Sashe 27
Ni Da Yaya Sadam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
" Kai wanene!? da ba za'a fad'a maka magana ba."! shima ya mayar masa a zafafe."!!! "Yaya Sulaiman kayi hakuri don Allah." Murya na rawa take maganar."! "Kika 'kara wata magana anan gurin sai ranki ya 'baci!! wallahi."! Yafad'a yana watsa mata mugun kallo...Mi'kewa tayi tana kuka " Wannan wane irin hali ne? yanzu meye laifin Yaya Sulaiman kuma? kawai don yayi maka addua aikin soja ai ba hauka bane." Bai san sanda ya dirgo daga gadon ba ya nufeta....Sulaiman na ganin abinda yake shirin yi yaje ya tare shi!!! "Karka kuskura ka daketa wannan ai hauka ne! dama dukaninku haka kuke ku kama matanku kuna jibga sai kace bayi."! Wani wawan! naushi ya kir'ba! masa a 'kirji! Sulaiman ya ri'ke kirjinsa yana tari! azabah! na sukanshi.....Gefe ya tureshi yaja tsaki tare da fad'i " Haka sai kace namiji ashe rago ne."!!! Sulaimai ya sake yunkurin kare Sayyada...."Wallahi karka kusantoni sai nayi maka illah! ka bar ganin kirjina daure da bandaji bani da dad'i!!!! Sulaiman ya tsorota da Sadam! domin ga dukkanin alamu allurar ce ta motsa kai Soja bala'i ne.....Sayyada ta makure jikinta a bango Rumfa yayi mata ya sanya hannu ya sha'keta mata wuya"!! Don Ubanki maimaita abunda kikace yanzu, wato kema kin fara daukar hud'ubarsa ko? kina nema ki zagemu ki zagi aikinmu? hakane ko ba haka bane."!? Cikin hargagi yake maganr....Hawaye sai tsere suke a fuskarta "Kayi hakuri don Allah ba zaginka nayi ba."!? " Ni da Sulaiman waye mijinki kuma maganar wa yafi cancanta ki dauka."? da karfin murya yake maganar....Tace"Kaine mijina kuma maganarka yafi dacewa na dauka." "Ok me yasa idan nace karkiyi abu sai kinyi raini ne ko me."!? Girgiza kai tayi..." Kayi hakuri kayi hakuri kayi hakuri."! abinda take fad'a kenan....Wuyanta ya saki ya koma ya kwanta yana wani irin nishi! kirjinsa ya rike! da alama ya fama gurin harbin....
Sulaiman na tsaye yana kallonsa yana nishi!! jini daga jikin bandejin yana fitowa saman kirjinsa, bai wani damu ba ya kad'e rigar jikinsa ya fice daga d'akin zuciyarsa tas yaji dadin yanda ya tashi ciwon nasa shine wahalalle wanda wahala ta yankewa cibiya Allah yasa ma gurin ya lalace ya jima a kwance yana jinya.
Ganin yanda yake rirri'ke kirjinsa da kuma jinin dake zirarowa yasa hankalinta yayi masifar tashi da sauri ta bude kofa ta fita Minti biyar suka shigo da likita hankali a tashe ya isa inda yake ya soma duba gurin mikin yana tambayar Sayyada garin ya akayi haka ta faru ita dai ta kasa cewa komai sai kuka takeyi
Sai da taga jinin dake zuba ya tsaya sannan hankalinta ya kwanta amma dai duk da haka hawaye bai daina zuba daga idonta ba.....Dr ya kalli Sadam! dake rintse ido yana cije lips yace.."Wai Yallabai ya akayi haka ta faru ne."! Ido a rufe yace."Bacci nakeyi na danne gurin." Dr yace."Ayya Madam kina gani a maimakon ki zauna kusa dashi shine amfanin zamanki a gurin ai idan da matsala ko zamu kawo maka mai kula da kai ne."? girgiza kai yayi alamun baya bukata.
Sayyada tace"Tsautsayi ne Dr nima bacci nakeyi shiyasa ban lura ba." Yace."Ai naga alama a yanda kike son Yallabai ba zaki bari hakan ta faru ba sai da dalili." Murmushi tayi mai ciwo tana tuno rashin mutuncin da yayi mata d'azu.
Dr Yace."Idan yayi break ki bashi magani kinji ko." Tace."Insha Allah." Bayan fitar Dr din dakin yayi shiru sai saukar numfashinsu ido ya bude yana kallon inda take tana can takure kan kujera taki kallonsa haushinsa takeji sosai tana da zuciya dole tayi taka tsantsan da rashin mutuncinsa.
