Sashe 15
Ni Da Yaya Sadam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Habu yace."Amma wannan magana ta bani mamaki wallahi wato kai da sai ranar daurin auran sannan ne zaka sanar damu."?
Ta'be baki yayi yace."Auran ne bana so kawai shiyasa sam! bana d'okinsa har so nake lokacin tafiyar yazo in matsa in basu guri."
Captain Habu yace."Amma ka bani mamaki wallahi!!! Sadam! murmishi kawai yayi baice komai ba, Habu yace."In tambaye ka mana."
Yace."Ina sauraronka." Yace."Yanzu ya zakayi da Halima idan taji maganar auranka baka tunanin abinda zai faru da ita."?
Sadam! ya 'bata fuskarsa yace."Wai shin Habu ni nake son Halima ko kuma ita ke sona."!? Captain Habu yace."Itace take sonka." Sai ya d'aga kafad'a yana ya mutsa fuska yace."To kagani ni banda matsala tunda dai ni da bakina ba'a ta'baji nace ina sonta ba ballanta kuce na yaudareta itake yaudarar kanta tunda tasan ni ba mahaukaci bane da zan aureta bayan kowa ya mayar da ita rigar sanyawarsa Kawai ina biye mata ne saboda darajar son da take min wannan shine dalili."
Captain Habu ya girgiza kai yace."Tabbas to amma ni ina tunanin al'amarin da zai faru taji labarin auranka wallahi zata iya kashe kanta saboda bakin ciki."
Sadam! yasa dariya yana kallon abokin nasa yace."Na lura kana tausayawa Halima da yawa kaje kawai ka aureta na bar maka kai nifa har yanzu banga wata 'ya macen da zata ya mutsa min tunani ba wallahi idan ba Uwata ba bana daukar wata mace wani abu saboda dukaninsu basu da kirki.''
Sulaiman yace."Me yayi zafi kake wannan maganar mace ni'ima ce ga d'a namiji sa'ida ce kuma salama ce ba zaka san da haka ba sai ranar da kayi aure sannan zaka gane abinda nake so ka gane."
Murmushi kawai yayi Habu yace."Don Allah abokina ka dinga 'kimanta mata kuma idan na baka shawara ka dinga dauka kamar yanda idan ka bani shawara nake dauka."
Yace."To na dauka." Habu yace."To yanzu yaushe zaka kaini inga amaryar tamu."?
'Bata fuska yayi yace."Kaji ka da wani zance kuma ka bari kawai ai in an daura auran nan zan kawo ta kaduna."
Yace."A'a dole fa kafin daurin aure muje in ganta gaskiyar magana kenan.'' Okey Zamu je insha Allah sati me zuwa."! Habu yace."Allah ya kaimu lafiya." To da wannan magana sukayi sallama Captain Habu yayi masa sallama ya koma ofis din sa.
*****
Sulaiman kuwa bayan komawarsa Kaduna sai da yayi jinyar zuciyarsa na sati guda sannan ya shirya tsaf ya nufi kasar india domin cigaba da gudanar da harkokinsa na kasuwanci Sulaiman komai da ruwanka ne shi ko wace sana'a tashi ce ya fita 'kasashen waje da dama domin gudanar da harkokinsa shiyasa kullum Allah yake kara yalwata masa arzkinsa gashi yana d'an ta'ba siyasa in lokacinta yazo.
Da tunanin Sayyada ya nufi 'kasar hindu.
****
Sayyada fa ananan ana rawar kai da giringid'ishi kullum ana gidan Mariya ana maganar aure ita kuma mariyar in ta kad'a magani da madara na 'karin ni'ima sai ta tsiyayawa Sayyadar tace ta shanye duk sanda mijinta ya soma kwanciyar aure da ita zaji dad'inta aikuwa Sayyada ta bada himma har ta zo gida tana fad'awa Baba Ladi tace"Ta had'a mata maganin Ni'ima wanda Sadam! zai dinga gamsuwa da ita yayin kwanciyar aure.
