← Book details Huriyya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 45 OF 159

Sashe 45

Huriyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Wato Hajiya Fatee magana nan ba ta waya ba ce, bari dai sai na zo kawai ko kuma idan kin shigo”

“Toh shikenan Hajiya sai mun hadu”

Ta sauke wayar tana murmushin jindadi, domin an yi tsara akan gaba Khairy ta kamalla karatu daman kuma can tana sha'awar hada jini da aminiyarta ko dan karfafa zumuncinsu.

**** **** ****

Hajiya Fatee ma da murmushi ta sauke wayar, sannan ta fito falo ta zauna tana ta sake saken yadda zata kara bullowa lamarin. Domin ta san ba karamar wahala zata sha ba kamin ta samu kan danta Fadeel ya yarda zai aure, a ganinta mallakar da Afrah ta yi masa ba karama ba ce ta yadda ta hana idonaa ganin ko wace mace sai ita kadai.

“Sallamu Alaikum”

Ta dago tana amsa masa.

“Wa'alaikassalam har ka dawo?”

“Eh ko da na je Already ta wuce ma”

Ta yi tusar baki tana jin rashin dadin bw tarardar Khairy ba.

“Aikin banza, zuwan kawai ka yi kenan”

Ya yi dariya yana saka keys din hannunsa ya taba kunnensa.

“No na sauke kanwarta yar farar nan ita ce bata samu mota ba, sai na kaita”

“Oh yar makauniya? Ko yar wajen Hajiya Nafisa?”

“Tana gani Hajiya fa”

“Amman sai da gilashi ai, ita da makafi duk daya, Allah yasa dai ka shiga ciki”

Ya yi fuskar mamaki.

“No why would i?”

“To wish her happy birthday mana, kuma Allah yasa dai baka je mata hannu sake ba”

Ya zauna yana dariya.

“Hajiya Khairi kanwata ce fa, kuma ban ma san tana birthday ba, sai da kika kira ni kika fada min naje na daukota, ban shirya komai ba”

“Toh sai ka shirya wani abun ka kai nata daga baya, ko tana kanwarka ai tana sin kyautatawa”

“Yanzu kuma ai ya wuce, sai da mu hari gaba kuma”

Ya mike tsaye yana cigaba da wasa da keys din hannunsa.

“Bari na tafi na bar aiki a office”

“Wane irin aiki yanzu da yamma, wai shike nan ba dama na zauna na yi hira da kai sai ka ji kamar kama kan kaya, yar hirar ma sai a hana ka?”

“Waye zai hana ni hira dake duk duniyar nan Hajiya?”

Ta tabe baki ta dauke kai.

“Dan Allah karki ce Afrah bata ma san na zo nan ba, ki daina dora mata laifi kina daukar alhakinta ne kawai”

“Kullum ai ni mai daukar alhakinta ce, daman ta ina Afrah zata yi laifi a gurinka? Yar zinari, ina dai son ka sani ni uwarka ce ko kana so ko baka so, matarka bata fi ni matsayi ba”

“Ai ba za a ma hada ba, babu mai matsayin uwa a duk duniyar nan Hajiya, amman duk da haka tana da nata iyaka mata ma tana da muhallinta, ban san miyasa kika tsani mutanen Afrah ba, yarinyar nan tana mutuntatako daidai gwargwado tana miki biyayya”

“Na ji dan Allah kama hanya ka tafi Allah ya bada sa'ar aiki”

Rokonsa take har da hade hannaye. Ya sauke ajiyar zuciya cikin yanayi na damuwa ya koma ya zauna domin ba zai iya barin gidan ran mahaifiyarsa a bace ba.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
“Ka tashi ka yi tafiyarka bana bukatar zaman ka daman ai bana da muhimmanci a gurinka, da ina da muhimmanci ba zaka wulakanta ni ba”

Maganarta ta sake sukarsa gaba daya sai mood dinsa ya sake sauyawa. Sometime baya ganewa rikicin Hajiya Fatee gashi bata yi tsufan da zai ce ya kai ace bata gane wasu abubuwan amman sau ta rika furta kalama anyhow.

“Hajiya yanzu laifina na rashin bawa Khairi kyauta ne? Zan je na siye na kai mata shi ke nan”

Ta yi kamar bata ji ba har ya mike tsaye ya fara tafiya sai kuma ya juyo yana kallonta domin a lokacin ne wani tunani ya zo masa.

“Hajiya me yasa kika damu da zancen siyawa Khairi gift?”

Ya tambaya with little confused domin shi be ma tana jin ta yi maganar birthday Khairi ba sai yau kuma ta nuna damuwarta akai sosai.

“Dalili ba na birthday ne ba kawai, ina ta karkata ha hankalinka ka gagara fahimta, saboda hankalin gaba daya yana can gurin matarka”

Ya koma ya zauna yana cigaba da kallonta irin kallon nan dake nuna karin bayani yake nema.

“To me nene dalilin Hajiya?”

Ta juyo ta fuskance shi.

