Sashe 41
Huriyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Tun ina Amarya lokacin da aka hade mu, ta taba ce komai ta dade sai na bar mata mijinta, kuma sai ta saka ni na yi nadamar auren Alhaji, har abada kuma ba zata taba son ko ta so yayana ba, domin kallon da take min na yar aiki be canja ba a idonta, sai ta kakkabe ni kamar yadda ake kabe tabarma a gidan da yardar Allah, tun da na ci amanar ta sai na gani”
Hawaye ya sauko mata.
“Gashi kuma na fara gani, Wallahi da na san zuciyar Hajiya Kaltume ta kai haka da ba zan yarda na auri Alhaji ba duk kuwa da irin magiyar da zai min”
“Oh Allah mai iko, toh wai haka zaku zuba mata ido shikenan ta kashe Hamad ta ci bulus”
“Ba mu da tabbacin ita ta kasheshi, ba Hamad din muka gani ba balle ya fada mana ita ce ko ba ita ba, ko da ma ance yana raye ba lallai ne ya gane ita ta aikata ba, kuma ba jami'an tsaro suka kamata ba, ba mu da wata hujja ta cewar ita ce kawai dai zato muke yi”
Hindu ta sauke ajiyar zuciya ta yi tagumi.
“Toh ni Kam Alhamdulillah ina da kishiya amman Wallahi ba kamar ta ki ba, ba a aure aka aurota miye laifinki wani yace kar ta iya kula da mijinta, ba mai aiki ba namjji ko uwarki aka hallata masa aure Wallahi wani sai ya aureta balle kuma mai aiki, har yaushe zaka dauki hakki ka dorawa kanka”
“Wallahi ni kadai na san abun da yake damuna, wata rana ji nake kamar na yi ta ihu wani lokacin kuma na ji kamar na bi hanya na yi ta tafiya, wani sa'in na ji kamar zan yi hauka, gaba daya ni ma neman fita hayyacina nake”
“Au kuma shi ne kike zaune? Kuma Gwaggo ta saka miki ido? Wallahi zama be gan mu ba, idan ma ke ba zaki iya ba ni zan nema idan na kawo miki karki sha”
Hindu ta mike tsaye a fusace ta figi mayafinta tare da jaka ta nufi dakin Gwaggo, domin fahimtar da ita abun da Iyami ta gagara ganewa. Amma ta share hawayeta da ya zuba a fuskar Hamid.
“Wallahi na yi damar auren mahaifinku, na janwa kaina bala'i na kai kaina cikin manyan mata da ba su da imani babu tausayi, gashi na jefa yarana a cikin matsala, ban san kuma gaba ba me zan gani ba”
Ta fashe da kuka sosai tana jin zafin mutuwar Hamad, ga zafin rabata da Hurriya da Appa yayi ga kuma zafin mutuwar aurenta a lokacin da bata yi tsammani ba, ga kuma zafin ta haihu ya kasa zuwa ya duba abun da ta haifa balle ya saka musu albarka.
______________
Wai ni kam Tsakanin Hurriya da Amma waya fi kowa ban tausayi?
A Next page zamu dunguma a labarin Hurriya, karku manta sunan littafin Hurriya, a yanzu ne zai amsa cikaken sunansa.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨
𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲
Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660
𝐏𝐚𝐠𝐞 7⃣
Two days later...
Hindu ta ciro gorar ruwa dake cike da rubutu ta aje a gaban Amma.
“Yace wannan ki sha shi a tsaye kuma ki shafa zaki yi haka har kwana 7, na karya sihiri ne da tsari sosai”
Amma ta kai hannu ta dauka tana juya rubutun.
“Rabawa zan yi har bakwai kenan”
“Eh wannan kuma na hayaki ne, wato matar nan ba karamin asiri ta yi miki ba na shiga tsakaninki da Alhaji, kuma yanzu haka tana nan tana shirin yin wani akan Hurriya”
“Shi ma dai tsafin yake kenan?”
