Sashe 4
Naga Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mami ta d’an bu’de idonta ta furta “To menene idan ba wannan ba?” “Ya sake ni…” Wani irin ja da baya Mami ta yi idonta a waje tana kallona baki a bu’de ta shiga shock sosai cikin wani irin yanayi ta furta “What? Ya sake ki Aysha? Shi Ahmad d’in ne ya sake ki? A kwana guda da kika yi a gidansa to Uban me kika masa?” Hawaye ne suka fara ambaliya a fuskata na gayawa Mami duk abinda ya faru ban b’oye mata komai ba. Dariya Mami ta yi tana furta “Sharrin D’a Namiji! Ga abinda nake gudu ya zo. Sai ki tashi mu je wajen Abbanki na bashi tukuicin alheri da Ahmad ya kawo masa, ya mayar masa da y’a k’aramar bazawara Ahmad dai mai nagartattun halayen da Ubanki yake faman b’ab’atu akai.” Ido na waro waje ganin tana ja hannuna “Tashi mu je mana.” Na ja hannun ina girgiza kai “Mami, ba zan iya zuwa wajen Abba ba, Allah ina tsoro, ban san yarda zai d’au lamarin ba.” Wani kallo ta min cikin b’acin rai ta furta “Tashi na ce miki mu je ko? Iyakacinsa dai dake fa’da, tunda ba zai iya zare miki ranki ba.” Ta fa’da a fusace ta kuma fincikeni muka fita wajen.
Abin haushi Jama’a an fito gaba d’aya kowa sai baza ido yake ana kallon mu. Kallo guda Mami ta musu suka dinga bajewa suna ba mu hanya. Ban yi mamaki ba don ni da kai na na san an samu topic.
Abba na zaune yana lazimin safiya. Umma ce a gefensa tana ha’da masa coffee da ya saba sha duk safiya. Da alama shi bai san abinda ya faru ba. Balle Umma da tun jiyan bata fita daga sashensa ba.
A razane duk suka zuba mana idonsu musamman Umma da har Cokalin hannunta yake fa’duwa. “FATIMA lafiya kuwa? Naga Aysha da sassafe.” Umma ta fa’da tashin hankalinta na sake bayyana a saman fuskarta.
Zama Mami ta yi a gefen Kujerar da yake kusa da Abba, ta saka ni a gefenta ta furta “Lafiyar kenan Umma, sai dai d’an gaban goshin naku ya muku Aiken tukuicin sakamakon alherin da kuka masa…”
Abba da yake laziminsa ya d’ago ya d’an zubawa Mami ido don ya san halin kayarsa sarai danger ce wutar baya. Umma kuwa cup d’in ta ajiye tana sake furta “Me ya faru to? amma fa Mammin Aysha ya kamata ki yiwa y’ar taki fa’da ta san fa ta girma, aure kuma ba wasan yara ba ne. Idan ban da shashashanci menene na dako wannan Uban sammakon, koma menene ba ga waya ba me yasa ba zata sanar miki ba? Sai ta d’ebo jiki ta taho ta saka y’an biki su tafi da ita a bakin duniya tunda ko gama watsewa ba su yi ba. Aa sam wannan wauta ce da shirme.” Mami wani kallo ta mata sai kuma ta cije baki.
“Kamawa ta yi, ta dako uban sammakon babu gaira ba dalili ba abinda zai sakata fitowa daga gidan Mijin da aka kai ta jiya.” Mami ta fa’da tana hura hanci da jijjiga k’afa. Umma dai shiru ta yi don ba mamaki ta lura idan ta cigaba da magana tata ce zata yi zafi.
Abbana yana jin su bai yi magana ba ya cigaba da laziminsa. Sai da ya idar sannan ya ‘d’au coffee d’insa ya shanye ya zuba min kallon da na kusan jin kayan cikina suna shirin fitowa. “Ke wace irin shashasha ce Aysha? Daga kai ki gidan Miji jiya yau ki fito? Kin d’auka auren wasa ne? Me ya fito da ke?”
