← Book details Ni Da Yaya Sadam Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 30

Sashe 28

Ni Da Yaya Sadam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"A gaskiya Sweetheart baka sona ta yaya zan iya xama a wani gurin kana cikin wannan hali karfa ka manta da cewar kaine za'bin raina farin cikin zuciyata."

Sayyada taji wani irin gumi mai d'umi!! na tsiyaya a jikinta....Ido jawur take kallonsu shi kuma sai murmushi yake kamar bashi ne masifaffan nan ba.....Inda suke ta nufa ta tsaya kansa"Baiwar Allah daga ina? kin shigowa mutane daki babu sallama babu neman iso sai kace wata kafura ai kafuran ma suna sallama da Hi ko makamancin hak"

Wani wawan kallo Halima kewa Sayyada cikin nuna ke wacece tace"Ke! ni kike fad'awa wannan maganar."? Sayyada tace"Baiwar Allah ba magana bace gyara ne nayi miki domin naga alamar kina yin abu irin na marasa hankali."

"Kutttt!!!! Sweetheart wannan wace jahilar yarinya ce take min maganar banza yanzu zan sanya a daureta wallahi."

Ya kalli Sayyada yana wani cin mur!!! "Ke bar gurun nan kinzo kin tsaya kan mutane saboda rashin tarbiya."

"Wallahi ba zan bar gurin nan ba.." Tafad'a cikin fad'awar gaba ga dukanin alamu matar nan nada matsayi mai karfi a gurinsa......"Wai Sweetheart wannan yarinyar a ina ka samo ta dagani 'yar kauye ce duba da yanda take maganar *He da He* ." Dariya ce ta kusa kufce masa yanda Halima ta fad'i maganar sharri ne kawai amma Sayyada bata irin wannan maganar ta *He da he* "Zaki bar gurin nan ko sai na sanya yanzu anzo anyi waje dake." Halima ce tayi wannan magana cikin hayaniya....Sayyada ta gyara tsayuwarta har da rike karfen gado tace"Sai dai in kece zaki fita daga dakin nan wallahi baki isa ki tambaye shi matsayina a gurinsa."!

Halima ta kalleshi wanda ya zuba musu ido kawai yana kallo Tace"Sweetheart bana son munafurci shin kai ma ka soma tara mata irin nasu Saleh." Yace."Ke bana son hauka malama wannan kanwata ce ita." Sayyada tace"Meye zaka 'boye mata kace mata ni matarka ce in yaso kome zatayi sai tayi."

Halima ta mike tsaye a zabure! tana fad'in"Da gaske take wannan maganar data fad'a."!!!!
'Karamin tsaki yaja "Ke! kinga nayi kama da wanda zai auri wannan 'yar 'kauyen Halima."! Tace." Nima dai haka na gani Sweetheart. " Sai ta koma ta zauna tana yiwa Sayyada kallon banza....Sayyada takaici ya turnuketa lallai Yaya Sadam! ita yake dizgawa gaban mutane......A zuciye tace"Ke Karuwa tashi ki fita daga d'akin nan ko kuma in tara miki jama'a."!! Halima tace"Ke!!! ni kike kira da karuwa don kutumar ubanki kin san waye ubana kuwa."!?? Sayyada tace"Oho! miki ko waye ubanki bai dame ni ba." A zafafe! Halima ta tsinka mata mari! ta sha'ke mata wuya ga hijab a jikinta......."Ke!!! Halima saketa."! yafada cikin karfin murya."Sweetheart kana jin abinda take cewa ko."!? "Eh naji saketa." Halima ta saketa tana huci!! Sayyada ta karkad'e hijab dinta ko a jikinta itama sai huci take....."Sayyada fita daga d'akin nan."!! cikin tsawa! yayi maganar da nufin tozarta mutum. gwiwowinta duk sukayi sanyi ta kalleshi ya ware mata manya manya idonsa wanda sai zaiyi rashin mutunci yake bud'esu."Ko bakiji abinda nace ba Fita a d'akin nan."!!! Wani 'karfin zuciya yazo mata tace"Ko baka fad'a zan fita yanzu." 'Kofar fita ta nufa zuciyarta na wata iriyar tafarfarsa..........!

