Sashe 24
Huriyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta buga kafa daya a kasa tana kukan da babu hawaye, Yasir kuma ya saka dariya.
“Appa dan Allah dai Appa”
Ba kasai Hurriya take zuwa masa da bukata ba, kusan duk wata bukata da take gabatar masa da ita kidayayyyiya ce, hakan ya sak idan ta zo masa sai ya biya mata ko dan tausayinta da yake na lalurar dake tare da ita, balle kuma yanzu da tausayinta ya ninku a zuciyarsa saboda rashin Amma a gidan, sai yake ganin yaransa kamar wasu marayu da uwarsu ta mutu ta bar su.
“Na ji amman daga wannan ba za'a sake ba?”
Ta amsa da sauri tana tsalle.
“Na yarda Appa na yarda Allah ya saka da alheri, Appa Allah ya biya maka bukatunka na alheri ya rabaka da Hajiya Lafiya ya kara buda maka a kasuwanci ya kyautata karshenka”
Ta masa kwatankwacin addu'ar da Amma take masa idan yayi mata wani abun kyautata da ta ji dadi. Appa ya shafa kansa yana jin zuciyarsa da tausayin da be san na minene ba. Yasir ma murmushi yayi yana taya ta murna yadda Appansy ya amince da wuri.
“Bari mu fara neman Gift din da zamu bawa mai birthday”
“Har da kyauta ake badawa?”
Appa ya tambaya sai Yasir ya amsa masa.
“Eh Appa idan mutum yayi birthday ana ba shi kyau sosai ma, kowa da kalar abun da yake ba shi”
“Oh toh saboda ki ci kudinmu kike son yi birthday kenan?”
Cewar Appa yana kallonta da zolaya, sai ta saka dariya kamar ba ita ta rufe idonta.
“Appa ba da kai ba an yafe maka”
Shi ma dariyar yayi, ya bita da kallo domin tuni ta nufi bangaren Momy domin labartawa Hamad cewar Appa ya yarda zai mata birthday kamin ya isa gurin hawaye ya cika idonta domin ta saba idan aka mata albishir Amma take fara fadawa sai dai a yau babu Amma a gidan kuma ta san babu wanda zai taya ta farinciki da murna sai dan'uwanta. Tana ahiga falon sai ta ja ta tsaya tana kallon Musib da ya hada hannayen Hamad ya rike yana zabga masa mari.
“Ba zaka yi magana ba? Waye yaje ma fadawa Appa karya da gaskiya ya zo ya rufata ta fada? Tsakanin kai da Hurriya”
“Ni ce”
Ta amsa kai tsaye domin ba zata jure ganin ana duka dan'uwanta ba da yaki yayi magana kuma ya ki yayi kuka sai dai idanuwansa sun kada sun yi ja sosai sai wani cika yake yana batsewa alamar zuciyarsa ta gama kawowa.
“Okay zo nan bakar mufuka wato daga dawowarku za ku fara hada Momy fada da Appa ko?”
Bata zo ba kamar yadda ya bukata sai dai kuma bata matsa daga inda take tsaye ba ssi hawayen da ta shigo da su suka fara sauko mata, Hamad ya juya ya kalleta har lokacin be ce komai ba, daman tun shigowarsa falon Musib ya rike shi wai sai ya fada masa waya fadawa Appa gulma har ya shigo yana mata fada ta yi kukan, Hamad ta kafiya ya ki magana hakan ya saka Musib dukansa. Musib ya saki hannun Hamad ya nufi gurin da Hurtiya take tsaye ya fara kai mata duka sai ta boye fuskarta ta fara kuka, yadda Hamad ya nufo gurin da suke tsaye sai ka dauka zai yi dambe yayansa Musib ne, ficewa yayi daga falon Musib na kokarin rikoshi ya fisge ya fice da gudu, be zame ko'ina ba sai gurin da Garden din gidan yake ya samo manya manyan duwatsu ya dauko har uku ya fito da su ya nufi gurin da Motar Momy take ta fara jefan gilashin a take ya fasa mata gilashin mota ya koma dayan bangaren ya sake jefawa. Kamin yayi na uku Appa da Yasir da suke tsaye a gurin da Hurriya ta bar su, suka iso gurin da sauri domin sun lura da lokacin da ya dauko duwatsu sun san ba za'ayi mai kyau ba, Yasir yayi saurin rike Hamad.
“Kai miye haka?”
Sai a lokacin Hamad ya fashe da kuka yana maida magana.
