Sashe 16
Ni Da Yaya Sadam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*Free Pege 13*
Cike da farin ciki Baba Marka take fad'in"Sannuku da zuwa sannu kunsha hanya ashe dai angon nawa yana tafe da har ina cewa zanzo biko ashe dai ana sane dani." Tabarma ta shimfida musu suka zauna Captain Habu sai murmushi yakeyi karamcin matar ke bashi sha'awa gaisawa sukayi a mutunce tana tambayar mutanan gida Sadam! ya kalli 'kofar dakin Baba Ladidi yace."Ina sauran mutanan gidan suke."!? Baba Marka tace"Baba Ladidi dai bata dad'e da fita kasuwa ba ita kuma Sayyada yanzu yanzu na aika kiranta tana gidan Kawarta Mariya." Ta kalli Amina dake tsaye tace"Ina Sayyadar."? Amina tace"Tana kan hanya." Kafin Baba Marka tace wani abu Sayyada ta shigo bakinta dauke da sallama.
Baba Marka tace"Yawwa gatanan ma." Sayyada ta karaso inda suke fuska babu yabo babu fallasa take gaishe su, Sadam! ya kalleta yana wani ya mutsa fuska sam! bai amsa gaisuwar ta ba Captain Habu ne ya amsa da fara'a a fuskarsa Sadam yaji takaicin yanda Habu yaga sayyada kaca-kaca duk da cewar bai tabbatar da cewar itace ba.
Dakin Baba Ladidi ta shiga ta cire kayan jikinta dogon hijab ta sanya har kasa ta fito kai tsaye bakin rijiya ta nufa ta jawo ruwa cikin rijiya bandaki ta nufa tayi wanka tana fitowa idanunsu suka game da juna yayi saurin kauda kansa yana kur'bar damammiyar furar da Baba Marka ta damo musu
Baba Ladidi ce tayi sallama ta shigo hannunta rike da wani buhu mayafi a saman ka tace"Ai tunda na doso bakin layi na hango motar sojoji a kafe nace to Soja yazo ganin amaryar tasa." Ta karashe maganar tana dariya hade da kokarin aje buhun a gefe ta cire mayafin dake saman kanta tana fad'in"Ai fa wannan ranar dama nasan dole ne ta tambaye ni." Baba Marka tace"Ai sai da na fad'a miki cewar ki bari ranar tayi sanyi in yaso sai ki tafi."
Ya d'ago kansa a nutse yana kallonta yace."Wai shin ma ina taje da wannan ranar."!? Baba Marka tace"Haba kaiko sai kace wani kurma kana ji fa nace kasuwa ta tafi."
Ya kalli Baba Ladidi dake firfita da mafici yace."Baba ashe dai baki fasa yawon kasuwar nan ba ko."!?
"Oo! ni ba abinda kake tunani ne ya kaini kasuwa ba ato tawa ce ta kaini ta wani gefan kuma sai in ce ta dalilin ka na shiga kasuwar."
Ta'be bakinsa yayi ya mayar da kansa 'kasa Baba Ladidi ta washe baki tana kallon captain Habu tace"Ashe tare kake da ba'ko sannu da zuwa samari ya mutan gida da fatan duk sunannan lafiya ko."?
Captain Habu yace."Kowa lafiya lau ai sunce ma a gaisheku da kyau."!
Baba Ladidi tace" Alhamdullhi ." Sai ta fara zazzage abinda ke cikin buhun tana dubawa tace"Kinga na samo saiwowin maganin nan da duk abinda ake bukata saboda haka yanzu yanzu zan sanya 'Dantani ya yanka min kazar."
Baba Marka tace"Hakan yayi sai ya had'a da Zabi gudu uku ya yankawa ba'ki ayi musu miya ko."!?
Tace"Kwarai kuwa kinga kuwa naga kayan miya masu kyau a kasuwa wallahi wannan ranar da ake kwalawa itace ta hanani na tsaya na siyo."
"Aifa! gwara da kika nufo gida a aika Dantani ya siyo yanzu." Baba Marka tafada tana kokarin mikewa mayafi ta dauko jikin kyauran dakinta ta yafa ta fito tana fad'in"Bari in kira Dantani d'in nasan dai yanzu ya dawo cin abinci daga gurin sana'arshi."