Madadin amsa masa jiki na ne ya dinga rawa kamar yarda zuciyata take bugawa. “Ba magana nake miki ba?” Ya sake fa’da da Tsawar gaske, hakan da yasa har ban san sanda na rik’e Mami da kyau ba ina makyarkyata “A’a Alhaji, kada ka sake hargitsata Ai ba laifinta ba ne fitowar dole ne ta fito tunda ya saketa…..” Gaba d’aya bakinsu a ha’de suka furta “Saki Fatima?” Ta jijjiga kai tana murmushi ha’de da furta “Sakamakon halaccin da kuka masa ne, duk duniya kuna ganin ba wanda ya cancanta kamar Ustaz Ahmad. Kullum zancenku nagartaccen mutum ne mai ilimin addini da ya shahara a duniyar Malamai. Yau ga ilimin nasa nan ya fara nuna muku….” D’akin tsit ya yi Abba jikinsa har rawa yake. Umma kuwa zama ta yi jab’ar a k’asa ta rik’e kanta kawai jikinta na rawa….
𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️
[8/5, 1:21 PM] Nazeefah Nashe: Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/LSB89Dp71pHETB3hpaWohR
NAGA RAYUWA♥︎♥︎♥︎
𝒩𝒶𝓏ℯℯ𝒻𝒶𝒽 𝒩𝒶𝓈𝒽ℯ★✍️
Free Book.. MIKIYA WRITERS ASSOCIATION
Arewabooks @nazeefah
Wattpad@Nazeefah381
08033748387.
★★★★★ 𝒫𝒶ℊℯ 4..
Da mamaki Umma take kallonta su Yaya Muhammad suma suka zuba mata ido. Ya Usman da ya kasa shiru ya ce “Au ke kuma auren ne ba kya son ta yi? Shi yasa zata ke k’unshe fuskarta, amma kamar wannan ba dabara ba ce..” Harara ta watsa masa tana furta “To kanari Uban surutu, ni na ce maka bana son ta yi aure? Auren ne dai ba yanzu zata yi shi ba sai ta yi dogon karatun da na tabbatar zata iya k’watar y’ancin kanta a
Wajen namiji sannan zan amince ta yi aure, haka kawai ba za’a aurar da ita da duhun kai ba shikkenan ta zama sai kace baiwa wajen namiji…” Cikin mamaki suka zuba mata ido, Umma kanta ta yi mamakin furucin Mamin, sai dai data tuna Mamin gidansu gangariyar y’an boko ne sai bata yi mamaki ba ta saki ajiyar zuciya kawai tana furta “Allah ya taimaka, ya nuna mana lokacin…” Yaya Muhammad gyara zama ya yi yana tab’e baki ya furta “Amma dai wannan kamar ba shawara ba ce mai b’illewa, Saboda kowa yanzu burinsa a ce y’arsa ta yi aure sai ta yi karatun a nata gidan Mijin….” “Sai ka bari sai ka haifi taka y’ar Muhammad ba wannan ba…” ta fa’da a zafafe tana nuna ni. Ta ja hannuna muka wuce samanta.
Tana banbamin fa’da har da rantsuwar nan gaba idan Muhammad bai yi wasa ba sai ta mare shi.
A kashegarin ranar kuwa bayan na yi wanka Mami ta tsantsara min kwalliya cikin shigar kayan hausawa da suka min matuk’ar kyau. Murna na dinga yi don kam dama ina son su Mamin ce bata ba ni damar sakawa ba.
Sanda na fita tsakargida idanun masu aiki duk a kaina suke, sunan ta dariya ganin kwalliyar da aka min. Har Iya ta kasa shiru ta ce “Lallai Aishatun Mami ta girma… Ma sha Allah a yi shekaru irin na dabino.”
Abba da yake zaune daga can gefe shi da su Yaya Muhd, baki sake ya dinga kallona yana furta “Inye Aishatun ba, irin wannan
Kwalliya haka? Waye ya siyo
Miki kayan hausawa…” ina dariya na zauna daf da shi an furta “‘Mami na ce, ita ta siyo min su da yawa ta ce na daina saka wa’dancan kayan yahudun.” Jan hancina Abba ya yi ya ce “Ai ke ce Yahudun.” Sannan ya juya yana kallon su Ya. Muhd ya furta “Kun ga abinda na gaya muku ko? Na gaya muku kada ku tada hankalinku a kan yarinyar nan Fatima ba zata yi sanadin gurb’acewar tarbiyyarta ba..Fateema mace ce data san abinda take yi.” Shiru su ka yi suna cigaba da shan kununsu Ya Ali ne ya furta “Ba shakka, to Allah yasa dai ba da wata manu…” wani kallo naga Umma ta masa sai ya ja bakinsa ya tsuke yana dariya.
