Sashe 6
Ni Da Yaya Sadam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Baba Ladi ta daga labule dakin ta shiga da sallama a bakinta. Sayyada ta bude lumsassun idanunta ta amsa tana kokarin mikewa zaune Baba ladi ta sami guri ta zauna tana fad'in"Ki tashi kisha kunun ga kosai na siyo mana yau gurin marka babu jama'a sosai shiyasa na dawo da wuri."
Sayyada ta mike zaune tana mutsika ido Baba Ladi ta bita da kallo tace"bacci kikayi ne naga duk kin sauya lokaci kankani."
Sayyada ta sunkuyar da kanta girgiza kanta tayi ba tace komai ba.
Baba Ladi bata kawo komai cikin ranta ba tace "Idan kin karya sai ki kwanta naga alama bacci kike ji." Ita dai Sayyada ba tace komai ba kwata kwata ma bata cikin nutsuwarta tun bayan fitarsa daga dakin.
Mazubi ta samo ta d'ibar masa kosan tana nufin shiga dakin shi kuma ya fito tace"Ina zakaje kuma ga kosan na kawo maka."
A dakile yace."Zanje can sashen Kawu Tanko na karya a can."
Ya kama hanyar futa Baba Ladi ta bishi da kallo tana gyda kai har sai da ya fita daga kofar ta dauke kanta tana girgiza kai tare da fad'in"Miskili kenan."
Kofar Kawu Tanko ya nufa lokacin Kawun tuni ya tafi gona suka gaisa da Baba Iyatu Amina ta fito daga daki a nutse ta gaisheshi ya saki fuska yana amsawa tace"Yaya Sadam! jiya kace zaka duba litattafai na makaranta."
Yace."Na manta ne amma yanzu jeki dauko in duba miki."
Ta mike da sauri ta nufi daki. Baba Iya tace"Kafin ku fara karatun bari in kawo maka kunu ka karya ko ayi maka wani abincin ne."!?
Yace."Kunun ma ya isa Baba." Tace."To." a cikin mazubi mai kyau ta kawo masa kunun tsamiya sai kamshi yake gwanin sha'awa gefe guda kuma ga wainar gero cikin wata Samira taji kuli-kuli tayi kyau.
Yace."Gaskiya Baba naji dadin wannan wainar na kwana biyu rabona da inyi irin wannan karin kummalon."
Baba Iya tace"Ai dama ku mutanan birni bakwa damuwa da cima irin wannan amma tafi gina jiki da kara lafiya."
Yace."Gaskiyar Baba." Hira suke da ita har ya kammala karyawa Amina ta dauko jakar makarantar ta ya duba sosai ya yaba da kokarin ta nan ya rasa kyautar da zaiyi mata yace."Me kike so na siya miki."!?
Mirmushi tayi yace."Ki fada mana aini nayi miki alkawari zan baki kyauta."
Tace."Ni kam Yayana kome ka bani ina so." Yace."Sai kin fadi me kike so kayan kwalliya ko zani ko mayafi."!?
Girgiza kai tayi yace."okey fadi me kike so."
Hannunsa ta kalla tana nuna wata siririyar azirfar dake hannunsa sai she'ki take.
Tace"Wannan zoben nake so kabani yana bani sha'awa."
Yayi tsai! yana kallonta na minti biyu yace."Wannan azirfar tawa tana da muhimanci Amina ki za'bi wani abun bayan ita."
Sai ta girgiza kai tace"Shikkenan kawai ka barshi."
Murmushi yayi yace."Bani hannunki na sa miki."
Ta matsa gurinsa da sauri tana dariyar farin ciki Azurfar ya ciro ya kama hannunta ya fara gwadawa duk tayi mata yawa dake Amina bata da wata 'kibar arziki haka ya tsunta ma suke sirara yace."Kinga tayi miki yawa ko." Dariya tayi tace"Kasa min a wannan hannun zata shiga." Sai ya kama hannun da ta nuna masa yana gwadawa......Sayyada ta shigo dakin taga abunda suke tsayawa tana kallonsu ta 'bata rai!!! fuuuuu! ta fice daga dakin tamkar zata fashe! duk suka bita da kallo Ta'be bakinsa yayi ya cigaba da abinda yake.