“Magana muka yi da Hajiya Kaltume ganin Khairi ta gama makaranta yanzu, kuma ba wani tsayaye take da shi ba zamu hadaku domin aminci na da Hajiya Kaltume ya kamata ace akwai auratayya a tsakaninmu ya kamata ace tarayyar ta wuce abokanta”

Wani kalar faduwar gaba ne ya same shi, jin yadda Hajiya Fatee ta gabato masa da maganar aure kai tsaye abun da be yi tsammani ba, domin ba shi da ra'ayin aure mace fiye da daya.

“Amma....Hajiya....”

Kamin ya furta ta tari numfashinsa.

“Aha... Ai sai ni ita da yake tana da yar albarka tana mata magana ta amince ita da take mace balle kuma ni da nake da ďan namiji, amman gashi nan zaka fara musamin gashi nan tun ba aje ko'ina ba zaka fara cewa ba haka ba”

Ya saka hannu daya ya shafa kansa gaba daya sai ta ruda masa tunani ya rasa ta ina ma zai bullowa lamarin.

“Ai na sani yanzu zaka fara lissafa min cewar baka da ra'ayin aure mace fiye da daya ko?”

Ya dago ya kalleta yana shafa fuskarsa sai dai be ce mata komai ba ya mike tsaye.

“Hajiya zan tafi gida”

“Toh a gaishe da sarauniya daman ai karshe na san haka za a rabu”

Ya sake kallonta cikin yanayi na damuwa sannan ya fice daga falon. Kamar marar lafiya haka ya isa gurin motarsa ya bude ya shiga, yayi zaman minti goma a ciki sannan ya murza key ya juya motar ya fice daga gidan. Kamar baya son driving haka yake tuka motar a madadin ya karasa gurin aiki sai ya koma gida, domin gaba daya jin yake jikinsa ma babu dadi. Tun daga kofar falon ya jiyo sautin muryar Afrah tana rera karatun qur'ane, a fakin ta zauna kan cushion ya dafa kansa gaba daya Hajiya Fatee ta gama ruda masa tunani, shi ko aure zai kara Khairi bata cikin irin matan da yake so, balle ma ba shi da burin na auren mace fiye da daya. Matarsa tana da duk wasu qualities da yake so a jikin mace, kuma suna zamansu lafiya tana masa biyayya daidai gwargwado gata da addini, why Hajiya zata rikita masa lissafi yanzu da wani zancen aure, sanannen abu ne Hajiya bata son matarsa kuma babu wani abu da zai iya yi akan haka sai hakuri.

“Rabin raina?”

Ya dago ya kalleta murmushin da yayi arba da shi a fuskarta ya saka shi jin sanyi, daman a duk lokacin da zuciya ta yi arba da wanda take so, idan ta kalleshi farinciki take ji. Kusa da shi ta zauna ta kai hannu ta shafa kansa zuwa bayansa.

“Yau kuma ta ina aka taba angona? Gurin aikin ne ko friends ko kuma a hanya”

“Ba ko daya kawai dai bana jindadi ne”

A take hankalinta ya tashi ta saka hannunta cikin rigarsa tana taba jikinsa.

“Me ya same ka? Fever ko headache?”

“Ba rashin lafiya ta jiki ba, rai na ne babu dadi”

Ta mike tsaye ta cire hijabin dake jikinta ta aje ta nufi kitchen sai ya bi kyakkyawar surarta da kallo, skirt din da ta saka irin wannan ne mai bin jiki gashi Allah ya hore mata baya. Tashi yayi ya bi bayanta tana kokarin dauko ruwa a fridge ta ji ya shafa gurin da ya fi ko'ina daukar hankalinsa.

“Wannan kwalliya haka ai sai ki mantar da ni damuwata ma, ni yanzu kin kwashe min tunani gaba daya kin bar kwakwalwar fanko”

Ta saka dariya tare da rufe fridge din.

“Kai da ba wani nan wayo ne dan kar na tambaye damuwar kuma sai na tambaya”

Ya juyo da ita ya rika bayanta yana kankance idonsa.

“To ai na manta, kin taba ganin an bada abun da babu?”

Da sauri ta ja baya shi kuma ya cire hannunsa a jikinsa sakamakon jin motsin yaransu da suka yi, ta nufi gurin cups shi kuma ya juya ya tarbeshi yana murmushi.

“Daddy...”

Ya daga ta farin din sannan ya daga mai binta ya aje ya sake daga na ukun da yake namiji ya aje.

“Daddy sannu da zuwa”

“Yauwa ashe kuna cikin gidan ko? Da na shigo ban ji motsin yarana ba”

“Daddy baka duba dakin mu ba da zaka gan mu ai, Aiman ne ya leka windows ya ce Daddy sai muka gano ka dawo”

Babbar data fi su wayo ta fada, ya rage tsawo ya shafa kansu yana murmushi.

“Na manta ai ban duba dakin ba, laifin Momy ne ita ce ta dauke min hankali”
Chapter 45 · 0% Book details