“Ya Musib ya yi min mari hudu, kuma gashi can yana dukan Hurriya, wai ya ce mun yi munafurci mun hada Momt da Appa fada”
Appa da ransa ya bace saboda abun da Hamad aikata, a take abun da ya fada ya gusar da bacin ran abun da Hamad yayi. Ya nufi falon fuska a hade Yasir dake rike da Hamad har lokacin yana ta zillo sai ya sake kwaso wasu duwatsun ya fasa motar ya bi bayan Appa. Da karfi Appa ya tura kofar falon ya shiga sai ya samu Hurriya duke kusa da kofar ta rufe fuskarta tana kuka marar sauti.
“Musib...!”
Appa ya aika masa da wani irin kira da karfin murya mai razanarwa. Musib dake boye kitchen ya fito baki kofar kitchen din yana amsa kiran muryarsa na rawa.
“Na'am...”
Appa ya taka ya karasa har inda yake ya dauke shi da mari. Daidai lokacin da Momy ta sauko tare da Namra.
“Akwai wanda na taba duka cikinku? Akan wani dalili zaka dokesu? Kai da ya kamata ka ga wasu musguna musu ku shigar musu kai zaka saka hannu da kanka ka dokesu? Karka sake! Ina gargadinka ba su ba Hurriya da Hamad kadai ba duka yayana kar ka sake saka hannu ka dake su”
Appa ya juyo ya kalli Momy dake tsaye kamar hoto tsabar mamaki ya ce.
“Na rantse da Allah idan wani ya sake dokar min ƴaƴa sai na masa abun da zai yi bakinciki da na kasance ubansa, ban doka ba ba zan yarda wani ya dokar min ba”
“Saboda ƴaƴan Iyami ne?”
Momy ta tambaya tana jin wani tuƙuƙi a zuciyarta, shi kuma ya amsa mata ba dan suna ƴaƴan Iyami kaɗai ɓa sai dai baya daukar a zalinci kowa, amman saboda ta ji haushi sai ya amsa mata da haka.
“Eh saboda suna Ƴaƴan Iyami...”
Yana fadar hakan ya juya ya fice daga falon, a nan ma Yasir da har lokacin yana rike da Hamad dake ta jan numfashi da karfi saboda zuciya, ya rufa masa baya tare da Hamad din, Hurriya kuma da ta tuni kuka yayi mata bankwana ya tafi ya barta tsaye tana kallon dramar da ake ta bi Appa da kallo kamin ta juyo ta kalli Momy.
“Ba hakka, haka ne... Daman ance maza ke bude wata kofar wani lokacin yau na gani, kuma ya bude muku kofa, za ku wahala a gidan nan. Musib yi hakuri”
Ta juya ta fara hawan stairs din daman bata sauko gaba daya. Musib ya watsawa Hurriya wani mugun kallo ya dauke ido ya bi bayan mahaifiyarsa. Zaunawa Hurriya ta yi a gurin ta rafka uban tagumi, gaba daya kwakwalwarta ta rike ce ji take kamar ba zata iya dauka ba.
*** *** ***
BAYAN WATA UKU....
Tun daga lokacin sai Hurriya da Hamad suka samu salama, ta duka Hamad kuma ya samu ta magana, ba a dukansa ba a fada masa magana marar dadi, saboda ana tsoron ya fadawa Appa, Musib da Miwan ma sai duk suka shafa musu lafiya, sai dai tsanar da Hajiya Kaltume take mata sai ya karu, har ta kai a gaban Hurriya Hajiya Kaltume take zagin Iyami sai dai ba zata yi a gaban Hamad ba, Hurriya tana jin zafin abun sosai sai dai bata taba fadawa kowa ba sai dai ta bar abun a zuciyarta. Hurriya na tsaye ita da Hamad suna wanke motar Yasir Hajiya Kaltume ta fito rike da jakarta Yasir din yana bayanta rike da makullin mota.
“A gaishe da ku, amman idan Appa ya gani karku ce ni na saka ku ku ce ku kuka saka kanku dan kar ya fara fada ya ce ban kai wankin mota ba na saka ku yi”
“Hamad ya fada masa zamu wanke maka mota ai kamin mu fara, ya ce mu je mu yi Allah ya mana albarka”
Hurriya ta amsa tana watsawa motar ruwa, domim wankin mota yana daga cikin abun da yake matukar burgeta, kuma ta taba yi sau daya a motar Appanta tun a lokacin da Amma take gidan. Hajiya Kaltume ta kallesu irin kallon nan na rasa ya zan yi da ku ta dauke kai ta nufi motar da za su shiga, tana nufar motar gabanta na kara tsananta faduwa har sai da taja ta tsaya.