Sayyada kam da kuka ta shiga kofar su Baba Ladidi na shimfida tabarma ta tsaya tana tambayarta abinda ke faruwa.
Cikin kuka tace"Baba Nifa ban gane ba kunce Yaya Sadam! ni zai aura to me yasa naga kamar yana son Amina wallahi ni bazan yarda ba sai dai ta hakura ta bar min mijina."
Baba Marka ta fito daga dakinta tana fadin"Wace magana nake ji haka."?
Baba Ladi tace"To nima dai yanzu nake jin maganar gurin Sayyada wai me ya faru ne Sayyada."!?
Tace"Yanzu na shiga kofar su naga yana sa mata zoben al'kawari a hannu kawai ya fito ya fad'i gaskiyar magana ni yake so ko Amina."!?
Baba Marka tace"To aikuwa dai wannan maganar abar dubawa ce Sayyada bari na shiga inga abinda yake faruwa babu shakka Sadam yana nema ya mai damu kananun mutane."!
Baba Marka na fita Baba Ladidi tace "Zauna muyi magana Ta zauna tana share hawaye Baba Marka tace" Sayyada yanzu idan Sadam! yace zai had'aku ya aura da 'yar uwarki ashe ba zaki zauna da ita ba ko."? Wallahi baba ba zan zauna da ita ba sai dai ya za'ba ni ko ita shikkenan."
tsakaninta da Allah take maganar.
Baba Ladidi tayi shiru tana nazarin maganar lallai akwai matsala kenan. Yanzu idan Sadam! Amina yake so za'a samu matsala daga 'bangaran Sayyada kenan al'kwarin dake tsakaninsu zai iya rugujewa tunda shi Sadam! din yana da kafewa akan magana.
Baba Marka na shiga ta tarar dasu suna hira cikin fahintar juna cikin zuciyarta tace"Babu shakka, da gaske Sayyada takeyi.
Ta zauna kan kujera 'yar tsuguno tace"Kai Sadam! fito nan zamuyi magana."
Yace."Yanzu dama zan fito ina so in le'ka cikin gari gurin 'yan uwa za muje tare da Amina."
Tace"To babu laifi ai ke Amina kema zonan."
Suka fito tare tsugunawa yayi a gefanta amina kuma ta zauna kan tabarma.
Baba Marka tace"Ina so ku fad'a min abunda yake tsakaninku bana son munafurci kai Sadam! duk kaine me laifi."
Yace."Baba ban fahimci maganar ki ba."!?
Tace"Sayyada taje mana da wata magana shin da gaske ne kasawa Amina zoben al'kawari kana so ka aureta ne ko yaya."!?
A take yayi kicin-kicin da fuska yace."Wannan wace iriyar magana ce Baba."!?
Tace"Magana ce me mahimanci shin tsakanin Amina da Sayyada wa kake so kana kokarin kayi mana wasa da hankali."
Kai tsaye yace."Cikin su babu wacce nake so."!
Baba Marka ta bud'e baki tana kallonsa cike da mamaki tace"To wannan zoben da kasa mata fa na menene."!?
Yace."Kawai nayi ra'ayi ne ba na komai bane Sayyada da Amina babu wacce nake jin zan aura a cikinsu duk na daukesu a matsayin 'yan uwana ne.
Baba Marka tace"Aikuwa baka isa ba sai ka auri daya daga cikinsu."
Miskilin murmushi yayi ya mike yana kallon agogon dake daure a hannunsa yace."Baba naga alama zan daina shigowa garin nan mutukar zaku cigaba da damuna kan wannan maganar wai shin ni kadai ne namiji a wannan family din gasunan da yawa amma sai kuyi ta takura min da wata magana! Ke Amina tashi dauko gyalanki mu tafi ni duk garin ma ya fice min daga rai."! Yafada yana zura takalminsa.