Har ta kai kofar fita Baba Ladidi tace"Wai Ina Sayyada ne? ko bata dawo daga gidan kawar tata ba."
Marka tace"Shigowarki ta shiga daki tana ciki tana jinki." Labule ta d'aga ta fito
Tana sanye da riga da siket na atamfa soso tayi wata irin kwalliya ta d'ige-d'ige a da kwalli kumatunta da saman goshinta sai le'banta data mulke shi da jan janbaki fuskar nan jazur da jar hoda abinka da farar fata. kanta babu dankwali sai ubangashi data daure shi a tsakiyar kai yana reto ga wani uban kyalli da yake saboda man data lafta masa
Sadam! na ganinta ta fito a haka ransa ya 'baci indai ba idonsa ne ke masa gizo ba har cibiyar ta sai da ya hango lokacin da take kokarin zama kusa da Baba dake rigar karama ce sannan hannunta me fad'i ne wanda tana d'agawa za'a iya ganin hamtarta Gashi kanta babu dankwali duk ta fito da surar jikinta, Rai a 'bace ya daka tsawa tare da fad'in"Maza ki tashi ki sanjo kaya wannan ai sun matse ki sannan dake ke mara hankali ce kin fito babu dankwali wai ke kinyi ado."
Cikin jin haushi ta watsa masa harara! ta dauke kanta tana zumbura baki.
Baba Ladidi tace"Dad'ina da kai kenan kai ba'ayi maka gwaninta a maimakon ka yaba da kwalliyar da tayi maka sai ka kushe hakan bai dace ba." Ta kalli Captain Habu tace"Don Allah ka dinga bawa abokinka shawara ya rage fad'a! da jarabar masifa yarinyar nan dai marainiya ce."
Captain Habu yayi dariya yana d'an kallon Sayyada ta 'kasan Ido gaskiya abokinsa yayi dace da mace nan gaba kad'an yasan yarinyar zata zama cikakkiyar mace.
Yace."Muma can gurin aikin haka muke fama dashi Baba Sadam! din ne ai ya cika zafi shiyasa ko a filin daga! ba'a cin galaba a kanmu."!
Baba Ladidi tayi dariya tana fad'in"Ai filin ya'ki daban damu da iyalinsa bana so a daura aure yazo ya tsawalawa yarinyar mutane."
Captain Habu yace."Karkiji komai Baba insha Allahu zamu rike Sayyada da kyau da kulawa." Baba tace"To nagode Mai gidana na kaina."!
Mikewa tayi ta shige d'aki Sayyada ta sunkuyar da kanta kasa tana wasa da 'yan ya tsunta na hannu Sadam! sai dalla! mata harara yake yana ya mutsa fuska. Shi ko Captain Habu sai janta yake da wasa tana murmushi.
Tsaki yayi yace"Wai don Allah Captain me ka hango naso a jikin wannan yarinyar ne? dube ta da kyau ka gani in banda iyaye iyayene Allah da ba zan takurawa kaina ba Duk tsiya nasan Halima ta fita komai da komai."!!!
Sayyada ta d'ago kai ta kalleshi ranta ya 'baci idanunta suka kawo ruwa wacece kuma Halima? Captain Habu ya 'bata fuska yana fad'in"Aboki meye haka wannan ai cin fuska ne." Sadam! ya kauda kansa gefe waya ya ciro yana dubawa
"Kiyi hakuri kinji amarya." Captain Habu ya fada da kokarin ganin ta saki fuskarta, Kallonsa tayi tace"Abokinka yace bai ga abinso a tare dani ba Allah yasa bashi kad'ai gareni ba ko yanzu yace baya so akwai dubanninsa masu so saboda haka nima ba wai sonsa nake ba Umarnin magabatana kawai nake bi." Tana gama maganarta ta mike ta shige daki hijab ta zura ta fito Baba Na daki tana fad'in"Sayyada kar ki fita ina zakije dawo ki shanye maganin nan na dama miki kar ki fita fa."
