Sashe 25
Ni Da Yaya Sadam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Rundinar sojoji ta Najeria tayi mutukar jin dadi da faruwar wannan al'amari tabbas sun dad'e suna so su kama koda d'aya ne daga cikin wad'anan mutane domin su kafa hojjoji kana kuma su tsaurara bunkice akansa domin ya sanar musu inda sauran 'yan uwansa suke.....Saboda haka hatta da mataimakin shugaban 'kasa sai da yazo ya duba Sadam! kuma ya jinjina masa a bisa namjin kokarin da yayi....Sannan ya sanar dashi sakon mai girma President yace."Yana gaishe shi da kyau kuma yana jinjina masa hakika ya cika gwarzon maza.......Wannan al'amari yayi masifar 'batawa 'yan adawa rai mussaman Captain Saleh wanda shine mutumin da ya rufe kwatar da silaf din duk dan kar ya samu hanyar fitowa, Sadam! na da ma'kiya a gurin aiki sosai da sosai don wasu ma basu zo duba shi ba sai kananun maganganu ne ke tashi.......A can 'bangaran gida kuma tun misalin karfe takwas na dare suke kiran wayar shi sai dai Captain Habu ya dauka yace."Baya kusa Hjy Fatsima data gaji sai tace Ya fada mata gaskiya idan wani abun ne ya faru Captain Habu ya boye mata....Tun sannan suka sha jinjin jikinsu Sayyada kuka ta hau yi! Hajiya Fatsima ke rarrashinta da ta kwantar da hankalinta babu abinda ya faru.....Alhaji Auwal na kasuwa labai ya riske shi cewar sojoji sunyi nasarar kama dan boko haram! cikin kasuwar bacci amma kuma daya daga cikinsu ya jikkata domin dan boko haram din yayi nasarar harbinsa a kafada.....Ba tsaya wasa ba ya nemi numbar d'an sa to shima dai captain habu ne ya dauka nan yake tambayarshi ya ake ciki Captain Habu yace babu wata matsala insha Allah ya nemi da ya bashi Sadam! din sai ya hau kame kame! kashe wayar kawai yayi ya nufi gida....Yana isa ya tarar dasu cikin tashin hankali da damuwa domin suna zaune suna kallon labarai tashar Bbc news suka nuna Sadam! din akwance kirjinsa daure da bandeji yana jawabi da yanda abun ya faru.........Duk suka tashi hankalinsu Sayyada sai kuka takeyi sai an kaita gurinsa, Sulaiman ne ke rarrashinsa idan ka ganshi sai ka dauka ya damu da al'amarin amma a cikin ransa dad'i yake ji sosai yaso Sadam din ya she'ke barzahu sai ya samu damar auran matarshi Sayyada.
Hajiya Fatsima ta sako hijab suka nufi barikin sojojin domin duba halin da d'ansu yake ciki.....Ganinsa zaune yana shan yoght sai hankalinsa ya kwanta Captain Habu ya gaisa dasu Hajiya Fatsima tace"Ka kyauta wato shine ka'ki yi min bayani abinda ya faru sai a tv na gani."
Yace."Mamah ai abun alkairi ake fad'a shiyasa ban sanar daku komai nasan da na fada miki a lokacin zakice zaku zo to ganinsa a wannan lokacin zai d'aga muku hankali shiyasa muka bari sai da aka gama komai tukkuna."
Alhaji Auwal yace."Alhamdullahi ai da sauki ma al'amarin Allah ya kare ku ya kare ya kuma baku nasara a duk inda zaku shiga." Captain Habu ya amsa da ameen kana ya fita ya barsu domin su gana.