13/6/2020

*BINTA UMAR ABBALE*

_*Littafin Ni da Yaya Sadam! na kudi ne 1_2 #400 ga masu bukata zasu tura kudin ta wannan accont din......0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars zan fada mata yanda zata biya kudin....08089965176 _07084653262.......Mutanan Nijar idan kuna bukata to zaku tura dala dari ta wannan numbar....9089976 _88137740 katin airtal ko orange Dala dari uku kudin Najeria.*_
*NI DA YAYA SADAM!!*
👫👫

*NA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*

*🌍MANAZARTA*
*WRITES ASSOCIATION🖊📚*
*M.W.A*

_'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu nazari da aiki da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta._
__________________________________

*Wannan shine Last Free Pege*
*Free Pege 20*
Da sauri ta bude kofa ta fice daga dakin zuciyarta na wata irinyar tafarfasa rarraba ido take a harabar gurin....Kai tsaye kawai sai ta nufi 'katon gate d'in da yake cike da sojoji ko tsoro ba taji burinta kawai ta fice daga bracck d'in bata ta'ba tsammanin Sadam! zaiyi mata irin wannan wulakancin ba, tana tafiya tana share hawayen bakin ciki tayi tayi ta tsayar da hawayen abun ya fassakara dole ta kyalesu suna zuba

Bayan fitar ta daga d'akin saboda ya san wautarta sai ya dauki wayarsa ya kira d'aya daga cikin sojojin dake bakin gate din yace."Za suga wata yarinya ta fito 'yar kimanin shekaru 15 ko kasa da haka tana sanye da atamfa blue kar su barta ta fita......Aikuwa hakane ya faru Sayyada na isa suka tare mata hanya tayi tayi su bude mata suka 'ki kawai sai ta nemi gurin bakin gate din ta sanya kukan bakin ciki.

Lokacin da yake wayar Halima ta sha'ka da yawa bayan ya gama wayar tace"Wai menene idan ta fita da zaka damu nifa jikina ya soma bani akwai wani abu a tsakanika da yarinyar nan wallahi." Yace."Babu wani abu a tsakaninmu na fad'a miki kanwata ce karki damu." Dake ta saba da wannan dad'in bakin nasa sai ta warware tace"Ya maganar auranmu to." ? kallon shashasha! yayi mata yace."Ashe baki aje wannan maganar a gefe ba kenanan."! Halima ta tunzura tana huci! tace"Wallahi ba zan ajiye maganar nan ba har sai na cimma burina akanka kome zakayi min zan jure.''Shiru yayi mata kawai.....Ta cigaba da cewa"Yanzu ka bakaji kunyar fada min wannan maganar ba? wane irin sone ban nuna maka ba zakace na ajiye maganar aura a tsakanina da kai insha Allahu kamar anyi an gama."

Kallon mahaukaciya kawai yake mata yo shi wannan ko da matan duniya zasu kare baya ta'ba jin xai iya auranta......Wayarshi ce tayi kara yana dubawa yaga Mu'azu daya daga cikin sojojin bakin gate yace."Yallabai yarinyar nan fa gata ta zauna tana turjiya kan hanya kuka kawai takeyi."

Yaji wani iri a jikinsa jin abinda Mu'azu yace."Please Mu'azu kayi kokarin kawo min ita dakin dana ke kwance." Mu'azu yace."Okey insha Allah."