"Baba nifa na tafi gidan su Ummi domin ba zan zauna a cikin gidan nan ba mutukar yana cikinsa sai ya tafi na dawo." Tana gama maganarta ta fuce daga gidan cikin bakin ciki da takaici, tana daf da fita babban soro suka ci karo da Amina hannunta rike da wata leda da alama daga shagon Magaji take lemon kwalba ne fenta da mirinda ta siyi da sanyi 'kara-'kara!! Sayyada ta tare mata hanya rai a 'bace tace"Dama neman ki nake.
Amina tace"Menene kuma."!? Sayyada ta rike 'kugu tana fad'in"Tambaya ta ma kike menene lallai ma Amina! dan kutumar ubanki wannan lemon ubanwa kika siyowa? Amina tace"Kar dai ki sake ki zageni Sayyada lemo kuma babu ruwanki da wanda na siyowa! Wallahi sai naji Uban da kika siyowa lemo sannan me zakiyi idan na zage ki." ? Amina tayi murmushi tana kokarin ratse ta ta wuce tace"Ni dai ba karya bace da zan zauna ina haus........Ai kafin ta 'karisa Sayyada ta buga tsalle ta kaud'a mata mari! "Nice karya dan babanki." Sai ta wafce ledar hannunta a take kwalbar lemukan suka fashe lemon ya zube a kasan gurin......Kwalbar lemon da ta fashe ta d'auka tayi kan Amina tana huci! wallahi sai nayi miki zane a fuskarki ni zaki kira karya ki shiga gonata ki kirani karya lallai Amina kin ta'bowa kanki bala'i! Amina da taga Sayyada na nema ta lahanta ta sai ta fara neman hanyar tserewa Sayyada ta jawo hijab dinta wanda gari jawo hijab din ta taka karamar kwalba a take ta huda mata kafa amma ko a jikinta kokari kawai take tayiwa Amina zane a fuska.....Ihu! Amina take tana fad'in "Wai Sayyada ke mahaukaciyar ina ce ne? me nayi miki.? A fusace tace" Mahaukaciyar gidaj Ubank....Kafin ta karasa taji saukar mari a fuskarta Yana tsaye ransa a 'bace yace"Sakar mata hijab." Sai ta rushe da kuka tana fad'in"Ai kamata yayi kafin ka yanke hukunci ka tambayi ba'asi kawai sai ka mareni alhalin itace da rashin gaskiya." Hararta yayi yace"Ban tambaye ki komai ba saketa ki wuce cikin gida." Sayyada ta sakar mata hijab Ya kalli Amina dake motsa baki yace."Ke Amina meye ya had'aku."? "Wallahi Yaya Sadam! ban san abinda nayi mata ba kawai karo mukaci tazo fita ni kuma zan shigo naje shagon Magaji na siyo muku lemo shine fa ta tareni da kokawa tana zagina."
Ya kalli Sayyada rai a bace! zai hau surfa bala'i Captain Habu yace."A'a ba haka ake ba ai kaji magana daga bakin Amina itama sai ka fara jin ta bakinta haka ake hukunci."
Hararasa yayi yace."Baka san halin wannan yarinyar bane Habu Sayyada batajin magana wallahi nasan itace da tsokana." Captain habu yace."Eh duk da haka dai kaji ta bakinta."
Ya jiyo da hankalinsa kanta ganin jinin dake fita daga hannunta yasa jikinsa yin sanyi ya kura mata ido a hankali yace."Meye ya had'aku?"
"Itace take cewa dani Karya shine nace sai ta fad'a min inda nayi karuwanci tunda dai ni nasan karuwa kawai ake kira da wannan kalmar."
Sadam! yaji takaicin wannan kalmar ta Karya ya kalli Amina da jan ido yace."Amina da hankalinki kike kiran 'yar uwarki da wannan kalmar."!? Amina tayi rau!rau! da ido tace"Wallahi zuciya ce ta ciyo ni kuma Sayyada ta dad'e tana min abubuwa shiyasa ban san sanda na kirata da wannan suna ba."
Yace."To daga yau sai yau kar ki sake kiranta da wannan kalmar kinji ko." Tace."To insha Allahu."