Ya jima yana kallonta tausayinta yake ji yanzu kuma nadamar abinda yayi mata yake....Tsaki yayi cikin ransa koma meye ya.faru itace ta jawowa kanta.
Hajiya Fatsima da Alhaji Auwal ne sukayi sallama. Sayyada ta amsa da sakakkiyar fuska tana gaishesu....Hjy Fatsima tayi ta naxarinta taga tabbas akwai damuwa a tare da ita ga idanunta sunyi jawur dasu.....Sadam! ya gaishe da iyayen nasa cikin dauriya da kokarin danne abubuwan dake damunsa Nan Alhaji Auwal yake tambayarsa ko Sulaiman yazo yace."Bai jima da fita ba....Ya tambaye shi yanayin jikin nasa yace."Da sauki bashi da wata matsala...Godiya yayi ga Allah yayi musu sallama kasuwa ya wuce kai tsaye.
Hajiya Fatsima tace"Sayyada ga abun kari nan na kawo muku ki karya sai ki had'awa mijin naki shima." Tace."To Mammah! tea ta had'a me kauri ta zuba soyayyan dankali da kwali ta dauka gadon da yake kwance ta nufa ta zauna gefansa a hankali tace"Ka tashi kayi break kasa magani." Sai da tayi magana sau biyu sannan ya mike zaune da dubara ya kar'bi kofin tea din....Ta mika masa tare da dora masa plate din dankalin a cinyarsa....Da kyar yake daga hannunsa yana kur'bar tea din saboda kafad'arsa ta dama harbin yake, kamar ta kar'ba ta bashi da kanta sai tayi wa kanta fad'a tasan hali zai iya gwaleta ko ya hantareta. mikewa ma tayi ta bar gurin tea ta hada ta zauna kusa da Mamah tana kur'ba amma hankalinta na kansa da kyar ya shanye tea din dankwalin kuwa bai fi uku yaci ba yace."Zo ki dauke plate din nan." Ta mike da sauri ta isa ta dauke masa....Ruwa ta dauko ta dawo gurin ta 'balli maganin ta mi'ka masa kar'ba yayi ya watsa a bakinsa ya kora da ruwa, Hjy Fatsima tana kallonsu cike da farin ciki a gaskiya ta yaba kwarai da yanda Sayyada take kula da Sadam!!!
Bai kai rabin awa da shan maganin ba bacci ya daukeshi....Nan Sayyada da Hjy Suka dinga hira Sayyada ta saki jikinta sosai da ita tana daukarta tamkar mahaifiyarta.
Sai kusan karfe daya sannan tayi niyar tafiya tace zasu dawo da daddare sannan tana komawa gida zata sanya baban gida ya kawo musu abincin rana." Sayyada kamar ta bita saboda abinda yace mata dazu *Banga abinda kike tsinana min ba saboda haka idan su Mamah sunzo dole ki bisu ku tafi gida* Wannan magana ta bata haushi mutuka amma duk sanda ya sakeyi mata irinta to sai dai ya nemeta ya rasa.
Sallah tayi ta koma gefansa ta zauna mifici ta dauka tana masa firfita duk kuwa da cewar akwai fanka a dakin idanunta kurrr gurin ciwon tana mamakin jinin da ya dinga tsiyaya d'azu.
Idanunta taji suna lumshewa alamun bacci na soma ya dauketa dama tasan za'a rina mutukar ta ci bashin bacci to duk inda ya kamata sai tayi take jin dadi.....A hankali ta ra'ba gefansa ta kwanta tana kallon fuskarsa, 'Kare masa kallo take sosai tana gazgata maganar mutane inda suke cewa duk family nasu ya fisu kyau sai dai su nuna masa hasken fata, ita yanzu kalar fatarshi ma burgeta take, ta tsurawa karamin bakinsa ido wanda wani bakin gashi me gazarzar! ya kewaye lebunansa lumshe ido tayi gabanta yana faduwa....Ta sanya hannu a hankali ta shafo kirjinsa! tare dashi suka sauke ajiyar zuciya, cike da tsoro ta zare hannunta gabanta na dukan uku uku!!! Sadam! bai san wainar da take toyawa ba kawai ajiyar zuciyar ce tazo a lokacin......minti biyu ta sake d'ora hannunta kan kirjinsa, Ta lumshe idonta tsigar jikinta sai tashi takeyi......Haka bacci mai nauyi ya dauketa.