“Yasir anya ba za mu fasa tafiyar nan ba? Gabana sai faduwa yake Wallahi tsoro nake ji ganin nake kamar wani abun zai sake faruwa”
Yasir ya ce.
“Babu abun da zai faru Hajiya dan Allah ki kwantar da hankalinki, ki yi imani da Allah, kuma kin ga tun da abun nan ya faru baki sake fita ba, yau kusan wata uku kenan dole ki ji haka”
Ta girgiza kai domin bata gamsu da kalaman Yasir ba.
“Ko dai mu hakura har wani lokacin?”
“Hajiya idan baki kawar da komai a ranki ba, babu ranar da zaki sake fita, rasuwa nawa aka yi baki je ba, ga haihuwa ba an yi ba daya ba amman baki fita ba, Hajiya Fatee ma tare abun nan ya same ku amman zuwanta biyar gidan nan, dan Allah ki daina tsoro babu abun da zai faru da yardar Allah”
“Toh Allah yasa”
Ta amsa tare da bude motar ta shiga ba dan ranta ya so ba, sai dan fitar ta zame mata dole ne saboda kiran da Hajiya Fatee ta yi mata tana kuka ba zata fita ba, balle kuma da ya kasance gidanta na farko da zata fara zuwa tun bayan da aka yi kidnapping dinsu, sai take ganin kamar hakan zai sake faruwa ne. A hankali Yasir ya rika jan motar suna tafiya yana dan taba mata hira, ita kuma ta kasa cewa komai sai kallon gari take har lokacin tsoro be fice ta ba, garin kuma tana ganin kamar ya sake saboda dadewa da ta yi bata fita ba.
“Bismillahi”
Ta furta yayin da ta bude motar zata fita, zuciyarta nata rawa, Yasir ya rakata har cikin falon Hajiya Fatee, yan aikin Hajiya Fatee suka fara gaisheta.
“Lafiya Kalau Ina Hajiya Fatee”
“Tana dakinta”
Hajiya Kaltume ta juya ta kalli Yasir.
“Bari na kirata ku gaisa”
“Okay”
“Appa dan Allah dai Appa”
Ba kasai Hurriya take zuwa masa da bukata ba, kusan duk wata bukata da take gabatar masa da ita kidayayyyiya ce, hakan ya sak idan ta zo masa sai ya biya mata ko dan tausayinta da yake na lalurar dake tare da ita, balle kuma yanzu da tausayinta ya ninku a zuciyarsa saboda rashin Amma a gidan, sai yake ganin yaransa kamar wasu marayu da uwarsu ta mutu ta bar su.
“Na ji amman daga wannan ba za'a sake ba?”
Ta amsa da sauri tana tsalle.
“Na yarda Appa na yarda Allah ya saka da alheri, Appa Allah ya biya maka bukatunka na alheri ya rabaka da Hajiya Lafiya ya kara buda maka a kasuwanci ya kyautata karshenka”
Ta masa kwatankwacin addu'ar da Amma take masa idan yayi mata wani abun kyautata da ta ji dadi. Appa ya shafa kansa yana jin zuciyarsa da tausayin da be san na minene ba. Yasir ma murmushi yayi yana taya ta murna yadda Appansy ya amince da wuri.
“Bari mu fara neman Gift din da zamu bawa mai birthday”
“Har da kyauta ake badawa?”
Appa ya tambaya sai Yasir ya amsa masa.
“Eh Appa idan mutum yayi birthday ana ba shi kyau sosai ma, kowa da kalar abun da yake ba shi”
“Oh toh saboda ki ci kudinmu kike son yi birthday kenan?”
Cewar Appa yana kallonta da zolaya, sai ta saka dariya kamar ba ita ta rufe idonta.
“Appa ba da kai ba an yafe maka”
Shi ma dariyar yayi, ya bita da kallo domin tuni ta nufi bangaren Momy domin labartawa Hamad cewar Appa ya yarda zai mata birthday kamin ya isa gurin hawaye ya cika idonta domin ta saba idan aka mata albishir Amma take fara fadawa sai dai a yau babu Amma a gidan kuma ta san babu wanda zai taya ta farinciki da murna sai dan'uwanta. Tana ahiga falon sai ta ja ta tsaya tana kallon Musib da ya hada hannayen Hamad ya rike yana zabga masa mari.