Cike da farin ciki Baba Marka take fad'in"Sannuku da zuwa sannu kunsha hanya ashe dai angon nawa yana tafe da har ina cewa zanzo biko ashe dai ana sane dani." Tabarma ta shimfida musu suka zauna Captain Habu sai murmushi yakeyi karamcin matar ke bashi sha'awa gaisawa sukayi a mutunce tana tambayar mutanan gida Sadam! ya kalli 'kofar dakin Baba Ladidi yace."Ina sauran mutanan gidan suke."!? Baba Marka tace"Baba Ladidi dai bata dad'e da fita kasuwa ba ita kuma Sayyada yanzu yanzu na aika kiranta tana gidan Kawarta Mariya." Ta kalli Amina dake tsaye tace"Ina Sayyadar."? Amina tace"Tana kan hanya." Kafin Baba Marka tace wani abu Sayyada ta shigo bakinta dauke da sallama.
Baba Marka tace"Yawwa gatanan ma." Sayyada ta karaso inda suke fuska babu yabo babu fallasa take gaishe su, Sadam! ya kalleta yana wani ya mutsa fuska sam! bai amsa gaisuwar ta ba Captain Habu ne ya amsa da fara'a a fuskarsa Sadam yaji takaicin yanda Habu yaga sayyada kaca-kaca duk da cewar bai tabbatar da cewar itace ba.
Dakin Baba Ladidi ta shiga ta cire kayan jikinta dogon hijab ta sanya har kasa ta fito kai tsaye bakin rijiya ta nufa ta jawo ruwa cikin rijiya bandaki ta nufa tayi wanka tana fitowa idanunsu suka game da juna yayi saurin kauda kansa yana kur'bar damammiyar furar da Baba Marka ta damo musu
Baba Ladidi ce tayi sallama ta shigo hannunta rike da wani buhu mayafi a saman ka tace"Ai tunda na doso bakin layi na hango motar sojoji a kafe nace to Soja yazo ganin amaryar tasa." Ta karashe maganar tana dariya hade da kokarin aje buhun a gefe ta cire mayafin dake saman kanta tana fad'in"Ai fa wannan ranar dama nasan dole ne ta tambaye ni." Baba Marka tace"Ai sai da na fad'a miki cewar ki bari ranar tayi sanyi in yaso sai ki tafi."
Ya d'ago kansa a nutse yana kallonta yace."Wai shin ma ina taje da wannan ranar."!? Baba Marka tace"Haba kaiko sai kace wani kurma kana ji fa nace kasuwa ta tafi."
Ya kalli Baba Ladidi dake firfita da mafici yace."Baba ashe dai baki fasa yawon kasuwar nan ba ko."!?
"Oo! ni ba abinda kake tunani ne ya kaini kasuwa ba ato tawa ce ta kaini ta wani gefan kuma sai in ce ta dalilin ka na shiga kasuwar."
Ta'be bakinsa yayi ya mayar da kansa 'kasa Baba Ladidi ta washe baki tana kallon captain Habu tace"Ashe tare kake da ba'ko sannu da zuwa samari ya mutan gida da fatan duk sunannan lafiya ko."?
Captain Habu yace."Kowa lafiya lau ai sunce ma a gaisheku da kyau."!
Baba Ladidi tace" Alhamdullhi ." Sai ta fara zazzage abinda ke cikin buhun tana dubawa tace"Kinga na samo saiwowin maganin nan da duk abinda ake bukata saboda haka yanzu yanzu zan sanya 'Dantani ya yanka min kazar."
Baba Marka tace"Hakan yayi sai ya had'a da Zabi gudu uku ya yankawa ba'ki ayi musu miya ko."!?
Tace"Kwarai kuwa kinga kuwa naga kayan miya masu kyau a kasuwa wallahi wannan ranar da ake kwalawa itace ta hanani na tsaya na siyo."
"Aifa! gwara da kika nufo gida a aika Dantani ya siyo yanzu." Baba Marka tafada tana kokarin mikewa mayafi ta dauko jikin kyauran dakinta ta yafa ta fito tana fad'in"Bari in kira Dantani d'in nasan dai yanzu ya dawo cin abinci daga gurin sana'arshi."