Baba Marka tace"Ai komai zakayi sai dai kayi kana maganar ga Samari nan a famly ko wanne yana da matarsa a hannu kai kadai ne kayi shaura bakayi aure ba sai kace kuma mu zuba maka ido to baka isa ba to kaji."!
Yace."Sai kuyi ai." ! hanyar fita ya nufa Amina ta bi bayansa tana sanye da hijab har kasa takaici duk ya isheta da jin maganar sa inda yake cewa baya sonsu ita da Sayyada.
Sayyada na zaune a bakin kofar su suka fito tana ganinsu ta 'bata rai!! ko kallonta baiyi ba ya nufi babbar 'kofar da zata sada mutum da kofar gidan.....Amina tabi bayansa cikin sanyin Jiki.
Cike da takaici da bakin ciki ta bar gurin kan gadon karfen Baba Ladidi ta kwanta ta dinga kukan bakin ciki tana bala'in son Yaya Sadam! shiyasa bata son kowa ya ra'be shi ta lura kuma shi ya tsaneta kamar yafi son Amina akanta.
****
Sai Yamma li'kis! suka dawo gida Sadam? sam bai shiga ciki ba sai yayi zamansa a majalisar Samarin garin inda ya saba zama idan ya shigo garin sai kusan tara da rabi na dare ya shigo gidan......Dama yayi zuciya yace ba zai kwana bangaran su Baba Ladidi ba saboda yasan zasu takura masa sai ya nufi kofar Kawu Tanko yana sanya kafar sa ya hango Sayyada jikin kyaure('kofa) tana tauna gyalanta shi kuma saurayin yana tsaye a kanta, kamar ma zai rungume ta gabansa ya fad'i! da sauri ya dawo da baya kai tsaye ya nufi inda suke.
Yana isa yaji muryar ta tana fad'in"Nifa ba wai bana sonka bane kawai an riga anyi min miji dan uwana ne don haka kayi hakuri don Allah yanzu ma Baba Ladidi ce tace nazo na baka hakuri ka daina zuwa zance."!
Talle ya cire hular dake kansa yana fifita da ita yace."Haba baby ai al'kawari bai ce haka ba ki duba lamarin da kyau ki tausayawa masoyink......Kafin ya karasa suka ganshi a tsaye a kansu fuskarsa kamar hadarin da yake daf da zubar da ruwa.
Sayyada tasha kunu! har yanzu haushinsa takeji kuma tayi al'kawarin sai taci mutuncin Amina tunda ta shiga gonar ta.
Talle ya kalleshi she'keke babu shakka shine wanda Sayyada take fada mijinta......Sadam! yayi musu wani irin kallo yana ya tsine fuska saboda yanda yake jin tsamin daud'a had'e da warin hammata ya cika gurin zuciyarsa har ta fara tashi miyau ya tsartar! ya d'auke kansa kwata kwata baya son kallon Talle saboda yanda yake hango wani bushashshan tasono a 'kofofin hancin sa abun 'kyamkyami! sosai yayi mamakin yanda akayi Sayyadar ta tsaya a gurin har take sha'kar wannan warin.
A murtuke yace."Kai Malam kama hanya ka tafi hirar ta isa haka ko baka san dare yayi bane uhum!? ya kalli Sayyada dake cin kunu yace."Ke kuma shashasha! kin tsaya kina sha'kar wannan mugun warin sai ya d'aure miki ciki ko da yake dake dashi duk d'aya kuke kema 'kazamar ce."!
Tace."To ina ruwanka damu."! "Eh babu ruwana daku ai ban ce wani abu ba masoya cewa nayi dare yayi ke ki shiga gida shi kuma ya tafi gida sai kuma gobe."!
Talle yace." Kaga Malam babu ruwanka damu ya muna soyayya zaka shiga tsakaninmu shin kai kuwa kasan menene so kuwa."!?
Sadam! ya saki wani murmushi na takaici yace."A'a ban sani ba sai kai Laila majnun! ko zaka koya min ne guy."! Talle yayi wani juyi yana fad'in"In kana so sai a ko ya maka." Tsaki yaja yana ya mutsa fuska yace."Sayyada wuce ki shiga gida." Zum'bura baki tayi tace"Ni ka kyaleni nayi zance na kai ma ba d'azu kayi da Amina ba to menene zakace dole sai na shiga gida."