Tun daga ranar ya zama na saba saka kayan hausawa, kuma ko aike na waje za’a yi Mami na bata bari na fita ba nik’ab har hakan ya zame min
Jiki. Sai dai a fuskar Umma
Wani lokacin ina kallon yanayinta kamar hakan baya mata da’di, sai dai ba yarda zata yi ne. Duk inda na je kuwa sha’awar shigata ake, don kowa ya ganni ya san d’iyar wacece? D’iyar mace mai mutunci wacce ta san ciwon kanta, kuma yake bawa y’arta tarbiyya, ba wacce da kanta take saka y’a’yanta shigar banza ba don kawai su kawo mata mazan aure ta dinga kuma zuga su da fa’din sun yi kyau.
Sanda na fara period kuwa, Mami hana aikena ta yi. Saboda wani irin kyau da na dinga zubawa, mak’erin y’an mata na ji suna cewa ya fara k’era ni. Don haka ta shiga taka tsantsan da ni. Idan Ya. Muhd ya yi magana ta hau masa masifa don haka ya gani ya zuba mata ido kamar yarda kowa ya yi.
Sanda maganar aurensu ta bujiro da y’ay’an abokin Abba Mami na jin iya secondary kawai suka gama. Ta dinga tab’e baki tana fa’din “Amma Sadik kun yi bak’ar dabara, yanzu meye riba a auren k’wailayen mata?” Ya Muhd don takaici kasa mata magana ya yi, Ya. SADIK MURMUSHI ya saki yana furta “Ai auren irinsu Mami ya fi riba, ko bakomai zasu bi duk wani tsari da aka shar’anta musu..” Ta ja tsaki ta furta “Mugunta zaku musu ba, ai shikkenan shi yasa duk bala’i ba zan yarda AYSHA ta yi aure daga gama secondary ba dole ko degree sai ta yi, idan ma bata yi masters ba…” Ya Muhd da yake tsaye ya tura hular sa goshi yana furta “A dai rage dogon buri, idan yarinya ta yi girma da yawa yanzu mazan ma gudun aurenta suke, don sun san tafi k’arfinsu…” Yana ji ta k’unduma wani zagi ya shige d’akinsu yana dariya.
Haka kuwa aka yi, bayan wani lokaci aka gudanar da bikin Ya. Muhd da Ya sadik. Muhd da Khadija, Yaya Sadik kuma da Nafisa a lokacin ina Js 3. Amma duk wata cika ta matantaka ta bayyana a surar jiki na.
★★★✍️
Abin haushi Jama’a an fito gaba d’aya kowa sai baza ido yake ana kallon mu. Kallo guda Mami ta musu suka dinga bajewa suna ba mu hanya. Ban yi mamaki ba don ni da kai na na san an samu topic.
Abba na zaune yana lazimin safiya. Umma ce a gefensa tana ha’da masa coffee da ya saba sha duk safiya. Da alama shi bai san abinda ya faru ba. Balle Umma da tun jiyan bata fita daga sashensa ba.
A razane duk suka zuba mana idonsu musamman Umma da har Cokalin hannunta yake fa’duwa. “FATIMA lafiya kuwa? Naga Aysha da sassafe.” Umma ta fa’da tashin hankalinta na sake bayyana a saman fuskarta.
Zama Mami ta yi a gefen Kujerar da yake kusa da Abba, ta saka ni a gefenta ta furta “Lafiyar kenan Umma, sai dai d’an gaban goshin naku ya muku Aiken tukuicin sakamakon alherin da kuka masa…”
Abba da yake laziminsa ya d’ago ya d’an zubawa Mami ido don ya san halin kayarsa sarai danger ce wutar baya. Umma kuwa cup d’in ta ajiye tana sake furta “Me ya faru to? amma fa Mammin Aysha ya kamata ki yiwa y’ar taki fa’da ta san fa ta girma, aure kuma ba wasan yara ba ne. Idan ban da shashashanci menene na dako wannan Uban sammakon, koma menene ba ga waya ba me yasa ba zata sanar miki ba? Sai ta d’ebo jiki ta taho ta saka y’an biki su tafi da ita a bakin duniya tunda ko gama watsewa ba su yi ba. Aa sam wannan wauta ce da shirme.” Mami wani kallo ta mata sai kuma ta cije baki.