Baba Ladi da Baba Marka suka dinga salati da sallalami! Baba Ladi tace"Don Ubanki a ina kikaji waannan maganar." ? babu kunya tace"Mariya ce ta fad'a mata. Tundaga ranar Baba Ladi ta hanata fita tace tana zuwa gidan Mariya tana koya mata rashin kunya.....Sayyada kam! tace"Lallai Baba kar! kar! nake kallon kowa idan Baba Ladi ta idar da sallahar walha bacci ya kwashe ta sai ta lalla'ba ta fice daga gidan bata dawowa sai yamma Baba Ladidi ta dinga fad'a kamar ta ari baki.
Suna zaune a tsakiyar dakin Mariya Ummi ta shigo sai suka hau shewa harda tafawa Ummi tace"Wace wainar kuke toyawa ne? Sayyada akayi wani fari da ido akace "Ke ma kin san wainar."! Ummi ta bata hannu suka tafa suna dariya.
Mariya tace" Wai Ummi kinji so ta take ta samu maganin da zai 'kara mata girman nono saboda tana so ya dinga cikawa angon nata hannu." Sai suka kwashe da dariya Sayyada tace"Wallahi da gaske nakeyi ni kunya nakeji duba fa ki gani nono kananu ne ko rigar nono bana sawa fa."
Ummi tace"Ke Dallah! banza kawai Wallahi ki kwantar da hankalinki nononki zai fito yayinda aka kai ki gidan miji shikkenan kullum idan yana ta'bawa shikkenan sai dai kiga suna girma sun cika riga." Sayyada ta bata hannu suka tafa tace"Da gaske kike don Allah."?
Ummi tace"Wallahi da gaske nake." Mariya tace"Hakane nima fa lokacin da aka kawo ni gidanan ba nonon arziki gareni ba amma ko wata uku banyi ba naga nonowana sunyi manya manya." Dariya sukayi suka tafa Sayyada tace"Wayyo Allah na ni wallahi har na 'kagara lokacin nan yazo wai don Allah Mariya yaya mutum yake ji idan yana sha'awar d'a namiji wayyo."!!!!!!!
Ta kare maganar tana kwanciya tare da lumshe ido.
Ummi tace"Kai! Sayyada gaskiya ke fitananniya ce anya kuwa."!?? Sayyada ta kai mata duka tana dariya tace"Ke sonsa ne kawai yayi min yawa shiyasa sai kunyi min uziri." Mariya tace"Wai yaushe zamu ganshi ne nifa ban san shi ba nafi sanin Yaya Sulaiman."! Ummi tace"Wallahi nima ban sanshi ba jikina na bani kyakkyawa ne dan gayu."
Sayyada aka lumshe ido ana murmushi mi'kewa tayi zaune tace"Sojana kenan." Suka kalleta gabadaya sukace "Au! Soja ne dama."!? Daga kai tayi tace " Eh mana ai ba zaku gane shi ba tunda ba sosai yake zuwa ba sannan kuma idan yazo baya dad'ewa yake tafiya watarana ma yini guda yake ya tafi sannan shi bashi da fara'a kamar Yaya Sulaiman kullum fuskarsa a murtuke take nima fa baya wani sakar min fuska."
Mariya tace"Ai dole mana Amina tace shi take so shegiya ni wallahi haushinta ma nakeji." Sayyada taja tsaki tare da fad'in"Rabu da tsinanniya kawai ai tuntuni na daina kulata."
Mariya tace"Kinyi min dai-dai 'kawata." Tafawa sukayi suna dariya *To ni dai fitowa nayi na barsu na lura hirar tasu ba zata 'kare ba*
*****
Sayyada sam! bata sanya Amina cikin sabgarta da kawayenta kawai take harka ko Aminar ce ta shigo kofar su Sayyada ba tayi mata kallon arziki Ballanta ta kulata Baba Ladi tayi mata fad'a har ta gaji......Wannan lamari na masifar 'batawa Amina rai! shin wai meye duniyar ne akan Namiji Sayyada duk ta tayar da hankalinta tana gaba da ita itafa bata zafafa ba duk da tana son Sadam! to idan shi baya sonta ya zatayi dole ta hakura kuma idan yace ba zai aureta ba nan ma dole ta hakura ta fito da mijin aure ita a ganinta wannan ba abun tayar da hankali bane.