Sayyada ta mike zaune tana mutsika ido Baba Ladi ta bita da kallo tace"bacci kikayi ne naga duk kin sauya lokaci kankani."
Sayyada ta sunkuyar da kanta girgiza kanta tayi ba tace komai ba.
Baba Ladi bata kawo komai cikin ranta ba tace "Idan kin karya sai ki kwanta naga alama bacci kike ji." Ita dai Sayyada ba tace komai ba kwata kwata ma bata cikin nutsuwarta tun bayan fitarsa daga dakin.
Mazubi ta samo ta d'ibar masa kosan tana nufin shiga dakin shi kuma ya fito tace"Ina zakaje kuma ga kosan na kawo maka."
A dakile yace."Zanje can sashen Kawu Tanko na karya a can."
Ya kama hanyar futa Baba Ladi ta bishi da kallo tana gyda kai har sai da ya fita daga kofar ta dauke kanta tana girgiza kai tare da fad'in"Miskili kenan."
Kofar Kawu Tanko ya nufa lokacin Kawun tuni ya tafi gona suka gaisa da Baba Iyatu Amina ta fito daga daki a nutse ta gaisheshi ya saki fuska yana amsawa tace"Yaya Sadam! jiya kace zaka duba litattafai na makaranta."
Yace."Na manta ne amma yanzu jeki dauko in duba miki."
Ta mike da sauri ta nufi daki. Baba Iya tace"Kafin ku fara karatun bari in kawo maka kunu ka karya ko ayi maka wani abincin ne."!?
Yace."Kunun ma ya isa Baba." Tace."To." a cikin mazubi mai kyau ta kawo masa kunun tsamiya sai kamshi yake gwanin sha'awa gefe guda kuma ga wainar gero cikin wata Samira taji kuli-kuli tayi kyau.
Yace."Gaskiya Baba naji dadin wannan wainar na kwana biyu rabona da inyi irin wannan karin kummalon."
Baba Iya tace"Ai dama ku mutanan birni bakwa damuwa da cima irin wannan amma tafi gina jiki da kara lafiya."
Yace."Gaskiyar Baba." Hira suke da ita har ya kammala karyawa Amina ta dauko jakar makarantar ta ya duba sosai ya yaba da kokarin ta nan ya rasa kyautar da zaiyi mata yace."Me kike so na siya miki."!?
Mirmushi tayi yace."Ki fada mana aini nayi miki alkawari zan baki kyauta."
Tace."Ni kam Yayana kome ka bani ina so." Yace."Sai kin fadi me kike so kayan kwalliya ko zani ko mayafi."!?
Girgiza kai tayi yace."okey fadi me kike so."
Hannunsa ta kalla tana nuna wata siririyar azirfar dake hannunsa sai she'ki take.
Tace"Wannan zoben nake so kabani yana bani sha'awa."
Yayi tsai! yana kallonta na minti biyu yace."Wannan azirfar tawa tana da muhimanci Amina ki za'bi wani abun bayan ita."
Sai ta girgiza kai tace"Shikkenan kawai ka barshi."
Murmushi yayi yace."Bani hannunki na sa miki."
Ta matsa gurinsa da sauri tana dariyar farin ciki Azurfar ya ciro ya kama hannunta ya fara gwadawa duk tayi mata yawa dake Amina bata da wata 'kibar arziki haka ya tsunta ma suke sirara yace."Kinga tayi miki yawa ko." Dariya tayi tace"Kasa min a wannan hannun zata shiga." Sai ya kama hannun da ta nuna masa yana gwadawa......Sayyada ta shigo dakin taga abunda suke tsayawa tana kallonsu ta 'bata rai!!! fuuuuu! ta fice daga dakin tamkar zata fashe! duk suka bita da kallo Ta'be bakinsa yayi ya cigaba da abinda yake.