“Aa ba tsafi yake ba, kawai dai yana duba ne da kasa, ke ya dubo mana abubuwa da yawa fa, Wallahi ya ce yanzu haka ta yi miki jifa kuma tana daf da samun idan kuma ta same ki rayuwarki zata canja sai kin zama abar tausayi, ya ce idan baki tashi tsaye an yi yanka ba an maida mata da jefarta to zaki koma kwance ne, kuma ya tabbatar min idan aka yi haka ba jefarta ko asirin da ta yi sai ya karye”
Amma ta aje rubutun da sauri.
“Subhanallahi, Subhanallahi Hindu kin ji abun da nake gudu, wannan ai shirka ne”
“Wane irin shirka kuma? Ke fa matsala ne da ke, mu da muke neman warware sihiri? Ba fa sheri zamu yi ba warware ne”
Amma ta girgiza kai.
“Hmm hmm Hindu ba zan taba komai nasa ba, ba zan iya kauce hanya saboda duniya ba, komai mukaddari ne daga Allah”
Hindu ta rike baki.
“Toh ke ma dai ba a banza ta barki ba, wato sai da ta kwantar da ke ta yadda ba zaki iya yin komai ba”
“Ko ma dai minene ni dai ba zan yi yanka ba, ba zan aikata wani abun da zai hana ni kwanciyar kabari lafiya ba, saboda rayuwar duniya mai karewa, ni dai na bar komai ga Allah shi zai isar min, Allah ka isar min ga duk wanda yayi min cuta, ga duk wanda ya hana ni zama da mijina, ga duk wanda ya raba tsakanin Uba da Yarsa, Hindu Wallahi ba zan iya shirka ba, ki yi hakuri dan Allah zan baki kudin da kika kashe”
“Ba sai kin biya ba, ai na san mai kudi kika aura Hajiya Iyami, ni dai ban tafi gurin wani na ce yayi min tsafi ba, kuma dai ina sane ba zan yi shirka ba, amman na miki alkawari daga yau ba zaki sake jin bakina akan neman taimako ba kin yi da yar halak”
Ta fara tattara kayan tana sakawa a jakar, Amma na kokarin fahimtar da ita amman bata saurareta ba ta fice daga gidan cikin bacin rai. A gurin Amma aikata irin abubuwan nan shirka ne, neman taimakon wani wanda ba Allah ba shirka ne, Hindu kuma tana ganin matukar ba shari suka je nema ba, kuma ba wata ibada suka yi da Allah kadai ake yi ma ba, to ba su aikata shirka ba, fahimta ta sha banban sai aka samu sabanin ra'ayi kowa ya kasa fuskantar inda dan'uwansa ya dosa. Gwaggo ce ta fito daga dakinta ta zauna falon cikin yanayi na rashin jindadin abun da ya faru domin tana jin komai dake faruwa.
“Ai da baki mata haka ba, da sai ki karba ki aje ba dole sai kin yi amfani ba, kuma abun da be tsabawa addinin ba, ba a hanawa kai aikatawa Iyami, ke kanki kin san ruwa baya tsami banza kuma na tsorata da lamarin matar nan domin bata da imani”
“Gwaggo idan na karba kamar na yarda ne, kuma idan Kaltume bata da imani ta aikata tsafi mu ma sai mu biyeta mu aikata? Saboda namiji? Namijin da ko babu asiri zai iya cewa ya gaji da zama da ni, namijin da zan iya faduwa na mutu yau da dare ya sadu da abokiyar zamana? Ni kam ba zan yarda na zama daya daga cikin matan da Annabi ya ce mafi yawansu suna wuta ba, domin farkon abun da ke shigar da bawa a wuta tsabawa Allah ne da kin bin dokokinsa”
“Duk da haka dai, Iyami ki nemi tsarin jiki kuma ki nemi na karya sihiri ban ce ki yi tsafi ba, amman ki yi tunani”
Gwaggo ta tashi ta fice daga falon zuwa harabar gida. Amma ta girgiza kai.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, wai duk saboda kishi zai saka Kaltume ta aikata min haka kuma ta aikatawa yarana? Duk saboda namiji? Ka bata lahirarka? Appan Hurriya dama ban aureka ba, ina ma ban je gidan aiki ba”
Tana maganar hawaye na sauko mata. Ta dora duka hannayenta a kai tana jin kamar ta bude bakinta ta saka kara ba tare da an mata komai ba, gaba daya duniyar ta rikice mata kashe ya hade ta rasa ina zata sa kanta ta ji sanyi ina zata saka rayuwarta ta ji sassauci.