Idonsa ya bude a hankali sai ya ganta kwance a gefansa hannunta a kirjinsa ya jima yana kallon hannunta ya kasa daukewa....Gyaran murya yayi tayi saurin bude idonta a firgice ta mike zaune! kauda kansa yayi ya mi'ke zaune itama mikewa tayi ta nufi toilet ta wanke baki ta fito....Tana kallonsa yana kokarin sakkowa daga bed din tana jin tsoron tunkararsa bata son hayaniya da hargagi ta lura shi kuma komai lalura baya fasa halinsa.
Yazo ya wuce ta ya shiga bandakin alwala ya daura bayan ya wanke bakinsa ya fito fuska a daure Sallah ya tayar yana idarwa akayi knocking din kofar...kallonsa tayi ya watsa mata harara! tayi kasa da kanta.....Mikewa yayi yaje ya bude kofar....Baban gida ne da kwandon abinci anan ya dakatar dashi ya karbi kwandon abincin Baban gida ya dubashi yana masa sannu da jiki ya amsa babu wata cikakkiyar walwala kisin Sayyada ne kawai ke sasakar ransa ta riga ta gama nuna masa matsayinsa ta nuna masa tafi kaunar Sulaiman a kansa ba tun yau ba dama ya fahimci akwai wata a 'kasa a tsakaninsu."
Ajiye kwandon abincin yayi bai ce mata komai ba ya haye gadon wayarsa ya dauka yana dubawa.....Ganin lokacin shan maganinsa na nema ya wuce tace"Ko na had'a maka abincin kaci kasha magani." Idab dotse na magana to shima zaiyi ya shareta yana duba waya......Ta'be baki tayi duk yana kallonta ta 'kasan idonsa ya girgiza kai fuskarsa a daure Yace."Ke!!! ba cewa nayi idan Mammah tazo ki bita ba ke wace irin mara zuciya ce ne."!? taji wani sagewar jiki!! da jin abinda ya fad'a ido ta zuba masa tana kallo Cikin shan mur! yace."Da daddare ba sai na sake yi miki magana tana zuwa sahunki a likkafa ki bi bayanta."! Shiru tayi masa bakin ciki na sasakar zuciyarta......Sunanan zaune akayi Nocking din kofar a karo na biyu." Tashi kije ki bud'e."Ya fad'a hankalinsa kan waya, kamar kar ta tashi sai ta mike taje ta bud'e kofar suka had'a ido da ita tana sanye da ingilish wear riga da seket tayi rolling da karamin mayafi fuskar nan taci mai tayi make up kamar hauka ido ta sanya masa gashi sai kace aljannu hannu rike da key na mota da karamar pose Halima 'Yar gidan General AbdulSalam Shugaban sojojin Najera kenan....Wani matsiyacin kallo ta watsa Sayyada ta tsartar mata da yawu" Bani hanya na wuce."!! tafad'i cikin izgili da d'agawa! Sayyada bata san sanda ta kauce daga hanya ba tana kallo ta shige ta barta a tsaye a gurin.
Jingina jikinta tayi a bango tana kallon ikon Allah.....Halima ce ta isa inda yake ta d'ora kanta a gefan kirjinsa tana shashshekar kuka!" Sweetheart abinda ya same ka kenan! wayyo na shiga uku ina can Gombe gurun bikin kawata Captain Saleh ya sanar dani halin da ake ciki me yasa kai baka fad'a min ba." A marairace take maganar." Har yanzu kanta na damtsen hannunsa na hagu......Motsi yayi yana so ya tashi fuskarsa da akwai alamun sassauci yace."Halima abun alkairi shi ake shela ba irin wannan ba dama kin tsaya a inda kike kin gama shagalin bukinki."
Sulaiman na tsaye yana kallonsa yana nishi!! jini daga jikin bandejin yana fitowa saman kirjinsa, bai wani damu ba ya kad'e rigar jikinsa ya fice daga d'akin zuciyarsa tas yaji dadin yanda ya tashi ciwon nasa shine wahalalle wanda wahala ta yankewa cibiya Allah yasa ma gurin ya lalace ya jima a kwance yana jinya.
Ganin yanda yake rirri'ke kirjinsa da kuma jinin dake zirarowa yasa hankalinta yayi masifar tashi da sauri ta bude kofa ta fita Minti biyar suka shigo da likita hankali a tashe ya isa inda yake ya soma duba gurin mikin yana tambayar Sayyada garin ya akayi haka ta faru ita dai ta kasa cewa komai sai kuka takeyi
Sai da taga jinin dake zuba ya tsaya sannan hankalinta ya kwanta amma dai duk da haka hawaye bai daina zuba daga idonta ba.....Dr ya kalli Sadam! dake rintse ido yana cije lips yace.."Wai Yallabai ya akayi haka ta faru ne."! Ido a rufe yace."Bacci nakeyi na danne gurin." Dr yace."Ayya Madam kina gani a maimakon ki zauna kusa dashi shine amfanin zamanki a gurin ai idan da matsala ko zamu kawo maka mai kula da kai ne."? girgiza kai yayi alamun baya bukata.