To ammafa a cikin ranta tanan da wannan kudiri na duk sanda Sadam! d'in ya shigo garin zata sanar masa halin da take ciki a kansa tasan idan ya hadasu duka ya aura ai ba haramun ya aikata ba.
****
Saura Sati guda daurin aure Baba Ladi da baba Marka tsaye gaban wani katon turmi me zurfi ko wanne da ta'barya mai tsayi a hannunsa dagab tukud'i suke da gumbar mata.
Tsaf! suka daka suka kwashe sannan suka zauna zaman had'awa! lokacin Sayyada nacan gidan Mariya wai nan dilka ake da kurkur Mariya ta dage! tana wa Sayyada dilka wai lallai sai tayi kyau kafin Ranar daurin aure.
Amina ce ta shiga kofar taga abinda sukeyi tace"Baba Wannan meye?"? Baba Marka tace"Zaki san ko meye idan lokacinki yazo maza kije gidan Mariya ki kirawo Sayyada." Amina tace"To." Ta nufi gidan Mariya dake bayan layi.
Tsakar gida ta tarar dasu sunyi d'an malele da yaji da manja harda tumatiri da albasa suna sha suna dariya da hirar aure kamar yanda suka saba.
Babu wacce ta amsa gaisuwarta sai kallon banza da suka watsa mata Amina tace"Sayyada kije Baba Ladidi na kiranki." Ta juya zata fita Sai taji Sayyada na kwaikwaiyar maganar ta da hanci "Wai Sayyada kije Baba Ladidi na kiranki yan! yan! yan!!!!! Ta juyo tana kallonsu sai suka kwashe da dariya Amina ta bar gidan da sauri takaici kamar ya kasheta wai Sayyada ce take biyewa wasu bare suna wulakantata......Sayyada ta wanke hannunta tare da zura hijab dinta tace" Bari naje na dawo yanzu." takalmanta tasa ta fice daga gidan.
Amina ta hango tana tafiya so take ta isketa har inda take ta ci mata Uwa! tana karya kwana taga motar da ya saba zuwa da ita garin tayi parking irin motocin nan ne na gurin aiki.Kafin ta an kara Taga ya fito daga motar tare da Abokinsa sai gabanta ya hau dukan uku uku! ta hau kallon jikinta wani ko d'ad'd'an zanin atamfa ne a jikinta da wata t_shirt mai karamin hannu kanta ko d'ankwali babu sai hijab data zurma "Wallahi ba zai ganni a haka ba." a fili tayi wannan maganar la'bewa tayi tana le'kensu inda taga Amina ta iskesu ta tsuguna har 'kasa ta gaishesu, girgiza kai tayi haushi ya turnuketa tana kallon sanda Yake amsawa yana mata dariyarsa mai tsada Sayyada kamar ta kurma ihu! sai cije baki take tana gyada kai tana kallonsu suka nufi cikin gidan tare........Sai bayan taga shigewarsu ne sannan ta fito daga inda ta 'buya. Gidan ta nufa duk ranta babu dadi.
6/6/2020
*BINTA UMAR ABBALE*
_*Littafin Ni da Yaya Sadam! na kudi ne 1_2 #400 ga duk mai bukatar karantawa sai ya tura kudinsa ta wannan accont din......0542382124.......Binta Umar gtbank idan kuma katin waya mutun zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din zan fad'a masa yanda zai biya kud'in....08089965176 _07084653262.....Mutanan Nijar idan kuna bukatar littafin to sai ku tura dala dari ta wannan numbars.....90899076 _88137740 katin airtal ko orange.....Dala dari itace a madadin dari uku na najeria.*_
*NI DA YAYA SADAM!!*
👫👫
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
*🌍MANAZARTA*
*WRITES ASSOCIATION🖊📚*
*M.W.A*
_'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu nazari da aiki da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta._
__________________________________
Ta'be baki yayi yace."Auran ne bana so kawai shiyasa sam! bana d'okinsa har so nake lokacin tafiyar yazo in matsa in basu guri."