Har ta kai kofar fita Baba Ladidi tace"Wai Ina Sayyada ne? ko bata dawo daga gidan kawar tata ba."
Marka tace"Shigowarki ta shiga daki tana ciki tana jinki." Labule ta d'aga ta fito
Tana sanye da riga da siket na atamfa soso tayi wata irin kwalliya ta d'ige-d'ige a da kwalli kumatunta da saman goshinta sai le'banta data mulke shi da jan janbaki fuskar nan jazur da jar hoda abinka da farar fata. kanta babu dankwali sai ubangashi data daure shi a tsakiyar kai yana reto ga wani uban kyalli da yake saboda man data lafta masa
Sadam! na ganinta ta fito a haka ransa ya 'baci indai ba idonsa ne ke masa gizo ba har cibiyar ta sai da ya hango lokacin da take kokarin zama kusa da Baba dake rigar karama ce sannan hannunta me fad'i ne wanda tana d'agawa za'a iya ganin hamtarta Gashi kanta babu dankwali duk ta fito da surar jikinta, Rai a 'bace ya daka tsawa tare da fad'in"Maza ki tashi ki sanjo kaya wannan ai sun matse ki sannan dake ke mara hankali ce kin fito babu dankwali wai ke kinyi ado."
Cikin jin haushi ta watsa masa harara! ta dauke kanta tana zumbura baki.
Baba Ladidi tace"Dad'ina da kai kenan kai ba'ayi maka gwaninta a maimakon ka yaba da kwalliyar da tayi maka sai ka kushe hakan bai dace ba." Ta kalli Captain Habu tace"Don Allah ka dinga bawa abokinka shawara ya rage fad'a! da jarabar masifa yarinyar nan dai marainiya ce."
Captain Habu yayi dariya yana d'an kallon Sayyada ta 'kasan Ido gaskiya abokinsa yayi dace da mace nan gaba kad'an yasan yarinyar zata zama cikakkiyar mace.
Yace."Muma can gurin aikin haka muke fama dashi Baba Sadam! din ne ai ya cika zafi shiyasa ko a filin daga! ba'a cin galaba a kanmu."!
Baba Ladidi tayi dariya tana fad'in"Ai filin ya'ki daban damu da iyalinsa bana so a daura aure yazo ya tsawalawa yarinyar mutane."
Captain Habu yace."Karkiji komai Baba insha Allahu zamu rike Sayyada da kyau da kulawa." Baba tace"To nagode Mai gidana na kaina."!
Mikewa tayi ta shige d'aki Sayyada ta sunkuyar da kanta kasa tana wasa da 'yan ya tsunta na hannu Sadam! sai dalla! mata harara yake yana ya mutsa fuska. Shi ko Captain Habu sai janta yake da wasa tana murmushi.
Tsaki yayi yace"Wai don Allah Captain me ka hango naso a jikin wannan yarinyar ne? dube ta da kyau ka gani in banda iyaye iyayene Allah da ba zan takurawa kaina ba Duk tsiya nasan Halima ta fita komai da komai."!!!
Sayyada ta d'ago kai ta kalleshi ranta ya 'baci idanunta suka kawo ruwa wacece kuma Halima? Captain Habu ya 'bata fuska yana fad'in"Aboki meye haka wannan ai cin fuska ne." Sadam! ya kauda kansa gefe waya ya ciro yana dubawa
"Kiyi hakuri kinji amarya." Captain Habu ya fada da kokarin ganin ta saki fuskarta, Kallonsa tayi tace"Abokinka yace bai ga abinso a tare dani ba Allah yasa bashi kad'ai gareni ba ko yanzu yace baya so akwai dubanninsa masu so saboda haka nima ba wai sonsa nake ba Umarnin magabatana kawai nake bi." Tana gama maganarta ta mike ta shige daki hijab ta zura ta fito Baba Na daki tana fad'in"Sayyada kar ki fita ina zakije dawo ki shanye maganin nan na dama miki kar ki fita fa."
