← Book details Naga Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 30

Sashe 27

Naga Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Muka gama tsara bikinmu da y’ay’an Anty Aseeya k’anwar Mami, kafin Ustaz ya sake dawowa d’aukar mu. Sanda muka isa gida Asma tana fita ya saka hannunsa ya rik’e hannuna. Tsawon minti guda yana murza hannun kafin ya ware idonsa a kaina. “Me yasa ba kya amsa wayata da daddare?” Muryata a hankali na furta “Barci Ustazuna barci ne ke hana ni sak’at.” Ya cije leb’ensa yana narkar da idonsa cikin nawa ya furta “Ki yi barci ki more AYSHA, gwara ki yi barcin yanzu don ina tabbatar miki ranar first night d’inmu ba barci till down zamu yi mai zafin gaske….” Da sauri na lumshe ido na. Ya saki hannun yana furta “Good night, abinda bai yi ba a lefe feel free ki gaya min.” Na girgiza kai na ina furta “Na san Ustazu na ya iya zab’e zan kuma yi farin ciki da dukkan abinda ya fito daga hannunka.” “Jikina fa?” Ya furta yana d’aga gira da sakin murmushi… da sauri na fice ina furta “Har jikin…” Sai naga ya waro ido ya buso min iska alamar kiss yana sakin murmushi ya furta “I love you till my last breath…” na shige gida cikin wani irin zallar farin ciki.

Tun a gate Asma ta wani rungumeni tana furta AYSHA ke mai sa’a ce kin ga lefenki kuwa?” Murmushi kawai na saki wata kunya na sake baibayeni wai ni Aysha yau ake zancen aure na a gidanmu. A parlorn Abba na tarar da su da yake na san lefen suke kalla hakan ya saka ni guduwa sama don har ga Allah ba zan iya zaman kallon lefen ba…

Da daddare Mami ta shigo still yau ma cikin shigar wata shegiyar rigar barci sai zabga k’amshin turare take. Gashinta a sake sai baza k’amshi yake da alama ta yi gabbasar gashi. Glass cup ne a hannunta mai d’auke da madara ta zauna a gefen gadon ta mik’a min cup d’in. “Tashi ki sha AYSHA.” Na karb’a na kafa kai na shanye. Mami ta zuban ido tana saki wani malalacin murmushi ta furta “Yau zan sanar da ke abinda baki sani ba Aysha Zan koya miki yarda zaki mallaki Ustaz in a romantic way…. “ Dishi dishi na dinga gani a idona na fara kallon Mami bibbiyu da duk abinda take furtawa yana shiga kunne na kafin na ga ta saka hannu ta baje gashin kanta ta ‘dago tana min wani kallo…..

𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️😉‎
[8/5, 1:21 PM] Nazeefah Nashe: NA GA RAYUWA…….20.

Gaskiya ku min kara, ku yi dandazo ku nuna wa Littafin mu ja Bright pens na Aysha Cool. K’arfe a wuta….. soyayya wacce zata girgiza media… a fito a siyi k’arfe a wuta ko na yi yajin aikin rubutu na sati guda 😒 yauwa eeehe.

Don samun littafin kai tsaye ka tuntub’i AYSHA COOL MARUBUCIYAR K’ANWAR MAZA. Kowa dai ya san yarda labarin ya kara’de Media.. tuna da sunan K’ARFE A WUTA.

I dedicated this page to my lovely sis Nimcyluv. “Saboda sonki da littafin Na ga rayuwa na mallaka miki wannan page d’in. Really appreciated 🥰.

Masu bina private kan na mayar da shi na ku’di saboda na dinga musu posting 2 times a day. Ku yi hak’uri Na ga rayuwa dai kyauta na bada shi don haka In sha Allah zamu gama cikin nasara idan ku'din ne ya muku yawa ku siyi books 'dinmu na Bright pens. 🤗

_____________

Cikin lumsassun idona nake kallon abubuwanda Mamin take min a sunan tana koya min yarda zan mallaki zuciyar Ustaz. Har k’afata ta ja a hankali tana matsawa cikin wani salo. “Hakan da nake miki Aysha shine romantic tausa kuma haka ake son ki yiwa Mijinki, ba kunya tsakanin Miji da Mata ki zage ki nemi zuciyar Mijinki ko ta wani hali….” Wasu abubuwan daga baya sam kasa fahintar su nayi, sabida wani irin barci da ya dinga fisgata k’arshe dai ban san ya aka yi ba sai wayar gari nayi naga asuba ta yi. Har gari ya fara haske. Na juya Babu Mami a d’akin idona na lumshe duk abinda ya faru a daren ranar ya shiga dawo min daki-daki. Ajiyar zuciya na sauke kafin na mik’ na shiga toilet don abin na Mami ya girmi kwanyata.