(Ni kan na ce anya akwai irin su Iyami kuwa🤔)
Hawaye ya sauko mata.
“Gashi kuma na fara gani, Wallahi da na san zuciyar Hajiya Kaltume ta kai haka da ba zan yarda na auri Alhaji ba duk kuwa da irin magiyar da zai min”
“Oh Allah mai iko, toh wai haka zaku zuba mata ido shikenan ta kashe Hamad ta ci bulus”
“Ba mu da tabbacin ita ta kasheshi, ba Hamad din muka gani ba balle ya fada mana ita ce ko ba ita ba, ko da ma ance yana raye ba lallai ne ya gane ita ta aikata ba, kuma ba jami'an tsaro suka kamata ba, ba mu da wata hujja ta cewar ita ce kawai dai zato muke yi”
Hindu ta sauke ajiyar zuciya ta yi tagumi.
“Toh ni Kam Alhamdulillah ina da kishiya amman Wallahi ba kamar ta ki ba, ba a aure aka aurota miye laifinki wani yace kar ta iya kula da mijinta, ba mai aiki ba namjji ko uwarki aka hallata masa aure Wallahi wani sai ya aureta balle kuma mai aiki, har yaushe zaka dauki hakki ka dorawa kanka”
“Wallahi ni kadai na san abun da yake damuna, wata rana ji nake kamar na yi ta ihu wani lokacin kuma na ji kamar na bi hanya na yi ta tafiya, wani sa'in na ji kamar zan yi hauka, gaba daya ni ma neman fita hayyacina nake”
“Au kuma shi ne kike zaune? Kuma Gwaggo ta saka miki ido? Wallahi zama be gan mu ba, idan ma ke ba zaki iya ba ni zan nema idan na kawo miki karki sha”
Hindu ta mike tsaye a fusace ta figi mayafinta tare da jaka ta nufi dakin Gwaggo, domin fahimtar da ita abun da Iyami ta gagara ganewa. Amma ta share hawayeta da ya zuba a fuskar Hamid.
“Wallahi na yi damar auren mahaifinku, na janwa kaina bala'i na kai kaina cikin manyan mata da ba su da imani babu tausayi, gashi na jefa yarana a cikin matsala, ban san kuma gaba ba me zan gani ba”
Ta fashe da kuka sosai tana jin zafin mutuwar Hamad, ga zafin rabata da Hurriya da Appa yayi ga kuma zafin mutuwar aurenta a lokacin da bata yi tsammani ba, ga kuma zafin ta haihu ya kasa zuwa ya duba abun da ta haifa balle ya saka musu albarka.
______________
Wai ni kam Tsakanin Hurriya da Amma waya fi kowa ban tausayi?
A Next page zamu dunguma a labarin Hurriya, karku manta sunan littafin Hurriya, a yanzu ne zai amsa cikaken sunansa.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨
𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲
Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660
𝐏𝐚𝐠𝐞 7⃣
Two days later...
Hindu ta ciro gorar ruwa dake cike da rubutu ta aje a gaban Amma.
“Yace wannan ki sha shi a tsaye kuma ki shafa zaki yi haka har kwana 7, na karya sihiri ne da tsari sosai”
Amma ta kai hannu ta dauka tana juya rubutun.
“Rabawa zan yi har bakwai kenan”
“Eh wannan kuma na hayaki ne, wato matar nan ba karamin asiri ta yi miki ba na shiga tsakaninki da Alhaji, kuma yanzu haka tana nan tana shirin yin wani akan Hurriya”
“Shi ma dai tsafin yake kenan?”
“Aa ba tsafi yake ba, kawai dai yana duba ne da kasa, ke ya dubo mana abubuwa da yawa fa, Wallahi ya ce yanzu haka ta yi miki jifa kuma tana daf da samun idan kuma ta same ki rayuwarki zata canja sai kin zama abar tausayi, ya ce idan baki tashi tsaye an yi yanka ba an maida mata da jefarta to zaki koma kwance ne, kuma ya tabbatar min idan aka yi haka ba jefarta ko asirin da ta yi sai ya karye”
Amma ta aje rubutun da sauri.