Sayyada gefansa ta zauna tana ta kallon kirjinsa inda aka harbe shi tsigar jikinta sai tashi takeyi hawaye kuwa wannan na bin wannan...Sulaiman ya gyada kai ba tare da yace wa dan uwan nasa komai ba ya fice daga dakin ya tsani yaga Sayyada na kusantar inda Sadam! yake. Motarsa ya shiga ya bar barikin sojojin.....A nutse ya gaisa da iyayen nasa yana musu 'karin bayanin kan yanda al'amarin ya faru...Hajiya Fatsima sai da tayi kuka tace"Ni kuwa Da zaka bi shawara ta to da ka ajiye aikin nan Sadam! akwai had'ari a cikinsa." A take ya 'bata fuska yace."Mammah bana son kina irin wannan magana wallahi! tunda na fara wannan aiki bana fata in aje kuma wallahi wallahi wallahi bana yi domin kudi ko wata daukaka ko mukami inayi ne kawai saboda 'kasata Nejaria sannan inayi ne domin taimakon al'umma addua kawai nake bukata a gurunku." Tace"Shikkenan Sadam! Ubangiji Allah ya shige maka gaba Allah ya kare ku a duk inda kuke ya tsare gabanku da bayanku." Suka amsa da "ameen." dukaninsu.......To koda suka tashi tafiya Sayyada ta'ki binsu akayi akayi ta'ki sai ma ta haye kan gadon ta 'buya a bayansa .Alhji Awal yace."A kyaleta ta zauna Sadam! bai so haka saboda abokanan aikinsa na shigowa duba shi to dan ba yanda zaiyi yasa ya hakura suka tafi suka barta.
To a cikin mota iyayen maganar suke inda Hajiya Fatsima take cewa''Ni kuwa rashin jituwar Sadam da Sulaiman na bani tsoro Alhaji yara kamar ba 'yan uwa ba ka duba ka gani Sulaiman ne ya dace ya zauna yayi jinyar dan uwansa amma ka lura ko minti biyar baiyi ba ya fita kuma bai ce masa sannu ba wannan al'amari ya 'bata min rai kuma babu babban mai laifi sai Sulaiman din tunda dai shine babba."
Alhaji Auwal yana draving yace."Kin san Sulaiman akwai sabga mybe kiransa akayi a waya shiyasa kika ga ya fita bai zauna ba amma na tabbatar zai koma ya duba shi bana so ki sanya wani abu a cikin ranki."
Tace."Wallahi al'amarin ke bani mamaki shiyasa nake magana Allah ya dai-dai ta tsakaninsu." Ya amsa da ''ameeen ya rabbi."!
***
Kallonta yake itama tana kallonsa idanunta yayi fululu saboda kuka babu yabo babu fallasa yace."Ya kamata ki daina wannan kukan ya isa haka."
Ta goge hawayen fuska mirya a dashe tace."Tausayinka nakeji don girman Allah ka daina wannan aikin kaji."
Shan kunu yayi yace."Ke! bana son shirme! Wannan aikin idan kinga na bari to bana nuffashi."
Hawaye ya sake kwaryo mata, tausayi ta bashi ya sanya hannu yana goge mata hawayen fuska a daure yace."Idan baki daina min wannan kukan ba yanzu zansa Captain Habu ya mai dake gida."
Zum'bura baki tayi....Yace."Ni dai na fad'a miki." fuskarta ta hau gogewa da hannunta tana kallonsa shima yana kallonta zuwa yanzu ya gama fahimtar yana da babban matsayi a zuciyar yarinyar yana ganin tsananin sonsa da kaunarsa a cikin kwayar idonta.....Suna cikin wannan hali Captain habu ya shigo da take away a hannunsa, Sai yasa dariya yana fad'in"Kaga laila majnun ko."!! Sadam yayi saurin dauke kansa yana dan harararsa, Yana dariya ya zauna a wata kujera yace"Sayyada lallai kina son abokina da yawa nifa yau na dauka hawayenki ne zai kare." murmushi tayi ta sunkuyar da kanta kasa.