Sayyada kam da kuka ta shiga kofar su Baba Ladidi na shimfida tabarma ta tsaya tana tambayarta abinda ke faruwa.
Cikin kuka tace"Baba Nifa ban gane ba kunce Yaya Sadam! ni zai aura to me yasa naga kamar yana son Amina wallahi ni bazan yarda ba sai dai ta hakura ta bar min mijina."
Baba Marka ta fito daga dakinta tana fadin"Wace magana nake ji haka."?
Baba Ladi tace"To nima dai yanzu nake jin maganar gurin Sayyada wai me ya faru ne Sayyada."!?
Tace"Yanzu na shiga kofar su naga yana sa mata zoben al'kawari a hannu kawai ya fito ya fad'i gaskiyar magana ni yake so ko Amina."!?
Baba Marka tace"To aikuwa dai wannan maganar abar dubawa ce Sayyada bari na shiga inga abinda yake faruwa babu shakka Sadam yana nema ya mai damu kananun mutane."!
Baba Marka na fita Baba Ladidi tace "Zauna muyi magana Ta zauna tana share hawaye Baba Marka tace" Sayyada yanzu idan Sadam! yace zai had'aku ya aura da 'yar uwarki ashe ba zaki zauna da ita ba ko."? Wallahi baba ba zan zauna da ita ba sai dai ya za'ba ni ko ita shikkenan."
tsakaninta da Allah take maganar.
Baba Ladidi tayi shiru tana nazarin maganar lallai akwai matsala kenan. Yanzu idan Sadam! Amina yake so za'a samu matsala daga 'bangaran Sayyada kenan al'kwarin dake tsakaninsu zai iya rugujewa tunda shi Sadam! din yana da kafewa akan magana.
Baba Marka na shiga ta tarar dasu suna hira cikin fahintar juna cikin zuciyarta tace"Babu shakka, da gaske Sayyada takeyi.
Ta zauna kan kujera 'yar tsuguno tace"Kai Sadam! fito nan zamuyi magana."
Yace."Yanzu dama zan fito ina so in le'ka cikin gari gurin 'yan uwa za muje tare da Amina."
Tace"To babu laifi ai ke Amina kema zonan."
Suka fito tare tsugunawa yayi a gefanta amina kuma ta zauna kan tabarma.
Baba Marka tace"Ina so ku fad'a min abunda yake tsakaninku bana son munafurci kai Sadam! duk kaine me laifi."
Yace."Baba ban fahimci maganar ki ba."!?
Tace"Sayyada taje mana da wata magana shin da gaske ne kasawa Amina zoben al'kawari kana so ka aureta ne ko yaya."!?
A take yayi kicin-kicin da fuska yace."Wannan wace iriyar magana ce Baba."!?
Tace"Magana ce me mahimanci shin tsakanin Amina da Sayyada wa kake so kana kokarin kayi mana wasa da hankali."
Kai tsaye yace."Cikin su babu wacce nake so."!
Baba Marka ta bud'e baki tana kallonsa cike da mamaki tace"To wannan zoben da kasa mata fa na menene."!?
Yace."Kawai nayi ra'ayi ne ba na komai bane Sayyada da Amina babu wacce nake jin zan aura a cikinsu duk na daukesu a matsayin 'yan uwana ne.
Baba Marka tace"Aikuwa baka isa ba sai ka auri daya daga cikinsu."
Miskilin murmushi yayi ya mike yana kallon agogon dake daure a hannunsa yace."Baba naga alama zan daina shigowa garin nan mutukar zaku cigaba da damuna kan wannan maganar wai shin ni kadai ne namiji a wannan family din gasunan da yawa amma sai kuyi ta takura min da wata magana! Ke Amina tashi dauko gyalanki mu tafi ni duk garin ma ya fice min daga rai."! Yafada yana zura takalminsa.
Baba Marka tace"Ai komai zakayi sai dai kayi kana maganar ga Samari nan a famly ko wanne yana da matarsa a hannu kai kadai ne kayi shaura bakayi aure ba sai kace kuma mu zuba maka ido to baka isa ba to kaji."!