Da yake na san alhamis ce ban wani damu da neman abin kari ba. Still bayan naje ba gaishesu barcin na ji ina sake ji don haka na koma d’aki kawai na sake kwanciya. Daga ranar ya zama kullum Mami sai ta bani wannan madarar na sha da daddare ina sha kuma barci mai nauyin gaske zai d’auke ni ba zan farka ba sai asubahi. A haka kwanakin bikin suka dinga matsawa na dinga zuba wani kyau ga k’irjina ya cika k’ugu na ma haka na yi k’iba ta ban mamaki. Don bana manta wata rana muna zaune a parlorn Abba ana auna ni d’inkin da za’a min wata k’wararriyar tela da ta yi shuhura a ‘dinkin Amare cike da mamaki Umma yake kallo na ta ce “Fateema kin ga yarda AYSHA ta cika ta yi k’iba kuwa kamar ma har ta tare a gidan Mijin? Ko dai har kun fara shan sabayar?” Mami murmushi kawai ta yi ta ‘d’auke kanta tana kallona k’asa k’asa.

Da yamma kuwa ina dawowa daga Islamiyya na shiga parlorn Mamin sai naga ta yi bak’i wasu manyan mata, da kana ganinsu kaga y’an duniya… Sak na yi ina kallonsu a zaune sun ci matsatstsun kaya dole na yi mamaki don ban saba ganin irin su ba a gidanmu. Gaba d’aya k’irjinsu a waje yake, sun baza gashi ga sark’a a k’afarsu. Mami na gani na ta tsuke fuska, k’ok’arin Gaishesu na yi amma sai ta dakatar da ni. “AYSHA sauka k’asa wajen Umma na gama da bak’i tukun.” Sak na yi na juya sai na ji d’aya a cikinsu tana furta “Ma sha Allah, Fateema wannan yarinyar fa komai ya ji akwai kaya gaskiya…” “Ita nake baku labari…” Shine kawai abinda naji. Na sauka k’asa jikina a sanyaye saboda mamakin abinda Mami ta ce na yi. Bata tab’a ce min na sauka k’asa don na yi bak’i ba, sai yau bak’in ma irin wa’dannan marasa kamun kai.

Parlorn Umma na shiga sai na sameta tana waya. Da ido ta bi ni da kallo har na zauna a kujerar da take kusa da ita. Sai da ta gama wayar ta juyo tana kallona ta furta “Ke AYSHA lafiya? Naga kin shigo sukuku da ke.” Girgiza mata kai na yi “Bakomai, Mami ce ta ce nazo nan saboda ta yi bak’i.” “Ki zo nan?” Umman ta furta cikin mamaki don itama abin da bata saba gani ba ne. Na d’aga kaina a hankali. Sai naga taja ajiyar zuciya ta ce “Tashi ki je kitchen maza cikin fridge ki d’auko min wasu jarkoki guda uku suna nan. Ki ha’do da cup.” Na mik’e na shiga kitchen d’in Umman da yake cikin parlornta. D’auko biyu na yi saboda da d’an girmansu kafin na koma na d’auko d’aya da cup. Umma ta bu’de ta farkon ta zuba Rabin cup ta mik’o min “Karb’i ki sha, ba kuma wai don da’di ake shan irin wannan kayan ba don na san ki da shegen kwa’dayi.” Na runtse idona na shanye. Ta sake zuba min na sauran gororin tana furta “Kullum ki dinga zuwa cikin fridge kina bu’desu ki sha, Ko Mamin naki na baki?” Na girgiza kai bata bani komai. Na so gaya mata sai madarar da take bani duk dare da take saka ni barci sai dai na kasa. Ina kallo ta d’an cije leb’enta ta furta “Ai shikkenan, da ni da ita duk d’aya ne, ki dage sosai wajen shan su, akwai wasu ma da zan saka a kawo miki duk da dai na san ko da wannan kika tsaya kin fita zarra Magungunan Anty Surayya mai Bojuwa herbals ba k’arya ba ne, suna da amfani k’warai a jikin mutum. Zan kuma baki numberr wayarta don ki dinga tuntub’arta don samun ingantattun magani na gyaran zamantakewar aure…. Ta mik’e sai gata ta dawo da wata roba. Zuba y’an k’wayoyin maganin ta yi a hannunta ta ha’da min da dabino tace na taune. Sauran kazar sababi tace a satinnan zata kawo miki. Na san komai don haka kunya ta kamani don ina karatun litattafai saboda haka na san magungunan da Umman ta bani da dalilin ba ni su. Da Mami ce ba zan ji kunyarta ba kamar Umman don ita Umma sam bata saki jiki da ni ba. “Gyaran jiki dai ba kya buk’atarsa don fatar ki mai kyau ce ba abinda kike buk’ata, sai zuwa saloon a miki predicure da manicure zuwa jibi ki shirya ki je.” Na d’aga mata kai. Daga haka ta mik’e ta shige kitchen na san ba kunya ce ta saka ta barin wajen. Na d’an saki murmushi kawai ina jin soyayyar Umman da wani irin tausayinta a raina. Ni kenan y’arta mace amma ta iya kyauta da ni ta kuma d’auke kanta a kaina. Lallai Umma ta cika fulanin k’warai masu kunya kara da d’auke kai.

Sai dare sannan bak’i Mami suka tafi. Ina shiga parlorn naga sun yi kaca kaca da shi. Tab’e baki nayi na shige mai aikin da take gyarawa.
Chapter 27 · 0% Book details