Captain Habu yace."Amma ka bani mamaki wallahi!!! Sadam! murmishi kawai yayi baice komai ba, Habu yace."In tambaye ka mana."
Yace."Ina sauraronka." Yace."Yanzu ya zakayi da Halima idan taji maganar auranka baka tunanin abinda zai faru da ita."?
Sadam! ya 'bata fuskarsa yace."Wai shin Habu ni nake son Halima ko kuma ita ke sona."!? Captain Habu yace."Itace take sonka." Sai ya d'aga kafad'a yana ya mutsa fuska yace."To kagani ni banda matsala tunda dai ni da bakina ba'a ta'baji nace ina sonta ba ballanta kuce na yaudareta itake yaudarar kanta tunda tasan ni ba mahaukaci bane da zan aureta bayan kowa ya mayar da ita rigar sanyawarsa Kawai ina biye mata ne saboda darajar son da take min wannan shine dalili."
Captain Habu ya girgiza kai yace."Tabbas to amma ni ina tunanin al'amarin da zai faru taji labarin auranka wallahi zata iya kashe kanta saboda bakin ciki."
Sadam! yasa dariya yana kallon abokin nasa yace."Na lura kana tausayawa Halima da yawa kaje kawai ka aureta na bar maka kai nifa har yanzu banga wata 'ya macen da zata ya mutsa min tunani ba wallahi idan ba Uwata ba bana daukar wata mace wani abu saboda dukaninsu basu da kirki.''
Sulaiman yace."Me yayi zafi kake wannan maganar mace ni'ima ce ga d'a namiji sa'ida ce kuma salama ce ba zaka san da haka ba sai ranar da kayi aure sannan zaka gane abinda nake so ka gane."
Murmushi kawai yayi Habu yace."Don Allah abokina ka dinga 'kimanta mata kuma idan na baka shawara ka dinga dauka kamar yanda idan ka bani shawara nake dauka."
Yace."To na dauka." Habu yace."To yanzu yaushe zaka kaini inga amaryar tamu."?
'Bata fuska yayi yace."Kaji ka da wani zance kuma ka bari kawai ai in an daura auran nan zan kawo ta kaduna."
Yace."A'a dole fa kafin daurin aure muje in ganta gaskiyar magana kenan.'' Okey Zamu je insha Allah sati me zuwa."! Habu yace."Allah ya kaimu lafiya." To da wannan magana sukayi sallama Captain Habu yayi masa sallama ya koma ofis din sa.
*****
Sulaiman kuwa bayan komawarsa Kaduna sai da yayi jinyar zuciyarsa na sati guda sannan ya shirya tsaf ya nufi kasar india domin cigaba da gudanar da harkokinsa na kasuwanci Sulaiman komai da ruwanka ne shi ko wace sana'a tashi ce ya fita 'kasashen waje da dama domin gudanar da harkokinsa shiyasa kullum Allah yake kara yalwata masa arzkinsa gashi yana d'an ta'ba siyasa in lokacinta yazo.
Da tunanin Sayyada ya nufi 'kasar hindu.
****
Sayyada fa ananan ana rawar kai da giringid'ishi kullum ana gidan Mariya ana maganar aure ita kuma mariyar in ta kad'a magani da madara na 'karin ni'ima sai ta tsiyayawa Sayyadar tace ta shanye duk sanda mijinta ya soma kwanciyar aure da ita zaji dad'inta aikuwa Sayyada ta bada himma har ta zo gida tana fad'awa Baba Ladi tace"Ta had'a mata maganin Ni'ima wanda Sadam! zai dinga gamsuwa da ita yayin kwanciyar aure.