“Subhanallahi, Subhanallahi Hindu kin ji abun da nake gudu, wannan ai shirka ne”
“Wane irin shirka kuma? Ke fa matsala ne da ke, mu da muke neman warware sihiri? Ba fa sheri zamu yi ba warware ne”
Amma ta girgiza kai.
“Hmm hmm Hindu ba zan taba komai nasa ba, ba zan iya kauce hanya saboda duniya ba, komai mukaddari ne daga Allah”
Hindu ta rike baki.
“Toh ke ma dai ba a banza ta barki ba, wato sai da ta kwantar da ke ta yadda ba zaki iya yin komai ba”
“Ko ma dai minene ni dai ba zan yi yanka ba, ba zan aikata wani abun da zai hana ni kwanciyar kabari lafiya ba, saboda rayuwar duniya mai karewa, ni dai na bar komai ga Allah shi zai isar min, Allah ka isar min ga duk wanda yayi min cuta, ga duk wanda ya hana ni zama da mijina, ga duk wanda ya raba tsakanin Uba da Yarsa, Hindu Wallahi ba zan iya shirka ba, ki yi hakuri dan Allah zan baki kudin da kika kashe”
“Ba sai kin biya ba, ai na san mai kudi kika aura Hajiya Iyami, ni dai ban tafi gurin wani na ce yayi min tsafi ba, kuma dai ina sane ba zan yi shirka ba, amman na miki alkawari daga yau ba zaki sake jin bakina akan neman taimako ba kin yi da yar halak”
Ta fara tattara kayan tana sakawa a jakar, Amma na kokarin fahimtar da ita amman bata saurareta ba ta fice daga gidan cikin bacin rai. A gurin Amma aikata irin abubuwan nan shirka ne, neman taimakon wani wanda ba Allah ba shirka ne, Hindu kuma tana ganin matukar ba shari suka je nema ba, kuma ba wata ibada suka yi da Allah kadai ake yi ma ba, to ba su aikata shirka ba, fahimta ta sha banban sai aka samu sabanin ra'ayi kowa ya kasa fuskantar inda dan'uwansa ya dosa. Gwaggo ce ta fito daga dakinta ta zauna falon cikin yanayi na rashin jindadin abun da ya faru domin tana jin komai dake faruwa.
“Ai da baki mata haka ba, da sai ki karba ki aje ba dole sai kin yi amfani ba, kuma abun da be tsabawa addinin ba, ba a hanawa kai aikatawa Iyami, ke kanki kin san ruwa baya tsami banza kuma na tsorata da lamarin matar nan domin bata da imani”
“Gwaggo idan na karba kamar na yarda ne, kuma idan Kaltume bata da imani ta aikata tsafi mu ma sai mu biyeta mu aikata? Saboda namiji? Namijin da ko babu asiri zai iya cewa ya gaji da zama da ni, namijin da zan iya faduwa na mutu yau da dare ya sadu da abokiyar zamana? Ni kam ba zan yarda na zama daya daga cikin matan da Annabi ya ce mafi yawansu suna wuta ba, domin farkon abun da ke shigar da bawa a wuta tsabawa Allah ne da kin bin dokokinsa”
“Duk da haka dai, Iyami ki nemi tsarin jiki kuma ki nemi na karya sihiri ban ce ki yi tsafi ba, amman ki yi tunani”
Gwaggo ta tashi ta fice daga falon zuwa harabar gida. Amma ta girgiza kai.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, wai duk saboda kishi zai saka Kaltume ta aikata min haka kuma ta aikatawa yarana? Duk saboda namiji? Ka bata lahirarka? Appan Hurriya dama ban aureka ba, ina ma ban je gidan aiki ba”
Tana maganar hawaye na sauko mata. Ta dora duka hannayenta a kai tana jin kamar ta bude bakinta ta saka kara ba tare da an mata komai ba, gaba daya duniyar ta rikice mata kashe ya hade ta rasa ina zata sa kanta ta ji sanyi ina zata saka rayuwarta ta ji sassauci.
(Ni kan na ce anya akwai irin su Iyami kuwa🤔)