← Book details Huriyya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 159

Sashe 18

Huriyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Ina fa, ai babu imani a tare da su, abinci sa mun ji yunwa suke ba mu, idan dare yayi muna nan cikin hudu sai idan sun haska mu, sun dauremu sai kace awaki, sannan a ciyayi muke bacci, baba kalar kwaron da be cize ni ba, shi kam sauro ya samu abun nema style style yake mana na cizo, kuma duk ranar da aka yi waya ba a samu daidaituwa ba sai sun mana duka, kuma a kafa muka yi tafiyar nan har ciki daji, yara kanana na haife su amman haka suke juya ni kamar waina, Allah dai ya isar min akan Iyami kawai zan ce, kuma kiyayya yanzu na fara, dacan ina boyewa  Wallahi yanzu a fili zan nuna bana sonta bana son yaranta, duk sai na ga bayansu”

“Hmmm Hajiya karki ga yadda Hurriya ta shigo falon nan tana ta zumudi ta ji dadi an kama ki har tambaya take”

Khairi ta shimfida mata fahimtarta akan Hurriya. Hajiya Kaltume ta cize baki.

“Shegya bakar dagga, daman idan bata yi murna ba ai bata cika yar kishiya ba, aiko sai ta gane shayi ruwa a gidan nan, ke shiga dakin yayanki ki kwaso min gilasan yarinyar nan gaba daya ki boye min su”

Kamar mai jiran umarni haka Khairi ta tashi da zafinta da murnarta ta nufi hanyar stairs. Maama ta tashi daga kasan da take zaune ta zauna kan kujera.

“Amman Hajiya Yaya Yasir zai iya gane dauka kika yi fa?”

“Ta ina zai gane fada masa zaki yi? Ko ma ya gane ai ba bayarwa zan yi ba, idan ya matsa min har shi ba zan ragawa ba, dan ni mai kaunar mai kaunar Iyami da yayanta ma bana kaunarsa, arzikinta daya ma dawo Wallahi da na mutu can da sai ta gane kurenta, kuma ita da Alhaji har abada”

Sosai ta hade fuska tana maganar irin hadewar da ya kara mata muni da bakin fata.

“Hajiya ai ba ita kadai ba, Hajiyar su Appa ma fa bata zo ba sai a waya ta kira, amman Wallahi da Amma ce da tun ranar zata iso gidan”

“Hmmm ita ai bata da wata power yanzu, ko ba komai a bakin rame take, kuma babu yadda zata yi da ni, bugu da kari kuma na kore matar da take so, sai na ga uban da zai dawo da ita a gidan nan”

Sun dade suna hirar Hajiya Binta da Maama kamin Khairi ta fito daga dakin Yasir da gilasan har uku ta nunawa Hajiya.

“Kin gansu Hajiya cikin closet dinsa ya saka su”

“Je ki yi musu mugun boyo idan ma bala'i yayi bala'i ki ce masa ni na dauka da kaina”

“Ba sai ance haka ba, kawai kowa yace be shiga dakin ba kuma babu wanda ya dauka”

“Shi ke nan, ya ma fi sauki”

Khairi ta fada a ganinta shawarar da yayarta Maama ta bada ta fi, sama da ta Hajiya Kaltume. Kamin Khairi ta isa stairs aka dauke wuta, a take hankali Hajiya Kaltume ya tashi domin har yanzu bata gama wartsakewa daga tashin hankali da azabar da ta sha a dajin ba.

“Innalillahi Maama kunna haske, na shiga uku... ”

Kamin Maama ta kunna fitilar wayarta Mekano dake aikin bada hasken wuta a gidan ya fara aikinsa, haske ya cika ko'ina. Hajiya Kaltume ta dafa zuciyarta tana sauke gajiya.

“Kai Allah raba musulmi da wahala, har yanzu ji nake kamar ina kusa da dajin nan, shiyasa ko waya bana son karba, mun ga tashin hankali mun ga shiga uku duk saboda bakar Iyami”

Hajiya ta karasa tana fashewa da kuka, domin Iyami ta hana ta zaman lafiya ta hana ta rawar gaban hantsi.

*** *** ***

Ta dayan bangaren Iyami tana ta fama da nata, tunanin da damuwa sun hana ta walawa ko da kuwa tsakar gidan ne, ga wani sabon lalurar laulayi da ya same ta bayan dawowarta gidan iyayenta, iyakar kokarinta tana yi na nunawa Gwaggo da Bappa ta karbi kaddara, sai dai a kasan zuciyarta tana fama da tunani domin kuwa tana son mijinta, domin tana zaune lafiya a gidan tana rumgume da yayanta ciwonsu lafiyarsu duk ta sani, ba kamar yanzu da tunanin halin da suke ciki yake hana ta sukuni ba. Gashi a duk lokacin da Hamad ya zo gidan sai ya fada mata abun da aka yi musu, Hurriya ce bata fada saboda bata son tashin hankali Amma kuma tana da zurfin ciki. Gwaggo ma tana iyakar kokarinta na kwantar mata da hankali ganin cikin dake jikinta gudun kar ta jawa kanta wata matsala. Addu'a kuma su dukansu suka dukufa da yinta ta neman Allah ya daidaita tsakaninta da Appa, sai dai ta bar kyau tun ranar haihuwa domin bata damu da yin azkar din neman tsari ba, tana ta tawaya a wannan babin, duk kuwa da ta san tana cikin kishiyoyi irinsu Hajiya Kaltume da Momy.

☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆

𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲

Hello Habibaties 😍🥰
Amin kara please ku yi following dina a Arewabook. @khadeejacandy

https://www.arewabooks.com/u/khadeejacandy

𝗣𝗮𝗴𝗲 1️⃣0️⃣

Washe garin ranar...

Hurriya na cire uniform dinta na makarantar boko ta dauki bakar abaya ta saka, ta bude gurin da take zuba hullunata tun bayan da ta kwaso kayanta daga bangaren Amma ta dawo da su bangaren Momy a dakin da aka bata, ta dauko farar hulla ta saka a kanta. Sannan ta fara gyara dakinta ta kintsa komai, cikin natsuwa ta fito daga dakin ta shiga dakin Hamad da ya watsar nasa uniform din akan gado ta dauka ta aje masa ta gyara masa dakin, daman shi be kula da gyara daki ba ko a lokacin da Amma na gidan balle kuma yanzu da tufafinsa ma sai da Hurriya ta kwaso ta dawo masa da su dakinsa dake bangaren Momy. After ta gyara nasa dakin ta sauka kasa domin dauko abun shara da mopper haka take kullum idan ta dawo take gyara nata dakin da na Hamad domin Momy ta hana masu aikinta share dakin Hamad da Hurriya haka ma ta hana ko cokali suka aje masu aiki su dauka, kamar ya yaran gidan ba haka Momy take treating dinsu, musamman ma Hurriya da bata iya budewa kowa cikinta, Hamad kuma idan ya ci abinci a nan yake bari sai dai Hurriya ta dauke masa, ba kowane rules and regulations na Momy ya sani ba, ko na ya sani ba amfanin da za su masa domin ba bi zai yi ba.

Gurin da ake aje kayan taje ta dauko ta hauro sama a hankali, domin Momy ta jaddada mata bata son jin karar tafiyar kowa a saman, hakan ya saka take kokarin ganin ta kiyaye dokokinta, ta san ba dan komai take nata haka ba sai dan ta takura mata idan kuma ta fadawa Appa wata kila zata iya jawa kanta matsala a gurin Momy. Dakin dan'uwanta ta fara gyarawa sannan ta shiga nata dakin ta fara sharewa. Cikin ɗoki Hamad ya shigo dakin nata.

“Hurriya za mu je dauko Hajiya yanzu”

Ta juyo ta kalleshi da sauri.

“Wace Hajiya”

“Hajiyar Appa tace zata zo, Appa ya kira ni yace na zo muje daukota yanzu nan”

Hurriya ta daka tsalle tana murna, daga ita har Hamad suna matukar son zuwa gurin Hajiya Binta kuma suna daukin ganinta a gidan ubansu, al'adace ta Alhaji Haruna, duk ranar da mahaifiyarsa zata zo gidansa da kansa yake zuwa ya daukota idan kuma ta tashi tafiya shi zai maidata gidanta, komai yake zai aje ya dauko ko ya kaita gida matukar gidansa zata zo, wannan ya saka tun ana sauran kwana biyu ta zo gidan take sanar masa, shi kuma ya sanar ma matansa a shirya mata tarba mai kyau. Murmushin da murnar da Hurriya ta gani a fuskar dan'uwanta Hamad ya ninka farinciki zuwan Hajiya Binta da take a gidan, domin tun tafiyar Amma bata san wata rana da Hamad ya sake fuska yana far'a kamar yau ba.

“Zan mata wanka mai kyau kin san ta iya tsokana ta tana cewa ban iya wanka mai kyau ba, tufafi zan canja yanzu nan”

Da karfi yake maganar, kamar yadda ya saba yi a bangaren Amma idan yana cikin farinciki. Hurriya ta yi saurin yi masa alama.

“Yi a hankali kar Momy ta ji ta fara maka masifa?”

“Saboda me?”

“Bata son hayaniya kuma tace idan zamu hauro ko sauka stairs mu yi a hankali kar mu yi making sound bata son ana hawa mata da karfi”

“Yaushe tace haka?”

“An dade, kai ai ba zama kake bangaren ba sai idan zaka kwanta shiyasa baka sani ba”

“Sai na fadawa Hajiya duk abun da ake mana a gidan nan”

Hurriya ta saki mopper dake hannunta ta nufo kofar dakin gun da Hamad yake tsaye.

“Hamad kar ka yi haka, kasan zata yi ma Appa fada shi kuma zai yi ma Momy, idan aka yi Momy kuma kan mu zai dawo”

“Sai na sake fada mata, Appa ma dan ina fushi ne da shi shiyasa ba zan fada masa ba, ni ba zan ma iya zama bangaren nan ba i hate them”

Ya saki kofar ya nufi tasa kofar ya bude, Hurriya ta dora hannu daya akai tana jin ina ma ace bata fada ba, tsoro take kar ace daga dawowarta bangaren ta fara hada munafurci, kuma ta san at the end abun gurinta zai dawo. Hamad na canja tufafi ya dauki turare ya saka ya canja shoes ya fito daga dakin ya sauko kasa ya fice daga falon daga Miwan har Namra dake falon be cewa kowa komai ba. Miwan ya bishi da harara

“Yaro nan fa ya raina mutane, idan zai shigo haka zai shigo babu sallama idan ya tashi be iya gaishe da kowa”

“Yaya idan ka ce zaka biye ta Hamad za ku yi ta samun matsala ne fa, Amma ma da tana nan fama take da shi balle kuma mu”

“Ba ruwana da rashin jinsa ko rashin kunya ni ubansa zanci Wallahi”
Chapter 18 · 0% Book details