Baba Ladi da Baba Marka suka dinga salati da sallalami! Baba Ladi tace"Don Ubanki a ina kikaji waannan maganar." ? babu kunya tace"Mariya ce ta fad'a mata. Tundaga ranar Baba Ladi ta hanata fita tace tana zuwa gidan Mariya tana koya mata rashin kunya.....Sayyada kam! tace"Lallai Baba kar! kar! nake kallon kowa idan Baba Ladi ta idar da sallahar walha bacci ya kwashe ta sai ta lalla'ba ta fice daga gidan bata dawowa sai yamma Baba Ladidi ta dinga fad'a kamar ta ari baki.
Suna zaune a tsakiyar dakin Mariya Ummi ta shigo sai suka hau shewa harda tafawa Ummi tace"Wace wainar kuke toyawa ne? Sayyada akayi wani fari da ido akace "Ke ma kin san wainar."! Ummi ta bata hannu suka tafa suna dariya.
Mariya tace" Wai Ummi kinji so ta take ta samu maganin da zai 'kara mata girman nono saboda tana so ya dinga cikawa angon nata hannu." Sai suka kwashe da dariya Sayyada tace"Wallahi da gaske nakeyi ni kunya nakeji duba fa ki gani nono kananu ne ko rigar nono bana sawa fa."
Ummi tace"Ke Dallah! banza kawai Wallahi ki kwantar da hankalinki nononki zai fito yayinda aka kai ki gidan miji shikkenan kullum idan yana ta'bawa shikkenan sai dai kiga suna girma sun cika riga." Sayyada ta bata hannu suka tafa tace"Da gaske kike don Allah."?
Ummi tace"Wallahi da gaske nake." Mariya tace"Hakane nima fa lokacin da aka kawo ni gidanan ba nonon arziki gareni ba amma ko wata uku banyi ba naga nonowana sunyi manya manya." Dariya sukayi suka tafa Sayyada tace"Wayyo Allah na ni wallahi har na 'kagara lokacin nan yazo wai don Allah Mariya yaya mutum yake ji idan yana sha'awar d'a namiji wayyo."!!!!!!!
Ta kare maganar tana kwanciya tare da lumshe ido.
Ummi tace"Kai! Sayyada gaskiya ke fitananniya ce anya kuwa."!?? Sayyada ta kai mata duka tana dariya tace"Ke sonsa ne kawai yayi min yawa shiyasa sai kunyi min uziri." Mariya tace"Wai yaushe zamu ganshi ne nifa ban san shi ba nafi sanin Yaya Sulaiman."! Ummi tace"Wallahi nima ban sanshi ba jikina na bani kyakkyawa ne dan gayu."
Sayyada aka lumshe ido ana murmushi mi'kewa tayi zaune tace"Sojana kenan." Suka kalleta gabadaya sukace "Au! Soja ne dama."!? Daga kai tayi tace " Eh mana ai ba zaku gane shi ba tunda ba sosai yake zuwa ba sannan kuma idan yazo baya dad'ewa yake tafiya watarana ma yini guda yake ya tafi sannan shi bashi da fara'a kamar Yaya Sulaiman kullum fuskarsa a murtuke take nima fa baya wani sakar min fuska."
Mariya tace"Ai dole mana Amina tace shi take so shegiya ni wallahi haushinta ma nakeji." Sayyada taja tsaki tare da fad'in"Rabu da tsinanniya kawai ai tuntuni na daina kulata."
Mariya tace"Kinyi min dai-dai 'kawata." Tafawa sukayi suna dariya *To ni dai fitowa nayi na barsu na lura hirar tasu ba zata 'kare ba*
*****
Sayyada sam! bata sanya Amina cikin sabgarta da kawayenta kawai take harka ko Aminar ce ta shigo kofar su Sayyada ba tayi mata kallon arziki Ballanta ta kulata Baba Ladi tayi mata fad'a har ta gaji......Wannan lamari na masifar 'batawa Amina rai! shin wai meye duniyar ne akan Namiji Sayyada duk ta tayar da hankalinta tana gaba da ita itafa bata zafafa ba duk da tana son Sadam! to idan shi baya sonta ya zatayi dole ta hakura kuma idan yace ba zai aureta ba nan ma dole ta hakura ta fito da mijin aure ita a ganinta wannan ba abun tayar da hankali bane.