Yace."Ga abinci na kawo miki kici." Girgiza kai tayi alamun bata ci. Yace."Me yasa."? A hankali tace"Bana jin yunwa." Kai tsaye yace."Ban yarda ba dole kici wani abu idan kuma kin fiso angon naki ya baki a baki to." Tayi saurin kallonsa yana kwance idanunsa a rufe ya bude yana harar Captain habu din da jin abinda yace.....Captain habu ya mike yana fad'in"Bari in baku guri tun kafin in sha naushi." Dariya tayi tana kallon mutumin nata....Bayan fitar captain habu da minti biyar likita ya shigo da sauri ya kalle ta domin yaga yanayin da take ciki har yanzu hijab dinta na jikinta.....Ta gaishe da dector din shi kuma ya tambaye ta mai jiki tace da sauki....Ya hau duba jikin Sadam! suna hira sama-sama bayan ya bashi magani ya fita ya juyo yana kallonta da d'aurarriyar fuska yace."Kar wanda ya 'kara shigowa kika gaishe shi ranki sai ya 'baci!." Da mamaki ta kalleshi yace."Kinji abinda nace miki ko."? d'aga kanta tayi....Ya mai da idanunsa ya rufe yana jin wani irin kishi a cikin ransa ai dole ne ma ta bar asibitin nan,
Muryarta ya jiyo tana fad'in"Ka tashi kasha maganin to."! banza yayi mata tace"Kaji." ya bude idonsa yana kallonta sai ta sunkuyar da kanta...."Sayyada."! ya ambaci sunanta cikin wata iriyar murya.Ta kalleshi yace."Bana bukatar damuwa yanzu kuci abinci ki kwanta ok."
"Nifa bana ci."! Tafada duk ranta a 'bace! yace." Kanki kikayiwa ai." Dakin yayi shiru na tsawon minti goma ta mike ta shiga bandakin dake cikin dakin minti uku ta fito tazo ta ra'ba kusa dashi zata kwanta....."Ke! meye haka tashi ki koma kan kujerar can ki kwanta." Abinda ya fada yasa ta maka masa harara! ya kuma ganta ta gyara kwanciyarta a gefansa....."Wai kina so ki dauje min ciwo na ne? idan takura min Zakiyi zan fita in bar miki da'kin." Kuka tasa tana shashshake takaici ya isheshi ya mike zaune da kyar yana kallonta kudundune a cikin hijab tana kuka yace."Kiyi min shiru malama dukanki ko zaginki nayi da zaki cika min kunne da kuka mtswww!.
Rage sautin kukan tayi tana goge hawaye yace."Ki kwanta inda kike tunda kin nace! kar ki matso kusa dani balle ki sanya ni a wani hali." Ita dai bata ce masa komai ba ta kwanta......Cikin karfin hali ya mike yaje ya kulle dakin ya dawo ya kwanta minti goma bacci ya daukeshi.....Ta bude idonta tana kallonsa kauna da sonsa da tausayinsa na 'kara nunkuwa a cikin ranta.
Itace ra riga tashi taga gari har ya soma haske tana kallon agogo ya nuna mata lokaci karfe shida da kwata na safe da sauri ta sauka taje ta dauro alwala ta fito motsinta shine ya farkar dashi ya mike zaune alhamdullahi jikin da sauki ya mike ya nufi toilet din Alwala yayi ya fito ya tada sallah, kusa da ita........A hankali ta juya tace."Ina kwana ya jiki"? Ya amsa mata babu yabo babu fallasa, mikewa tayi ta zauna gefan gadon hijab din ta cire ya kalleta da d'aurarriyar fuska "Ki shirya idan anjima za'a mayar dake gida ko kuma idan su Mamah sunzo ki bisu."
Hajiya Fatsima ta sako hijab suka nufi barikin sojojin domin duba halin da d'ansu yake ciki.....Ganinsa zaune yana shan yoght sai hankalinsa ya kwanta Captain Habu ya gaisa dasu Hajiya Fatsima tace"Ka kyauta wato shine ka'ki yi min bayani abinda ya faru sai a tv na gani."
Yace."Mamah ai abun alkairi ake fad'a shiyasa ban sanar daku komai nasan da na fada miki a lokacin zakice zaku zo to ganinsa a wannan lokacin zai d'aga muku hankali shiyasa muka bari sai da aka gama komai tukkuna."