“Kamawa ta yi, ta dako uban sammakon babu gaira ba dalili ba abinda zai sakata fitowa daga gidan Mijin da aka kai ta jiya.” Mami ta fa’da tana hura hanci da jijjiga k’afa. Umma dai shiru ta yi don ba mamaki ta lura idan ta cigaba da magana tata ce zata yi zafi.
Abbana yana jin su bai yi magana ba ya cigaba da laziminsa. Sai da ya idar sannan ya ‘d’au coffee d’insa ya shanye ya zuba min kallon da na kusan jin kayan cikina suna shirin fitowa. “Ke wace irin shashasha ce Aysha? Daga kai ki gidan Miji jiya yau ki fito? Kin d’auka auren wasa ne? Me ya fito da ke?”
Madadin amsa masa jiki na ne ya dinga rawa kamar yarda zuciyata take bugawa. “Ba magana nake miki ba?” Ya sake fa’da da Tsawar gaske, hakan da yasa har ban san sanda na rik’e Mami da kyau ba ina makyarkyata “A’a Alhaji, kada ka sake hargitsata Ai ba laifinta ba ne fitowar dole ne ta fito tunda ya saketa…..” Gaba d’aya bakinsu a ha’de suka furta “Saki Fatima?” Ta jijjiga kai tana murmushi ha’de da furta “Sakamakon halaccin da kuka masa ne, duk duniya kuna ganin ba wanda ya cancanta kamar Ustaz Ahmad. Kullum zancenku nagartaccen mutum ne mai ilimin addini da ya shahara a duniyar Malamai. Yau ga ilimin nasa nan ya fara nuna muku….” D’akin tsit ya yi Abba jikinsa har rawa yake. Umma kuwa zama ta yi jab’ar a k’asa ta rik’e kanta kawai jikinta na rawa….
𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️
[8/5, 1:21 PM] Nazeefah Nashe: Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/LSB89Dp71pHETB3hpaWohR
NAGA RAYUWA♥︎♥︎♥︎
𝒩𝒶𝓏ℯℯ𝒻𝒶𝒽 𝒩𝒶𝓈𝒽ℯ★✍️
Free Book.. MIKIYA WRITERS ASSOCIATION
Arewabooks @nazeefah
Wattpad@Nazeefah381
08033748387.
★★★★★ 𝒫𝒶ℊℯ 4..
Da mamaki Umma take kallonta su Yaya Muhammad suma suka zuba mata ido. Ya Usman da ya kasa shiru ya ce “Au ke kuma auren ne ba kya son ta yi? Shi yasa zata ke k’unshe fuskarta, amma kamar wannan ba dabara ba ce..” Harara ta watsa masa tana furta “To kanari Uban surutu, ni na ce maka bana son ta yi aure? Auren ne dai ba yanzu zata yi shi ba sai ta yi dogon karatun da na tabbatar zata iya k’watar y’ancin kanta a
Wajen namiji sannan zan amince ta yi aure, haka kawai ba za’a aurar da ita da duhun kai ba shikkenan ta zama sai kace baiwa wajen namiji…” Cikin mamaki suka zuba mata ido, Umma kanta ta yi mamakin furucin Mamin, sai dai data tuna Mamin gidansu gangariyar y’an boko ne sai bata yi mamaki ba ta saki ajiyar zuciya kawai tana furta “Allah ya taimaka, ya nuna mana lokacin…” Yaya Muhammad gyara zama ya yi yana tab’e baki ya furta “Amma dai wannan kamar ba shawara ba ce mai b’illewa, Saboda kowa yanzu burinsa a ce y’arsa ta yi aure sai ta yi karatun a nata gidan Mijin….” “Sai ka bari sai ka haifi taka y’ar Muhammad ba wannan ba…” ta fa’da a zafafe tana nuna ni. Ta ja hannuna muka wuce samanta.