Babu irin rarrashin da Mu'azu baiyi mata ba amma fafur ta'ki binsa ita dole sai sun bude mata kofa ta fita.....Mu'azu ya kara kiran numbarsa a karo na biyu Yace."Kayi kokari ka bata wayar kace zamuyi magana." Nan ma Sayyada ta'ki kar'bar wayar zuwa yanzu ta daina kukan sai dai bakin ciki dake cin zuciyarta.....Koda Mu'azu ya sanar dashi cewar ta'ki kar'bar wayar sai hankalinsa ya tashi har ya yunkura zai tashi da nufi yaje ya dawo da ita sai zuciyarsa ta raya masa cewar kar yaje ya rarrasheta mutuncinsa zai zube a gurinta....Ya koma ya kwanta fuska a cud'e!......Halima kam tana ganin hankalinsa ya tashi kan yarinyar sai ta fashe da kuka ta mike a zafafe take farfad'a masa ba'kaken maganganu....Wanda suka sanya ya buga mata muguwar tsawar da ta sanya ta d'ibi takalmanta a hannu ta fice daga dakin......Hankali a tashe ta nufi bakin gate d'in ganin Sayyada a tsugune ya sanya ta isa inda take ba tare da tace mata komai ba ta mikar da ita tana girgiza kafadarta ''Ki fad'a min gaskiya meye alakarki da Sadam! Dazu kinyi wata magana wacce ta sanya jikina yayi sanyi don girman Allah karkiji tsorona." Sayyada tace"A kan me zanji tsoronki Ci kike bani ko sha ko kuma aljanna kike rabawa da zanji tsoranki gaskiyar magana shine Ni Sayyada matar Sadam! ce yau kwananmu shida da daurin aure."

Halima ta silale a gurin ta fad'i ji take kamar ta d'ora hannu aka tayi ta kurma ihu!!! gumi duk ya jikata....."Ni Sadam! zai yaudara jama'a!?? Hawaye ne suka soma kwarya a fuskarta

Sayyada ta saki baki tana kallonta wai kuka take kan d'a namiji lallai bata da hankali....To ganin Halima na hawaye sai hankalin sojojin nan ya tashi sanin wacece halima yasa suka fara gutsi tsoma a tsakaninsu suma sai yanzu suka fahimci cewar ashe Sayyada itace amaryar Sadam! da yaje can kauye aka aura masa lallai Sadam bai kyauta ba kuma a zahirin gaskiya ya yaudari Halima domin ta sakankance da cewar zai aureta amma ya yaudareta.

Mikewa tayi a jigace ta gyara yafan mayafinta ta dauko pose dinta ta koma dakin da Sadam din yake......Ya mike tsaye idanunsa a kan kofa yana so yaga shigowar yarinyar halima ta fado dakin yanda ya ganta a Jigace sai da gabansa ya fad'i yasan hali bata da hankali yanzu zatayi masa hauka sai ya daure fuska tamau! yana kallonta yace."Ba cewa nayi ki fice ki bar min daki ba tunda kema b......Bai karasa ba ta daga masa hannu "Rufe min baki bakin algungumi azzalimi! Sai ya saki baki yana kallonta tace" Nan ka fada min cewar yarinyar kanwarka har da rantsewa yanzu kuma ina fita ita ta tabbatar min da cewar matarka ce yau kwana shida da daura muku aure Sadam! ni zaka yaudara? ashe dama xaka iya yi min haka a irin kauna da son da nakeyi maka."? tana hawaye take maganar....Tausayi ta bashi yace."Kinga Karki dauka wannan auran zaiyi tasiri sam! bana son yarinyar kawai umarnin iyaye na nabi amma ke kanki kin san yarinyar ba sa'ar aurena bace idan kin kwantar da hankali ki nan gaba kadan zata zama 'yar aikin gidanki."

"Ai na daina yarda da wad'anannan kalaman naka na yaudara wallahi ka bani mamaki Sadam! ashe kai mayaudari ne ban sani ba."

Shan kunu yayi yace."Idan kin san ba'kaken maganganu zaki fad'a min to sawunki a likkafa ki kama hanya ki fice idan raina ya 'baci ba zakiji dad'i ba."
Chapter 28 · 0% Book details