Alhaji Auwal yace."Alhamdullahi ai da sauki ma al'amarin Allah ya kare ku ya kare ya kuma baku nasara a duk inda zaku shiga." Captain Habu ya amsa da ameen kana ya fita ya barsu domin su gana.
Sayyada gefansa ta zauna tana ta kallon kirjinsa inda aka harbe shi tsigar jikinta sai tashi takeyi hawaye kuwa wannan na bin wannan...Sulaiman ya gyada kai ba tare da yace wa dan uwan nasa komai ba ya fice daga dakin ya tsani yaga Sayyada na kusantar inda Sadam! yake. Motarsa ya shiga ya bar barikin sojojin.....A nutse ya gaisa da iyayen nasa yana musu 'karin bayanin kan yanda al'amarin ya faru...Hajiya Fatsima sai da tayi kuka tace"Ni kuwa Da zaka bi shawara ta to da ka ajiye aikin nan Sadam! akwai had'ari a cikinsa." A take ya 'bata fuska yace."Mammah bana son kina irin wannan magana wallahi! tunda na fara wannan aiki bana fata in aje kuma wallahi wallahi wallahi bana yi domin kudi ko wata daukaka ko mukami inayi ne kawai saboda 'kasata Nejaria sannan inayi ne domin taimakon al'umma addua kawai nake bukata a gurunku." Tace"Shikkenan Sadam! Ubangiji Allah ya shige maka gaba Allah ya kare ku a duk inda kuke ya tsare gabanku da bayanku." Suka amsa da "ameen." dukaninsu.......To koda suka tashi tafiya Sayyada ta'ki binsu akayi akayi ta'ki sai ma ta haye kan gadon ta 'buya a bayansa .Alhji Awal yace."A kyaleta ta zauna Sadam! bai so haka saboda abokanan aikinsa na shigowa duba shi to dan ba yanda zaiyi yasa ya hakura suka tafi suka barta.
To a cikin mota iyayen maganar suke inda Hajiya Fatsima take cewa''Ni kuwa rashin jituwar Sadam da Sulaiman na bani tsoro Alhaji yara kamar ba 'yan uwa ba ka duba ka gani Sulaiman ne ya dace ya zauna yayi jinyar dan uwansa amma ka lura ko minti biyar baiyi ba ya fita kuma bai ce masa sannu ba wannan al'amari ya 'bata min rai kuma babu babban mai laifi sai Sulaiman din tunda dai shine babba."
Alhaji Auwal yana draving yace."Kin san Sulaiman akwai sabga mybe kiransa akayi a waya shiyasa kika ga ya fita bai zauna ba amma na tabbatar zai koma ya duba shi bana so ki sanya wani abu a cikin ranki."
Tace."Wallahi al'amarin ke bani mamaki shiyasa nake magana Allah ya dai-dai ta tsakaninsu." Ya amsa da ''ameeen ya rabbi."!
***
Kallonta yake itama tana kallonsa idanunta yayi fululu saboda kuka babu yabo babu fallasa yace."Ya kamata ki daina wannan kukan ya isa haka."
Ta goge hawayen fuska mirya a dashe tace."Tausayinka nakeji don girman Allah ka daina wannan aikin kaji."
Shan kunu yayi yace."Ke! bana son shirme! Wannan aikin idan kinga na bari to bana nuffashi."
Hawaye ya sake kwaryo mata, tausayi ta bashi ya sanya hannu yana goge mata hawayen fuska a daure yace."Idan baki daina min wannan kukan ba yanzu zansa Captain Habu ya mai dake gida."
Zum'bura baki tayi....Yace."Ni dai na fad'a miki." fuskarta ta hau gogewa da hannunta tana kallonsa shima yana kallonta zuwa yanzu ya gama fahimtar yana da babban matsayi a zuciyar yarinyar yana ganin tsananin sonsa da kaunarsa a cikin kwayar idonta.....Suna cikin wannan hali Captain habu ya shigo da take away a hannunsa, Sai yasa dariya yana fad'in"Kaga laila majnun ko."!! Sadam yayi saurin dauke kansa yana dan harararsa, Yana dariya ya zauna a wata kujera yace"Sayyada lallai kina son abokina da yawa nifa yau na dauka hawayenki ne zai kare." murmushi tayi ta sunkuyar da kanta kasa.