“Ba zaka yi magana ba? Waye yaje ma fadawa Appa karya da gaskiya ya zo ya rufata ta fada? Tsakanin kai da Hurriya”
“Ni ce”
Ta amsa kai tsaye domin ba zata jure ganin ana duka dan'uwanta ba da yaki yayi magana kuma ya ki yayi kuka sai dai idanuwansa sun kada sun yi ja sosai sai wani cika yake yana batsewa alamar zuciyarsa ta gama kawowa.
“Okay zo nan bakar mufuka wato daga dawowarku za ku fara hada Momy fada da Appa ko?”
Bata zo ba kamar yadda ya bukata sai dai kuma bata matsa daga inda take tsaye ba ssi hawayen da ta shigo da su suka fara sauko mata, Hamad ya juya ya kalleta har lokacin be ce komai ba, daman tun shigowarsa falon Musib ya rike shi wai sai ya fada masa waya fadawa Appa gulma har ya shigo yana mata fada ta yi kukan, Hamad ta kafiya ya ki magana hakan ya saka Musib dukansa. Musib ya saki hannun Hamad ya nufi gurin da Hurtiya take tsaye ya fara kai mata duka sai ta boye fuskarta ta fara kuka, yadda Hamad ya nufo gurin da suke tsaye sai ka dauka zai yi dambe yayansa Musib ne, ficewa yayi daga falon Musib na kokarin rikoshi ya fisge ya fice da gudu, be zame ko'ina ba sai gurin da Garden din gidan yake ya samo manya manyan duwatsu ya dauko har uku ya fito da su ya nufi gurin da Motar Momy take ta fara jefan gilashin a take ya fasa mata gilashin mota ya koma dayan bangaren ya sake jefawa. Kamin yayi na uku Appa da Yasir da suke tsaye a gurin da Hurriya ta bar su, suka iso gurin da sauri domin sun lura da lokacin da ya dauko duwatsu sun san ba za'ayi mai kyau ba, Yasir yayi saurin rike Hamad.
“Kai miye haka?”
Sai a lokacin Hamad ya fashe da kuka yana maida magana.
“Ya Musib ya yi min mari hudu, kuma gashi can yana dukan Hurriya, wai ya ce mun yi munafurci mun hada Momt da Appa fada”
Appa da ransa ya bace saboda abun da Hamad aikata, a take abun da ya fada ya gusar da bacin ran abun da Hamad yayi. Ya nufi falon fuska a hade Yasir dake rike da Hamad har lokacin yana ta zillo sai ya sake kwaso wasu duwatsun ya fasa motar ya bi bayan Appa. Da karfi Appa ya tura kofar falon ya shiga sai ya samu Hurriya duke kusa da kofar ta rufe fuskarta tana kuka marar sauti.
“Musib...!”
Appa ya aika masa da wani irin kira da karfin murya mai razanarwa. Musib dake boye kitchen ya fito baki kofar kitchen din yana amsa kiran muryarsa na rawa.
“Na'am...”
Appa ya taka ya karasa har inda yake ya dauke shi da mari. Daidai lokacin da Momy ta sauko tare da Namra.
“Akwai wanda na taba duka cikinku? Akan wani dalili zaka dokesu? Kai da ya kamata ka ga wasu musguna musu ku shigar musu kai zaka saka hannu da kanka ka dokesu? Karka sake! Ina gargadinka ba su ba Hurriya da Hamad kadai ba duka yayana kar ka sake saka hannu ka dake su”
Appa ya juyo ya kalli Momy dake tsaye kamar hoto tsabar mamaki ya ce.
“Na rantse da Allah idan wani ya sake dokar min ƴaƴa sai na masa abun da zai yi bakinciki da na kasance ubansa, ban doka ba ba zan yarda wani ya dokar min ba”
“Saboda ƴaƴan Iyami ne?”
Momy ta tambaya tana jin wani tuƙuƙi a zuciyarta, shi kuma ya amsa mata ba dan suna ƴaƴan Iyami kaɗai ɓa sai dai baya daukar a zalinci kowa, amman saboda ta ji haushi sai ya amsa mata da haka.
“Eh saboda suna Ƴaƴan Iyami...”
Yana fadar hakan ya juya ya fice daga falon, a nan ma Yasir da har lokacin yana rike da Hamad dake ta jan numfashi da karfi saboda zuciya, ya rufa masa baya tare da Hamad din, Hurriya kuma da ta tuni kuka yayi mata bankwana ya tafi ya barta tsaye tana kallon dramar da ake ta bi Appa da kallo kamin ta juyo ta kalli Momy.