Sayyada tace"Tsautsayi ne Dr nima bacci nakeyi shiyasa ban lura ba." Yace."Ai naga alama a yanda kike son Yallabai ba zaki bari hakan ta faru ba sai da dalili." Murmushi tayi mai ciwo tana tuno rashin mutuncin da yayi mata d'azu.
Dr Yace."Idan yayi break ki bashi magani kinji ko." Tace."Insha Allah." Bayan fitar Dr din dakin yayi shiru sai saukar numfashinsu ido ya bude yana kallon inda take tana can takure kan kujera taki kallonsa haushinsa takeji sosai tana da zuciya dole tayi taka tsantsan da rashin mutuncinsa.
Ya jima yana kallonta tausayinta yake ji yanzu kuma nadamar abinda yayi mata yake....Tsaki yayi cikin ransa koma meye ya.faru itace ta jawowa kanta.
Hajiya Fatsima da Alhaji Auwal ne sukayi sallama. Sayyada ta amsa da sakakkiyar fuska tana gaishesu....Hjy Fatsima tayi ta naxarinta taga tabbas akwai damuwa a tare da ita ga idanunta sunyi jawur dasu.....Sadam! ya gaishe da iyayen nasa cikin dauriya da kokarin danne abubuwan dake damunsa Nan Alhaji Auwal yake tambayarsa ko Sulaiman yazo yace."Bai jima da fita ba....Ya tambaye shi yanayin jikin nasa yace."Da sauki bashi da wata matsala...Godiya yayi ga Allah yayi musu sallama kasuwa ya wuce kai tsaye.
Hajiya Fatsima tace"Sayyada ga abun kari nan na kawo muku ki karya sai ki had'awa mijin naki shima." Tace."To Mammah! tea ta had'a me kauri ta zuba soyayyan dankali da kwali ta dauka gadon da yake kwance ta nufa ta zauna gefansa a hankali tace"Ka tashi kayi break kasa magani." Sai da tayi magana sau biyu sannan ya mike zaune da dubara ya kar'bi kofin tea din....Ta mika masa tare da dora masa plate din dankalin a cinyarsa....Da kyar yake daga hannunsa yana kur'bar tea din saboda kafad'arsa ta dama harbin yake, kamar ta kar'ba ta bashi da kanta sai tayi wa kanta fad'a tasan hali zai iya gwaleta ko ya hantareta. mikewa ma tayi ta bar gurin tea ta hada ta zauna kusa da Mamah tana kur'ba amma hankalinta na kansa da kyar ya shanye tea din dankwalin kuwa bai fi uku yaci ba yace."Zo ki dauke plate din nan." Ta mike da sauri ta isa ta dauke masa....Ruwa ta dauko ta dawo gurin ta 'balli maganin ta mi'ka masa kar'ba yayi ya watsa a bakinsa ya kora da ruwa, Hjy Fatsima tana kallonsu cike da farin ciki a gaskiya ta yaba kwarai da yanda Sayyada take kula da Sadam!!!
Bai kai rabin awa da shan maganin ba bacci ya daukeshi....Nan Sayyada da Hjy Suka dinga hira Sayyada ta saki jikinta sosai da ita tana daukarta tamkar mahaifiyarta.
Sai kusan karfe daya sannan tayi niyar tafiya tace zasu dawo da daddare sannan tana komawa gida zata sanya baban gida ya kawo musu abincin rana." Sayyada kamar ta bita saboda abinda yace mata dazu *Banga abinda kike tsinana min ba saboda haka idan su Mamah sunzo dole ki bisu ku tafi gida* Wannan magana ta bata haushi mutuka amma duk sanda ya sakeyi mata irinta to sai dai ya nemeta ya rasa.
Sallah tayi ta koma gefansa ta zauna mifici ta dauka tana masa firfita duk kuwa da cewar akwai fanka a dakin idanunta kurrr gurin ciwon tana mamakin jinin da ya dinga tsiyaya d'azu.
