← Book details Huriyya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 29 OF 159

Sashe 29

Huriyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dayan ya fada sannan biyun da ba sa rike da makami suka iso gurin dayan ya rika Hurriya dayan kuma ya rika Ruma suka fara jansu zuwa motar. Hamad ya fashe da kuka sosai yayi saurin riko Hijabin Hurriya da ita ma kukan take, kamin ta kai bakinta ta gantsawa wanda ya rike mugun cizo a hannu, aiko ba shiri ya sake ta sai ta ranta ana kare, abun ka da marar jiki kamin dayan ya rikota ta yi nisa, sai yayi wuf ya cafke Hamad dake kokarin guduwa, suka dauke shi tare da Ruma sai motarsu. Suka shiga da sauri suka fisgi motar sannan Salma da Khairi suka fara ihu tare da Namra suna kuka, Hurriya kam tun da ta sa gaba bata dawo ba sai da direban ya wasu mutane da suka tsaya bayan bata garin sun gudu suka bi sawunta, sai suka same ta tsakanin wani gida da kwararo ta duke a gurin ta runtse idon ta saka hannayensa ta danne kunnuwanta.

“Hurriya”

Ta razana ta bude ido jikinta da zuciyarta na rawa, gilashinta ya fadi gurin gudun da dake, shiga kwararon ma da ganinta dishe-dishe ta shiga lalabe ya taimka mata, shi ne silar tsayarwa a gurin ma, domin da tana ganin hanya da kyau ba zata kusa ba guduwa zata yi. Jin muryar direbansu ne ya saka ta fashe da kuka, tana lalabensa shi ya rikota yana matsar kwalla suka fito gurin. Kin yarda ta yi su koma gurin saboda tsoro sai da direban ya janyo motar ya kawo gurin sannan ta yarda zata shiga.

“Ina Hamad?”

Ta tambaya yana taimaka mata ta hau bus din har lokacin kowa kuka yake, ita kuwa bata ji kukan dan'uwanta ba kuma bata ji muryarsa ba.

“Sun tafi da shi”

A take ta saki hannun direban ta yi shiruuuuu kamin ta fara haki.

“Wayyo Allah na Hamad”

Ta dora hannu akai ta fadi a gurin ta fashe da kuka mai karfi.

______________________

Masu karatu shin suwaye wadannan mutanen da suka dauki Hamad?
Me suke so? Za su dawo da shi ko kuma yaya?
Anya Hajiya Kaltume da Hajiya Fatee za su nasara akan kudurinsu?
Wai ni kam me Afrah ta yi ma Hajiya Fatee ne ta tsane ta har take neman raba aurenta da danta? Anya ana samun uwar mijin dake neman raba auren danta ta hanyar asiri?
Anya asirin da Hajiya Kaltume ta saka aka yi ma Iyami akan karta sake aure zai yi kuwa? Amma zata dawo gidan mijinta Appa ko kuma wani auren zata yi ko kuma dai ba zata auru ba kamar yadda Hajiya Kaltume take fata?
Waye wannan Captain din?
Waye Wannan Fadeel din?
Anya Momy zata daina halinta na kyamar Iyami da yayanta kuwa?
Akwai tsabtataciyar Soyayya a cikin littafin mai taba zuciya ta zauna a ruhi, ku dai kun san ba mu fara komai ba. Kuma da yardar Allah ba zan ba ku kunya ba. 😀

Duk amsoshin wannan tambayar tana nan ƙumshe a cikin littafi na biyu da zamu fara ranar Litanin mai zuwa In Sha Allah. Sai dai shi Book two din ba free ba ne na kudi akan 500 only.

If you want subscribe biya 500 to

2451879008
Zenith Bank
Hadiza Abubakar

Sai ku turo shaidar biyan ta wannan number 08036126660

Ƴan Nijar kuma za su turo katin Zain ko Orange na 500 ta wannan number 08036126660.

Za ku iya bibiyar Litfafin nan a Arewabooks ga wadanda basa ra'ayin karantawa a Whatsapp. A username dina @khadeejacandy ko kuma ku yi searching book din Hurriya.

Sai mun hada ku a Paid Group Real Masoya masu Patronizing dina a ko da yaushe.🥰
Ku huta lafiya, Allah ya bawa masu niyar siya kudin biya. 🤲
https://www.arewabooks.com/chapter?id=653656a358cd413f0dc70b74

Kamin direban ya isa gida duk wanda ke cikin motar ya dauka Hurriya shudewa zata yi, saboda kukan da take yana yin sama da nufashinta kamar nunfashin zai fice daga jikinta gaba daya. Namra ce take rike da ita tana kuka tana bata hakuri.

“Yi Hakuri Hurriya In Sha Allah zai dawo lafiya Allah zai tsare su”

Hurriya bata iya furta komai, gashin idon nata ya rufe gaba daya saboda kukan hawayen ya hanata ganin dishe-dishe ma da take gani idan babu gilashi a idonta. Direban na fakawa Salma da Khairi suka fita suna kuka suka nufi bangaren Hajiya Kaltume suna kuka, Namra kuma ta tsaya ta riko Hurriya suka fito.

“Bana ganin komai Yaya Namra idon ya rufe gaba daya... Karki bar ni nan dan Allah tsoro nake ji... Kira min Yaya Yasir ko ki kaini gurin Amma ko ki kira min Appa na dan Allah”

Tana maganar muryarta na rawa saboda numfashim da ya sarke ta. Ta san a gurin dayan su ne kadai zata yi kukanta ta more kuma ta fada musu abun da ya faruwa. Kowane ďa ko ƴa idan abun farinciki ko kishiyarsa ya same shi guduwa yake gurin uwarsa, sai dai ita a yau bata da wannan gatan, ba dan mahaifiyarta bata raye ba sai dan bata tare da ubanta, bata taba sanin zafin rashin Amma a gidan ba sai yau, ko wane ďa yana bukatar uwa a kusa da shi balle kuma ita da take da lalaurar ido. Dukawa ta yi a gurin ta dora duka hannayenta biyu a kai ta kwalla ihu da kukam muryarta tana kuka har sai da duk wanda ke harabar gidan hankalinsa ya dawo kanta.

