da shi, ga kuma gasar da suke ta shirye shiryen turata. Har komiti suka hada na manyan makarantar suka zo har gida suka tarardar Appa suka tattauna da shi tare da nuna masa illar cire Hurriya a makarantar amman ya ki saurarensu saboda Hajiya Kaltume ta ba shi shawarar kaita makarantar Government, daga karshe ma sai suka rabu cikin rashin dadin rai domin Appa rufe su yayi da fada ya nuna musu Hurriya yarsa ce shi ke da iko da ita babu wanda ya isa ya fada masa me zai yi akan yarsa hukuncin da ya yanke ke nan kuma babu fashi.
Ta bangaren Hurriya ma hakan ya taba ta sosai domin yin sabin abokai da kuma canja wasu abubuwa na karantu domin malaman ba daya ba be ya zama abu ne marar sauki a gareta, hakan sai ya saka ta zama weak ta yadda bata iya maida hankali ta yi karatun yadda ya dace, gaba daya ta koma kamar ba ita ba, karatun da take ganewa a can bata ganewa yanzu, sai ayi darasi a gama bata fahimci komai ba, tunani da damuwa suka taru suka yi mata yawa, gashi kullum ita ce cikin kebe kanta bata son shiga cikin yan makarantar da bata saba da su ba.
**** **** ****
Hindu ta mika mata jaririn dake kuka.
“Iyami ina ta fada miki banza bata fitar da ke gidan Alhaji, amman kika sa kafa kika yi biris da maganata, yanzu gashin bayan fitar da ke ta dauke hankalinsa daga kan Yayansa, bayan an a kashe miki daya, kuma han karbe dan abun da yake hannunki, ina dadi ka haihu gari daya da miji amma yaki ya tako ya duba yara, ke da da ns yadda Alhaji yake sonki ai kin Allah kadai ya san yadda zai rika dauki yana hauka kin haifa masa yaya biyu kuma maza”
Amma ta Hamid dinta dake shan nono ta ce.
“Hindu ban saba irin abubuwa nan ba, ni Wallahi ban san kowa mai irin wannan aikin ba, kuma ni ina tsoron kauce hanya”
“Babu zancen kauce hanya, ai ba shirka zamu yi ba, kuma ba cewa zamu yi ayi mana na Sherri ba, aa mu dai kawai a karya sihirin da ta yi miki da na yayanki hankalin mijinki ya dawo ki koma gidansa ki rike yayanki, domin nan gaba kadan ma zai iya cewa su ma wadannan karbe su zai yi, tun kina cikin idda na so a nemi taimakon nan kika ki gashi yanzu har sai an sake daura aure”
“Hindu da dai mun hakura, komai fa yana da iyaka wata rana zai karye ko da ba ayi komai ba indai asiri ne.”
“Toh shi ke nan zauna a gurin, kina sakawa zuciyarki bakinciki ki lalace a banza ki zama bar tausayi daman haka suke so, yar ki kuma ta koma yar aikin gidan, idan ma ta yi sa'a kenan ita ma ba su kashe ta ba, nan gaba kadan idan ta girma ki rasa wa zai aureta, domin Wallahi ba zata yarda Hurriya ta yi aure ba ga nata yayan ko da kuwa sun yi aure, yanzu kina kallon yadda aka cireta ko ran mahaifinta, makaranta ma sai ya sakata a jnda karatunta zai lalace ba dan kuma ba shi da hali ba, sai dan an shiga tsakani”
Amma ta kalleta tana nazarin kalamanta ita kanta a yanzu ta yarda ba a banza Appa ya canjawa Hurriya makaranta ba, yarinyar da yake alfahari da basirarta har yana ikirarin fitar da ita waje ta yi karatu amman a yanzu ya cireta daga makarantar kudi ya maida ita makarantar government.
Huriyya ta dauke kai da sauri ta fara tafiya, sai kuma Momy ta kirata.
“Hurriya”
Ta juyo a hankali ta kalleta ta kasa amsawa har lokacin hawaye take.
“Zo ki zauna yi hakuri kinji”
Hurriya ta dawo ta zauna saman kujerar dake dama da Momy.
“Gaskiya dai Alhaji ya ci amanarki Wallahi, ni ai ko da bala'i sai na karbi yayana, ko da yake Iyami ba zata iya ja da Alhaji ba, ta ina talauci zai ja da arziki, amman dai gaskiya be dace ya rabaki da Iyami yanzu ba, ai sai tunanin ya hade miki ga na dan'uwa ki kamu da hawan jini da kurciyarki, kai Kaltume bata da imani, haka fa ta raba Sapna da ubanta, Sapna bata isa ta tako garin nan ta ce zata zo gurin ubanta ba, tana can kauye cikin talauci shi kuma ya kyaleta... Hmmmm”
Ta mike tsaye tana kwalawa mai aikinta kira.