Yace."Ga abinci na kawo miki kici." Girgiza kai tayi alamun bata ci. Yace."Me yasa."? A hankali tace"Bana jin yunwa." Kai tsaye yace."Ban yarda ba dole kici wani abu idan kuma kin fiso angon naki ya baki a baki to." Tayi saurin kallonsa yana kwance idanunsa a rufe ya bude yana harar Captain habu din da jin abinda yace.....Captain habu ya mike yana fad'in"Bari in baku guri tun kafin in sha naushi." Dariya tayi tana kallon mutumin nata....Bayan fitar captain habu da minti biyar likita ya shigo da sauri ya kalle ta domin yaga yanayin da take ciki har yanzu hijab dinta na jikinta.....Ta gaishe da dector din shi kuma ya tambaye ta mai jiki tace da sauki....Ya hau duba jikin Sadam! suna hira sama-sama bayan ya bashi magani ya fita ya juyo yana kallonta da d'aurarriyar fuska yace."Kar wanda ya 'kara shigowa kika gaishe shi ranki sai ya 'baci!." Da mamaki ta kalleshi yace."Kinji abinda nace miki ko."? d'aga kanta tayi....Ya mai da idanunsa ya rufe yana jin wani irin kishi a cikin ransa ai dole ne ma ta bar asibitin nan,
Muryarta ya jiyo tana fad'in"Ka tashi kasha maganin to."! banza yayi mata tace"Kaji." ya bude idonsa yana kallonta sai ta sunkuyar da kanta...."Sayyada."! ya ambaci sunanta cikin wata iriyar murya.Ta kalleshi yace."Bana bukatar damuwa yanzu kuci abinci ki kwanta ok."
"Nifa bana ci."! Tafada duk ranta a 'bace! yace." Kanki kikayiwa ai." Dakin yayi shiru na tsawon minti goma ta mike ta shiga bandakin dake cikin dakin minti uku ta fito tazo ta ra'ba kusa dashi zata kwanta....."Ke! meye haka tashi ki koma kan kujerar can ki kwanta." Abinda ya fada yasa ta maka masa harara! ya kuma ganta ta gyara kwanciyarta a gefansa....."Wai kina so ki dauje min ciwo na ne? idan takura min Zakiyi zan fita in bar miki da'kin." Kuka tasa tana shashshake takaici ya isheshi ya mike zaune da kyar yana kallonta kudundune a cikin hijab tana kuka yace."Kiyi min shiru malama dukanki ko zaginki nayi da zaki cika min kunne da kuka mtswww!.
Rage sautin kukan tayi tana goge hawaye yace."Ki kwanta inda kike tunda kin nace! kar ki matso kusa dani balle ki sanya ni a wani hali." Ita dai bata ce masa komai ba ta kwanta......Cikin karfin hali ya mike yaje ya kulle dakin ya dawo ya kwanta minti goma bacci ya daukeshi.....Ta bude idonta tana kallonsa kauna da sonsa da tausayinsa na 'kara nunkuwa a cikin ranta.
Itace ra riga tashi taga gari har ya soma haske tana kallon agogo ya nuna mata lokaci karfe shida da kwata na safe da sauri ta sauka taje ta dauro alwala ta fito motsinta shine ya farkar dashi ya mike zaune alhamdullahi jikin da sauki ya mike ya nufi toilet din Alwala yayi ya fito ya tada sallah, kusa da ita........A hankali ta juya tace."Ina kwana ya jiki"? Ya amsa mata babu yabo babu fallasa, mikewa tayi ta zauna gefan gadon hijab din ta cire ya kalleta da d'aurarriyar fuska "Ki shirya idan anjima za'a mayar dake gida ko kuma idan su Mamah sunzo ki bisu."