“Wayyo Amma ma, Amma..... Amma... Amma... Ke..... Amma na”

Namra ta yi saurin rika hannunta tana kuka.

“Hurriya ba gani nan ba, ta zo muje ciki Momy tana nan ai”

Ta fisge hannunta, sanin kanta ne daga Momy har Hajiya Kaltume babu wanda ta isa ta jingina a cikinsa ta yi kuka, domin ba su dauke ta kamar sauran ƴaƴansu ba.

“Kira min Yayana kira Yayana”

Domin karanta labarin ziyarci shafin dake sama na arewabooks @Khadeejacandy ko kuma ku yi searching din Hurriya.

𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660

𝐏𝐚𝐠𝐞 1️⃣

Kamin direban ya isa gida duk wanda ke cikin motar ya dauka Hurriya shudewa zata yi, saboda kukan da take yana yin sama da nufashinta kamar nunfashin zai fice daga jikinta gaba daya. Namra ce take rike da ita tana kuka tana bata hakuri.

“Yi Hakuri Hurriya In Sha Allah zai dawo lafiya Allah zai tsare su”

Hurriya bata iya furta komai, gashin idon nata ya rufe gaba daya saboda kukan hawayen ya hanata ganin dishe-dishe ma da take gani idan babu gilashi a idonta. Direban na fakawa Salma da Khairi suka fita suna kuka suka nufi bangaren Hajiya Kaltume suna kuka, Namra kuma ta tsaya ta riko Hurriya suka fito.

“Bana ganin komai Yaya Namra idon ya rufe gaba daya... Karki bar ni nan dan Allah tsoro nake ji... Kira min Yaya Yasir ko ki kaini gurin Amma ko ki kira min Appa na dan Allah”

Tana maganar muryarta na rawa saboda numfashim da ya sarke ta. Ta san a gurin dayan su ne kadai zata yi kukanta ta more kuma ta fada musu abun da ya faruwa. Kowane ďa ko ƴa idan abun farinciki ko kishiyarsa ya same shi guduwa yake gurin uwarsa, sai dai ita a yau bata da wannan gatan, ba dan mahaifiyarta bata raye ba sai dan bata tare da ubanta, bata taba sanin zafin rashin Amma a gidan ba sai yau, ko wane ďa yana bukatar uwa a kusa da shi balle kuma ita da take da lalaurar ido. Dukawa ta yi a gurin ta dora duka hannayenta biyu a kai ta kwalla ihu da kukam muryarta tana kuka har sai da duk wanda ke harabar gidan hankalinsa ya dawo kanta.

“Wayyo Amma ma, Amma..... Amma... Amma... Ke..... Amma na”

Namra ta yi saurin rika hannunta tana kuka.

“Hurriya ba gani nan ba, ta zo muje ciki Momy tana nan ai”

Ta fisge hannunta, sanin kanta ne daga Momy har Hajiya Kaltume babu wanda ta isa ta jingina a cikinsa ta yi kuka, domin ba su dauke ta kamar sauran ƴaƴansu ba.

“Kira min Yayana kira Yayana”

Namra na cira kafa da zimmar tafiya kiran Yasir sai ta hangoshi ya fito da saurinsa ya nufo inda yake.

“Hurriya”

Hurriya na jin muryarsa ta mike tsaye da sauri ta fara lalaben inda zata ganshi.

“Yayana Yayana Yayana”

Kusan duk wanda ke tsaye yana kallonta sai da ya tausaya mata, domin lalurar rashin gani babbar matsala ce. (Alhamdulillah da kyautar Allah, if you can read this ku gode Allah, ba zabinku ba ne, kyautar Allah ce, and don't forget littafin na kudi ne idan kika karanta baki biya ba, ko kika min sharing na barki da Allah)

Yasir na isowa ya rika hannunta dake ta rawa take da fatar bakinta.

“Yayana dan Allah ka kai ni gurin Amma... Dan Allah..”

Without second thought yaja hannunta ya karbi key hannun dayan direban da ya aje Hajiya Kaltume few minutes before the incident happen. Ya bude motar Namra bata kara jin tausayinta ba sai da ta ga yadda take lalaben motar zata shiga, Yaisr ya taimaka mata ya saka ta a back seat sannan ya zagaya ya shiga mazaunin direba ya murza key ya juya motar cikin tashin hankali, ba dan yana namiji ba da tuni shi ma ya fashe da kukan kamar yadda kanensa da mahaifiyarsa suke kukan. Shiru Hurriya ta yi a cikin motar domin bata ganin komai sai duhu zucuyarta kuma ta cika fa tsoron abun da ya faru. A harabar gate din gidan Yasir ya faka motar sannan ya budr ya fito da Hurriya. Sai da ya daga gate din gidan sai kuma ya ji ba zai iya shiga ciki ba domin ba zai iya zama mutum ya farko da ya labartawa Amma labarin an sace danta ba, ya san idan ya shiga gidan ta ga yarta a wannan halin sai ta tambaye shi shi kuma ba zai iya mata karya ba. Haka kuma ba zai iya barin Hurriya ta shiga cikin gidan ita kadai ba a wannan yanayin.

“Hurriya ko dai ki hakura mu koma? Ba zan iya shiga cikin gidan nan ba, bana son na daga hankalin Amma a yanzu”
Chapter 29 · 0% Book details