To ammafa a cikin ranta tanan da wannan kudiri na duk sanda Sadam! d'in ya shigo garin zata sanar masa halin da take ciki a kansa tasan idan ya hadasu duka ya aura ai ba haramun ya aikata ba.
****
Saura Sati guda daurin aure Baba Ladi da baba Marka tsaye gaban wani katon turmi me zurfi ko wanne da ta'barya mai tsayi a hannunsa dagab tukud'i suke da gumbar mata.
Tsaf! suka daka suka kwashe sannan suka zauna zaman had'awa! lokacin Sayyada nacan gidan Mariya wai nan dilka ake da kurkur Mariya ta dage! tana wa Sayyada dilka wai lallai sai tayi kyau kafin Ranar daurin aure.
Amina ce ta shiga kofar taga abinda sukeyi tace"Baba Wannan meye?"? Baba Marka tace"Zaki san ko meye idan lokacinki yazo maza kije gidan Mariya ki kirawo Sayyada." Amina tace"To." Ta nufi gidan Mariya dake bayan layi.
Tsakar gida ta tarar dasu sunyi d'an malele da yaji da manja harda tumatiri da albasa suna sha suna dariya da hirar aure kamar yanda suka saba.
Babu wacce ta amsa gaisuwarta sai kallon banza da suka watsa mata Amina tace"Sayyada kije Baba Ladidi na kiranki." Ta juya zata fita Sai taji Sayyada na kwaikwaiyar maganar ta da hanci "Wai Sayyada kije Baba Ladidi na kiranki yan! yan! yan!!!!! Ta juyo tana kallonsu sai suka kwashe da dariya Amina ta bar gidan da sauri takaici kamar ya kasheta wai Sayyada ce take biyewa wasu bare suna wulakantata......Sayyada ta wanke hannunta tare da zura hijab dinta tace" Bari naje na dawo yanzu." takalmanta tasa ta fice daga gidan.
Amina ta hango tana tafiya so take ta isketa har inda take ta ci mata Uwa! tana karya kwana taga motar da ya saba zuwa da ita garin tayi parking irin motocin nan ne na gurin aiki.Kafin ta an kara Taga ya fito daga motar tare da Abokinsa sai gabanta ya hau dukan uku uku! ta hau kallon jikinta wani ko d'ad'd'an zanin atamfa ne a jikinta da wata t_shirt mai karamin hannu kanta ko d'ankwali babu sai hijab data zurma "Wallahi ba zai ganni a haka ba." a fili tayi wannan maganar la'bewa tayi tana le'kensu inda taga Amina ta iskesu ta tsuguna har 'kasa ta gaishesu, girgiza kai tayi haushi ya turnuketa tana kallon sanda Yake amsawa yana mata dariyarsa mai tsada Sayyada kamar ta kurma ihu! sai cije baki take tana gyada kai tana kallonsu suka nufi cikin gidan tare........Sai bayan taga shigewarsu ne sannan ta fito daga inda ta 'buya. Gidan ta nufa duk ranta babu dadi.
6/6/2020
*BINTA UMAR ABBALE*
_*Littafin Ni da Yaya Sadam! na kudi ne 1_2 #400 ga duk mai bukatar karantawa sai ya tura kudinsa ta wannan accont din......0542382124.......Binta Umar gtbank idan kuma katin waya mutun zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din zan fad'a masa yanda zai biya kud'in....08089965176 _07084653262.....Mutanan Nijar idan kuna bukatar littafin to sai ku tura dala dari ta wannan numbars.....90899076 _88137740 katin airtal ko orange.....Dala dari itace a madadin dari uku na najeria.*_
*NI DA YAYA SADAM!!*
👫👫
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
*🌍MANAZARTA*
*WRITES ASSOCIATION🖊📚*
*M.W.A*
_'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu nazari da aiki da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta._
__________________________________