“Ba hakka, haka ne... Daman ance maza ke bude wata kofar wani lokacin yau na gani, kuma ya bude muku kofa, za ku wahala a gidan nan. Musib yi hakuri”
Ta juya ta fara hawan stairs din daman bata sauko gaba daya. Musib ya watsawa Hurriya wani mugun kallo ya dauke ido ya bi bayan mahaifiyarsa. Zaunawa Hurriya ta yi a gurin ta rafka uban tagumi, gaba daya kwakwalwarta ta rike ce ji take kamar ba zata iya dauka ba.
*** *** ***
BAYAN WATA UKU....
Tun daga lokacin sai Hurriya da Hamad suka samu salama, ta duka Hamad kuma ya samu ta magana, ba a dukansa ba a fada masa magana marar dadi, saboda ana tsoron ya fadawa Appa, Musib da Miwan ma sai duk suka shafa musu lafiya, sai dai tsanar da Hajiya Kaltume take mata sai ya karu, har ta kai a gaban Hurriya Hajiya Kaltume take zagin Iyami sai dai ba zata yi a gaban Hamad ba, Hurriya tana jin zafin abun sosai sai dai bata taba fadawa kowa ba sai dai ta bar abun a zuciyarta. Hurriya na tsaye ita da Hamad suna wanke motar Yasir Hajiya Kaltume ta fito rike da jakarta Yasir din yana bayanta rike da makullin mota.
“A gaishe da ku, amman idan Appa ya gani karku ce ni na saka ku ku ce ku kuka saka kanku dan kar ya fara fada ya ce ban kai wankin mota ba na saka ku yi”
“Hamad ya fada masa zamu wanke maka mota ai kamin mu fara, ya ce mu je mu yi Allah ya mana albarka”
Hurriya ta amsa tana watsawa motar ruwa, domim wankin mota yana daga cikin abun da yake matukar burgeta, kuma ta taba yi sau daya a motar Appanta tun a lokacin da Amma take gidan. Hajiya Kaltume ta kallesu irin kallon nan na rasa ya zan yi da ku ta dauke kai ta nufi motar da za su shiga, tana nufar motar gabanta na kara tsananta faduwa har sai da taja ta tsaya.
“Yasir anya ba za mu fasa tafiyar nan ba? Gabana sai faduwa yake Wallahi tsoro nake ji ganin nake kamar wani abun zai sake faruwa”
Yasir ya ce.
“Babu abun da zai faru Hajiya dan Allah ki kwantar da hankalinki, ki yi imani da Allah, kuma kin ga tun da abun nan ya faru baki sake fita ba, yau kusan wata uku kenan dole ki ji haka”
Ta girgiza kai domin bata gamsu da kalaman Yasir ba.
“Ko dai mu hakura har wani lokacin?”
“Hajiya idan baki kawar da komai a ranki ba, babu ranar da zaki sake fita, rasuwa nawa aka yi baki je ba, ga haihuwa ba an yi ba daya ba amman baki fita ba, Hajiya Fatee ma tare abun nan ya same ku amman zuwanta biyar gidan nan, dan Allah ki daina tsoro babu abun da zai faru da yardar Allah”
“Toh Allah yasa”
Ta amsa tare da bude motar ta shiga ba dan ranta ya so ba, sai dan fitar ta zame mata dole ne saboda kiran da Hajiya Fatee ta yi mata tana kuka ba zata fita ba, balle kuma da ya kasance gidanta na farko da zata fara zuwa tun bayan da aka yi kidnapping dinsu, sai take ganin kamar hakan zai sake faruwa ne. A hankali Yasir ya rika jan motar suna tafiya yana dan taba mata hira, ita kuma ta kasa cewa komai sai kallon gari take har lokacin tsoro be fice ta ba, garin kuma tana ganin kamar ya sake saboda dadewa da ta yi bata fita ba.
“Bismillahi”
Ta furta yayin da ta bude motar zata fita, zuciyarta nata rawa, Yasir ya rakata har cikin falon Hajiya Fatee, yan aikin Hajiya Fatee suka fara gaisheta.
“Lafiya Kalau Ina Hajiya Fatee”
“Tana dakinta”
Hajiya Kaltume ta juya ta kalli Yasir.
“Bari na kirata ku gaisa”
“Okay”