“Bilki”
Tsohuwar ta fito da gudu daga kitchen, daman haka take da yan aiki idan tana falo sai dai su boya a wani guri bata zama daki daya da su, idan har ka gansu a falo to tana dakinta ne ko kuma ta fita.
“Hajiya ga ni”
“A dauke plate din nan kuma ga yar Iyami nan idan zata ci abinci a zuba mata”
“Toh Hajiya”
Tsohuwar ta dauke plate din sannan ta kalli Hurriya dake zaune.
“Hurriya a zuba miki abinci?”
Hurriya ta girgiza kai alamar aa, Momy tabe baki ta dauki wayarta.
“Dan kan masa in ji sure, cikinki ko na wani, kin san dai ba rarrashinki zan yi dan ki daina kuka ko ki ci abinci ba, ina da tausayi da zuciyar imani amman laisa son dan wani kamar nawa kam karya haram babu boye boye ba munafurci, shiyasa ni na fi sha'awar uwarku ta dawo ta rike yayanta”
Tana fadan tana hawa sama har ta haye ta shige dakinta, Mai aikinta kam tuni ta san inda dare yayi mata. Hurriya ta bi ta kallo har ta haye stairs din, ji ta yi kamar ace wani na nan ta fada jikinsa ya rumgume ta yi kuka ammab babu wannan damar, saukowa ta yi daga saman kujera ta zauna kasa sai ta dora kanta sama kujera ta takure guri daya. Ta rufe ido hawaye na sauko mata. After like 30min ta ji an zungureta sai ta farka da sauri gilashin idonta ya fadi da sauri ta dauka ta saka ta gyara mayafin abayarta ta kalli Musib dake tsaye kanta.
“Miye na yi ma mutane bachi a kujera kin wani takure salon wani ya shigo ace ke ce marar gata a gidan ke ga munafuka, wato kin dawo babu zaman lafiya, mun rabu da Hamad ke kuma zaki kirkiri mugun abu ko?”
Kamar wani mace haka yake fada da ita yana gautsina fuska, gently ta mike tsaye domin ita ma bata san bacci ya dauke ta sai da ya tasheta. Tafiya ta fara yi ta haye sama ta dade a tsaye tana kallon kofar dakin Hamad tana jin kamar idan ta tura zata ganshi kwance ya ba kofar baya kamar yadda ya saba kwanciya. Wani hawayen ya sake cika idonta wani abu mai kama da dutse ya tsaya mata a tsakiyar zuciya ya mata nauyi. Cikin karfin hali ta kai hannu ta tura kofar dakinta ta shiga sai da maida kofar ta rufe ta jingina jikin kofar ta rumgume hannayenta not knowing what to do ita dai ba kuka take ji ba a yanzu, hawaye ne kawai ke mata zuba, tunanin dake mabanbantan duniyoyi ya hade mata guri daya, idan ta tuna Hamad ta tuna Amma, ta tuna Appa. Jin ta yi an yi knocking kofar dakin wani abu mai kama da tsoro ya fisgeta ta tashi tsaye da sauri jikinta na rawa ta yi baya tana kallon kofar, Namra ce ta turo kofar ta shigo da far'arta.
“Hurriya kin dawo”
Kamin ta rufe baki Yasir ya shigo cikin yanayi na damuwa yana kallonta.
“Hurriya”
Ta kasa amsawa Namra balle Yasir da ya shigo bayanta, ta hade yawu da karfi tana kallonsu. Yasir ya nufi gadonta ya zauna ya rasa me zai ce mata shi kansa be jin dawowarta gidan a yanzu mafita ne a gareta, babu yadda be yi ba wajen ganin ya fahintar da Hajiya Kaltume akan ta hana Appa dauko ta amman ta kasa fahimtarshi.
“Hurriya zauna”
Ta zauna a gurin kamar wata wadda tunani ya birkicewa kwakwalwa. Namra dai ta tsaya jikin kofar ita ma tara ran duk babu dadin ganin yar'uwarta cikin damuwa.
“Hurriya ki yi hakuri dan Allah, idan kina kukan nan sai ki saka kanki a damuwa”
Yasir ya daga ma Namra hannu alamar ta daina maganar sai ta yi shuru ta juya ta fice daga dakin, dan zumudin da ta zo da shi na murnar dawowar Hurriya sai ya gushe.
“Hurriya kina son zama nan ko kin fi son zama gurin Amma? Idan gurin Amma kike so zan mu tafi tare da ni dake mu yi ma Appa magana, idan be amince ba sai mu fadawa Hajiya Binta”
Ta girgiza kai alamar bata aa.
“Kina son zama nan din?”
Ta daga masa kai.
“Shi ke nan zo ki kwanta, kin yi sallah ko?”