"Baba nifa na tafi gidan su Ummi domin ba zan zauna a cikin gidan nan ba mutukar yana cikinsa sai ya tafi na dawo." Tana gama maganarta ta fuce daga gidan cikin bakin ciki da takaici, tana daf da fita babban soro suka ci karo da Amina hannunta rike da wata leda da alama daga shagon Magaji take lemon kwalba ne fenta da mirinda ta siyi da sanyi 'kara-'kara!! Sayyada ta tare mata hanya rai a 'bace tace"Dama neman ki nake.
Amina tace"Menene kuma."!? Sayyada ta rike 'kugu tana fad'in"Tambaya ta ma kike menene lallai ma Amina! dan kutumar ubanki wannan lemon ubanwa kika siyowa? Amina tace"Kar dai ki sake ki zageni Sayyada lemo kuma babu ruwanki da wanda na siyowa! Wallahi sai naji Uban da kika siyowa lemo sannan me zakiyi idan na zage ki." ? Amina tayi murmushi tana kokarin ratse ta ta wuce tace"Ni dai ba karya bace da zan zauna ina haus........Ai kafin ta 'karisa Sayyada ta buga tsalle ta kaud'a mata mari! "Nice karya dan babanki." Sai ta wafce ledar hannunta a take kwalbar lemukan suka fashe lemon ya zube a kasan gurin......Kwalbar lemon da ta fashe ta d'auka tayi kan Amina tana huci! wallahi sai nayi miki zane a fuskarki ni zaki kira karya ki shiga gonata ki kirani karya lallai Amina kin ta'bowa kanki bala'i! Amina da taga Sayyada na nema ta lahanta ta sai ta fara neman hanyar tserewa Sayyada ta jawo hijab dinta wanda gari jawo hijab din ta taka karamar kwalba a take ta huda mata kafa amma ko a jikinta kokari kawai take tayiwa Amina zane a fuska.....Ihu! Amina take tana fad'in "Wai Sayyada ke mahaukaciyar ina ce ne? me nayi miki.? A fusace tace" Mahaukaciyar gidaj Ubank....Kafin ta karasa taji saukar mari a fuskarta Yana tsaye ransa a 'bace yace"Sakar mata hijab." Sai ta rushe da kuka tana fad'in"Ai kamata yayi kafin ka yanke hukunci ka tambayi ba'asi kawai sai ka mareni alhalin itace da rashin gaskiya." Hararta yayi yace"Ban tambaye ki komai ba saketa ki wuce cikin gida." Sayyada ta sakar mata hijab Ya kalli Amina dake motsa baki yace."Ke Amina meye ya had'aku."? "Wallahi Yaya Sadam! ban san abinda nayi mata ba kawai karo mukaci tazo fita ni kuma zan shigo naje shagon Magaji na siyo muku lemo shine fa ta tareni da kokawa tana zagina."
Ya kalli Sayyada rai a bace! zai hau surfa bala'i Captain Habu yace."A'a ba haka ake ba ai kaji magana daga bakin Amina itama sai ka fara jin ta bakinta haka ake hukunci."
Hararasa yayi yace."Baka san halin wannan yarinyar bane Habu Sayyada batajin magana wallahi nasan itace da tsokana." Captain habu yace."Eh duk da haka dai kaji ta bakinta."
Ya jiyo da hankalinsa kanta ganin jinin dake fita daga hannunta yasa jikinsa yin sanyi ya kura mata ido a hankali yace."Meye ya had'aku?"
"Itace take cewa dani Karya shine nace sai ta fad'a min inda nayi karuwanci tunda dai ni nasan karuwa kawai ake kira da wannan kalmar."
Sadam! yaji takaicin wannan kalmar ta Karya ya kalli Amina da jan ido yace."Amina da hankalinki kike kiran 'yar uwarki da wannan kalmar."!? Amina tayi rau!rau! da ido tace"Wallahi zuciya ce ta ciyo ni kuma Sayyada ta dad'e tana min abubuwa shiyasa ban san sanda na kirata da wannan suna ba."
Yace."To daga yau sai yau kar ki sake kiranta da wannan kalmar kinji ko." Tace."To insha Allahu."