Yace."Sai kuyi ai." ! hanyar fita ya nufa Amina ta bi bayansa tana sanye da hijab har kasa takaici duk ya isheta da jin maganar sa inda yake cewa baya sonsu ita da Sayyada.
Sayyada na zaune a bakin kofar su suka fito tana ganinsu ta 'bata rai!! ko kallonta baiyi ba ya nufi babbar 'kofar da zata sada mutum da kofar gidan.....Amina tabi bayansa cikin sanyin Jiki.
Cike da takaici da bakin ciki ta bar gurin kan gadon karfen Baba Ladidi ta kwanta ta dinga kukan bakin ciki tana bala'in son Yaya Sadam! shiyasa bata son kowa ya ra'be shi ta lura kuma shi ya tsaneta kamar yafi son Amina akanta.
****
Sai Yamma li'kis! suka dawo gida Sadam? sam bai shiga ciki ba sai yayi zamansa a majalisar Samarin garin inda ya saba zama idan ya shigo garin sai kusan tara da rabi na dare ya shigo gidan......Dama yayi zuciya yace ba zai kwana bangaran su Baba Ladidi ba saboda yasan zasu takura masa sai ya nufi kofar Kawu Tanko yana sanya kafar sa ya hango Sayyada jikin kyaure('kofa) tana tauna gyalanta shi kuma saurayin yana tsaye a kanta, kamar ma zai rungume ta gabansa ya fad'i! da sauri ya dawo da baya kai tsaye ya nufi inda suke.
Yana isa yaji muryar ta tana fad'in"Nifa ba wai bana sonka bane kawai an riga anyi min miji dan uwana ne don haka kayi hakuri don Allah yanzu ma Baba Ladidi ce tace nazo na baka hakuri ka daina zuwa zance."!
Talle ya cire hular dake kansa yana fifita da ita yace."Haba baby ai al'kawari bai ce haka ba ki duba lamarin da kyau ki tausayawa masoyink......Kafin ya karasa suka ganshi a tsaye a kansu fuskarsa kamar hadarin da yake daf da zubar da ruwa.
Sayyada tasha kunu! har yanzu haushinsa takeji kuma tayi al'kawarin sai taci mutuncin Amina tunda ta shiga gonar ta.
Talle ya kalleshi she'keke babu shakka shine wanda Sayyada take fada mijinta......Sadam! yayi musu wani irin kallo yana ya tsine fuska saboda yanda yake jin tsamin daud'a had'e da warin hammata ya cika gurin zuciyarsa har ta fara tashi miyau ya tsartar! ya d'auke kansa kwata kwata baya son kallon Talle saboda yanda yake hango wani bushashshan tasono a 'kofofin hancin sa abun 'kyamkyami! sosai yayi mamakin yanda akayi Sayyadar ta tsaya a gurin har take sha'kar wannan warin.
A murtuke yace."Kai Malam kama hanya ka tafi hirar ta isa haka ko baka san dare yayi bane uhum!? ya kalli Sayyada dake cin kunu yace."Ke kuma shashasha! kin tsaya kina sha'kar wannan mugun warin sai ya d'aure miki ciki ko da yake dake dashi duk d'aya kuke kema 'kazamar ce."!
Tace."To ina ruwanka damu."! "Eh babu ruwana daku ai ban ce wani abu ba masoya cewa nayi dare yayi ke ki shiga gida shi kuma ya tafi gida sai kuma gobe."!
Talle yace." Kaga Malam babu ruwanka damu ya muna soyayya zaka shiga tsakaninmu shin kai kuwa kasan menene so kuwa."!?
Sadam! ya saki wani murmushi na takaici yace."A'a ban sani ba sai kai Laila majnun! ko zaka koya min ne guy."! Talle yayi wani juyi yana fad'in"In kana so sai a ko ya maka." Tsaki yaja yana ya mutsa fuska yace."Sayyada wuce ki shiga gida." Zum'bura baki tayi tace"Ni ka kyaleni nayi zance na kai ma ba d'azu kayi da Amina ba to menene zakace dole sai na shiga gida."