Ta amsa masa da kai sannan ta nufi gadon ta kwanta shi kuma ta tashi ya fice, kai tsaye bangaren mahaifinsa ya nufa sai dai yayi rashin sa'a be tararda shi ba, domin tuni ya fita after ya kai Hurriya bangaren Momy daman ita kawai yake jiran a dawo da ita gidan ya fita, saboda Hajiya Kaltume ta fada masa idan be yi da gaske ba Amma ba zata ba shi Hurriya ba.
Hurriya bata tabbatar da mahaifinta ya daina yayinta ba sai da ya canja mata makaranta ya saka ta makarantar government, yayinda sauran yan'uwanta da suke ajin karshen a private school suke can suna karatu. Ita kuma aka bata direba daya da zai rika kaita makaranta yana daukota ita kadai, ba karama ta kaddama aka yi ba kamin Appa ya saka ta government school, domin malaman dake karantar da ita a private school suna sonta sosai saboda kokarin da take da shi, ga kuma gasar da suke ta shirye shiryen turata. Har komiti suka hada na manyan makarantar suka zo har gida suka tarardar Appa suka tattauna da shi tare da nuna masa illar cire Hurriya a makarantar amman ya ki saurarensu saboda Hajiya Kaltume ta ba shi shawarar kaita makarantar Government, daga karshe ma sai suka rabu cikin rashin dadin rai domin Appa rufe su yayi da fada ya nuna musu Hurriya yarsa ce shi ke da iko da ita babu wanda ya isa ya fada masa me zai yi akan yarsa hukuncin da ya yanke ke nan kuma babu fashi.
Ta bangaren Hurriya ma hakan ya taba ta sosai domin yin sabin abokai da kuma canja wasu abubuwa na karantu domin malaman ba daya ba be ya zama abu ne marar sauki a gareta, hakan sai ya saka ta zama weak ta yadda bata iya maida hankali ta yi karatun yadda ya dace, gaba daya ta koma kamar ba ita ba, karatun da take ganewa a can bata ganewa yanzu, sai ayi darasi a gama bata fahimci komai ba, tunani da damuwa suka taru suka yi mata yawa, gashi kullum ita ce cikin kebe kanta bata son shiga cikin yan makarantar da bata saba da su ba.
**** **** ****
Hindu ta mika mata jaririn dake kuka.
“Iyami ina ta fada miki banza bata fitar da ke gidan Alhaji, amman kika sa kafa kika yi biris da maganata, yanzu gashin bayan fitar da ke ta dauke hankalinsa daga kan Yayansa, bayan an a kashe miki daya, kuma han karbe dan abun da yake hannunki, ina dadi ka haihu gari daya da miji amma yaki ya tako ya duba yara, ke da da ns yadda Alhaji yake sonki ai kin Allah kadai ya san yadda zai rika dauki yana hauka kin haifa masa yaya biyu kuma maza”
Amma ta Hamid dinta dake shan nono ta ce.
“Hindu ban saba irin abubuwa nan ba, ni Wallahi ban san kowa mai irin wannan aikin ba, kuma ni ina tsoron kauce hanya”
“Babu zancen kauce hanya, ai ba shirka zamu yi ba, kuma ba cewa zamu yi ayi mana na Sherri ba, aa mu dai kawai a karya sihirin da ta yi miki da na yayanki hankalin mijinki ya dawo ki koma gidansa ki rike yayanki, domin nan gaba kadan ma zai iya cewa su ma wadannan karbe su zai yi, tun kina cikin idda na so a nemi taimakon nan kika ki gashi yanzu har sai an sake daura aure”
“Hindu da dai mun hakura, komai fa yana da iyaka wata rana zai karye ko da ba ayi komai ba indai asiri ne.”
“Toh shi ke nan zauna a gurin, kina sakawa zuciyarki bakinciki ki lalace a banza ki zama bar tausayi daman haka suke so, yar ki kuma ta koma yar aikin gidan, idan ma ta yi sa'a kenan ita ma ba su kashe ta ba, nan gaba kadan idan ta girma ki rasa wa zai aureta, domin Wallahi ba zata yarda Hurriya ta yi aure ba ga nata yayan ko da kuwa sun yi aure, yanzu kina kallon yadda aka cireta ko ran mahaifinta, makaranta ma sai ya sakata a jnda karatunta zai lalace ba dan kuma ba shi da hali ba, sai dan an shiga tsakani”
Amma ta kalleta tana nazarin kalamanta ita kanta a yanzu ta yarda ba a banza Appa ya canjawa Hurriya makaranta ba, yarinyar da yake alfahari da basirarta har yana ikirarin fitar da ita waje ta yi karatu amman a yanzu ya cireta daga makarantar kudi ya maida ita makarantar government.