Idanunta taji suna lumshewa alamun bacci na soma ya dauketa dama tasan za'a rina mutukar ta ci bashin bacci to duk inda ya kamata sai tayi take jin dadi.....A hankali ta ra'ba gefansa ta kwanta tana kallon fuskarsa, 'Kare masa kallo take sosai tana gazgata maganar mutane inda suke cewa duk family nasu ya fisu kyau sai dai su nuna masa hasken fata, ita yanzu kalar fatarshi ma burgeta take, ta tsurawa karamin bakinsa ido wanda wani bakin gashi me gazarzar! ya kewaye lebunansa lumshe ido tayi gabanta yana faduwa....Ta sanya hannu a hankali ta shafo kirjinsa! tare dashi suka sauke ajiyar zuciya, cike da tsoro ta zare hannunta gabanta na dukan uku uku!!! Sadam! bai san wainar da take toyawa ba kawai ajiyar zuciyar ce tazo a lokacin......minti biyu ta sake d'ora hannunta kan kirjinsa, Ta lumshe idonta tsigar jikinta sai tashi takeyi......Haka bacci mai nauyi ya dauketa.
Idonsa ya bude a hankali sai ya ganta kwance a gefansa hannunta a kirjinsa ya jima yana kallon hannunta ya kasa daukewa....Gyaran murya yayi tayi saurin bude idonta a firgice ta mike zaune! kauda kansa yayi ya mi'ke zaune itama mikewa tayi ta nufi toilet ta wanke baki ta fito....Tana kallonsa yana kokarin sakkowa daga bed din tana jin tsoron tunkararsa bata son hayaniya da hargagi ta lura shi kuma komai lalura baya fasa halinsa.
Yazo ya wuce ta ya shiga bandakin alwala ya daura bayan ya wanke bakinsa ya fito fuska a daure Sallah ya tayar yana idarwa akayi knocking din kofar...kallonsa tayi ya watsa mata harara! tayi kasa da kanta.....Mikewa yayi yaje ya bude kofar....Baban gida ne da kwandon abinci anan ya dakatar dashi ya karbi kwandon abincin Baban gida ya dubashi yana masa sannu da jiki ya amsa babu wata cikakkiyar walwala kisin Sayyada ne kawai ke sasakar ransa ta riga ta gama nuna masa matsayinsa ta nuna masa tafi kaunar Sulaiman a kansa ba tun yau ba dama ya fahimci akwai wata a 'kasa a tsakaninsu."
Ajiye kwandon abincin yayi bai ce mata komai ba ya haye gadon wayarsa ya dauka yana dubawa.....Ganin lokacin shan maganinsa na nema ya wuce tace"Ko na had'a maka abincin kaci kasha magani." Idab dotse na magana to shima zaiyi ya shareta yana duba waya......Ta'be baki tayi duk yana kallonta ta 'kasan idonsa ya girgiza kai fuskarsa a daure Yace."Ke!!! ba cewa nayi idan Mammah tazo ki bita ba ke wace irin mara zuciya ce ne."!? taji wani sagewar jiki!! da jin abinda ya fad'a ido ta zuba masa tana kallo Cikin shan mur! yace."Da daddare ba sai na sake yi miki magana tana zuwa sahunki a likkafa ki bi bayanta."! Shiru tayi masa bakin ciki na sasakar zuciyarta......Sunanan zaune akayi Nocking din kofar a karo na biyu." Tashi kije ki bud'e."Ya fad'a hankalinsa kan waya, kamar kar ta tashi sai ta mike taje ta bud'e kofar suka had'a ido da ita tana sanye da ingilish wear riga da seket tayi rolling da karamin mayafi fuskar nan taci mai tayi make up kamar hauka ido ta sanya masa gashi sai kace aljannu hannu rike da key na mota da karamar pose Halima 'Yar gidan General AbdulSalam Shugaban sojojin Najera kenan....Wani matsiyacin kallo ta watsa Sayyada ta tsartar mata da yawu" Bani hanya na wuce."!! tafad'i cikin izgili da d'agawa! Sayyada bata san sanda ta kauce daga hanya ba tana kallo ta shige ta barta a tsaye a gurin.
Jingina jikinta tayi a bango tana kallon ikon Allah.....Halima ce ta isa inda yake ta d'ora kanta a gefan kirjinsa tana shashshekar kuka!" Sweetheart abinda ya same ka kenan! wayyo na shiga uku ina can Gombe gurun bikin kawata Captain Saleh ya sanar dani halin da ake ciki me yasa kai baka fad'a min ba." A marairace take maganar." Har yanzu kanta na damtsen hannunsa na hagu......Motsi yayi yana so ya tashi fuskarsa da akwai alamun sassauci yace."Halima abun alkairi shi ake shela ba irin wannan ba dama kin tsaya a inda kike kin gama shagalin bukinki."