Tana banbamin fa’da har da rantsuwar nan gaba idan Muhammad bai yi wasa ba sai ta mare shi.
A kashegarin ranar kuwa bayan na yi wanka Mami ta tsantsara min kwalliya cikin shigar kayan hausawa da suka min matuk’ar kyau. Murna na dinga yi don kam dama ina son su Mamin ce bata ba ni damar sakawa ba.
Sanda na fita tsakargida idanun masu aiki duk a kaina suke, sunan ta dariya ganin kwalliyar da aka min. Har Iya ta kasa shiru ta ce “Lallai Aishatun Mami ta girma… Ma sha Allah a yi shekaru irin na dabino.”
Abba da yake zaune daga can gefe shi da su Yaya Muhd, baki sake ya dinga kallona yana furta “Inye Aishatun ba, irin wannan
Kwalliya haka? Waye ya siyo
Miki kayan hausawa…” ina dariya na zauna daf da shi an furta “‘Mami na ce, ita ta siyo min su da yawa ta ce na daina saka wa’dancan kayan yahudun.” Jan hancina Abba ya yi ya ce “Ai ke ce Yahudun.” Sannan ya juya yana kallon su Ya. Muhd ya furta “Kun ga abinda na gaya muku ko? Na gaya muku kada ku tada hankalinku a kan yarinyar nan Fatima ba zata yi sanadin gurb’acewar tarbiyyarta ba..Fateema mace ce data san abinda take yi.” Shiru su ka yi suna cigaba da shan kununsu Ya Ali ne ya furta “Ba shakka, to Allah yasa dai ba da wata manu…” wani kallo naga Umma ta masa sai ya ja bakinsa ya tsuke yana dariya.
Tun daga ranar ya zama na saba saka kayan hausawa, kuma ko aike na waje za’a yi Mami na bata bari na fita ba nik’ab har hakan ya zame min
Jiki. Sai dai a fuskar Umma
Wani lokacin ina kallon yanayinta kamar hakan baya mata da’di, sai dai ba yarda zata yi ne. Duk inda na je kuwa sha’awar shigata ake, don kowa ya ganni ya san d’iyar wacece? D’iyar mace mai mutunci wacce ta san ciwon kanta, kuma yake bawa y’arta tarbiyya, ba wacce da kanta take saka y’a’yanta shigar banza ba don kawai su kawo mata mazan aure ta dinga kuma zuga su da fa’din sun yi kyau.
Sanda na fara period kuwa, Mami hana aikena ta yi. Saboda wani irin kyau da na dinga zubawa, mak’erin y’an mata na ji suna cewa ya fara k’era ni. Don haka ta shiga taka tsantsan da ni. Idan Ya. Muhd ya yi magana ta hau masa masifa don haka ya gani ya zuba mata ido kamar yarda kowa ya yi.
Sanda maganar aurensu ta bujiro da y’ay’an abokin Abba Mami na jin iya secondary kawai suka gama. Ta dinga tab’e baki tana fa’din “Amma Sadik kun yi bak’ar dabara, yanzu meye riba a auren k’wailayen mata?” Ya Muhd don takaici kasa mata magana ya yi, Ya. SADIK MURMUSHI ya saki yana furta “Ai auren irinsu Mami ya fi riba, ko bakomai zasu bi duk wani tsari da aka shar’anta musu..” Ta ja tsaki ta furta “Mugunta zaku musu ba, ai shikkenan shi yasa duk bala’i ba zan yarda AYSHA ta yi aure daga gama secondary ba dole ko degree sai ta yi, idan ma bata yi masters ba…” Ya Muhd da yake tsaye ya tura hular sa goshi yana furta “A dai rage dogon buri, idan yarinya ta yi girma da yawa yanzu mazan ma gudun aurenta suke, don sun san tafi k’arfinsu…” Yana ji ta k’unduma wani zagi ya shige d’akinsu yana dariya.
Haka kuwa aka yi, bayan wani lokaci aka gudanar da bikin Ya. Muhd da Ya sadik. Muhd da Khadija, Yaya Sadik kuma da Nafisa a lokacin ina Js 3. Amma duk wata cika ta matantaka ta bayyana a surar jiki na.
★★★✍️