Sashe 11
Naga Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Tun daga tsakargida masu aiki suke bina da kallo har na isa parlorn. Su ma su Abba da mamaki suke kallo na ganin yanayin sauyin fuska a tare da ni ba kamar jiya ba da na tashi fuskar kamar hadarin kaji. Mamaki ya ishi Abba ya kasa shiru har sai da ya furta “Ayshan Mameeyn ta, ta samu ne naga kina wani farin ciki.” Sunne kaina na yi ina dariya da girgiza kai. Na mik’a masa kwalin wayar hannuna don na b’oye turarukan. Wayar ya bi da kallo yana furta “Wannan fa Aysha?” Cikin k’asa da murya ina kallon Mami da take min wani kallo na furta “Mutumin jiya ne ya ba ni.” Abba ya ‘dan ware ido yana furta “Ma sha Allah, labarin zuciya a tambayi fuska. Fateemah ya naga haka kuma? D’iyar take da alama ta yi na’am da zanka’de’den mijinta, ke tun baki tsaya kin ji waye ba kike kumfar bakin ba kwa son sa. Ustaz Ahmad Sulaiman Sa’eed babban Malamin nan, yaro da kwanyar manya shine fa yake son ta…” Cikin wani yanayi Mami ta ‘dago idonta tana furta “Ustaz!” Da mamaki a idonta, ta furzar da wani huci tana furta “Shine ma abinda ba zai yi wu ba cab’di! Kama sake nazari….”
𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️[8/5, 1:21 PM] Nazeefah Nashe: NA GA RAYUWA♥︎♥︎♥︎
𝒩𝒶𝓏ℯℯ𝒻𝒶𝒽 𝒩𝒶𝓈𝒽ℯ★✍️
Free Book.. MIKIYA WRITERS ASSOCIATION
Arewabooks @nazeefah
Wattpad@Nazeefah381
08033748387.
★★★★★ 𝒫𝒶ℊℯ 9
Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/LSB89Dp71pHETB3hpaWohR
“Kamar ya?” Abba ya furta yana saka k’wayar idonsa cikin ta Mami. Amma sam yau Mamin wannan kallon na Abba na da alama bai ratsa ta ba, don tab’e bakinta ta yi murya a sama ta furta “Kamar komai ma Abban Aysha.. Ta yaya za’a aura mat Uztaz hakan na nufin makarantar da na ci buri akanta ba zata yi ba kenan? Wani Ustaz ne zai bar matarsa tana yawo a titi fisabilillah, da ma wani d’an boko ne da sauk’i. Amma wannan ha’din sam bai ha’du ba, in dai za’a min adalci akan Aysha a tuna bani da wata da nake gani a matsayin y’ata a bar Aysha ta yi karatu…” Ta fa’da idanunta suna zubar da k’wallar da ta sanya duk jikina sanyi. Amma ban hango sanyin gwiwa a wajen Abba ba, kamar yarda na hango shi a wajen Umma, don a raunane ta ce “Abban Aysha ka yi hak’uri ka janye maganar auren nan….” wani kallo ha hurgawa Umman da ya sata shiru da bakinta tana kallon Mamin a raunace. “Ba zan janye ba, har abada kuwa, don ba zan ga samu naga rashi ba, wani irin solob’iyon Uba kuke so na zama? Allah ya kawowa y’ata nagartaccen Mijin da kowane Uba yake fata sai na masa butulci sabida wani karatun boko na banza da na wofi. Mutumin da ko y’ay’a d’ari yake so za’a ba shi a rana guda, duka ta tsallake ya ce Aysha ce ta masa Aysha yake son aure sai na zuba masa k’asa a ido, Saboda wata maganar banza da wofi. Ita ka’dai ce fa y’ata mace da nake fatan ta yi dace da Mijin k’warai.. ko yanzu yake so na tsame ta a boko na mata aure wallahil azeem na shiryawa haka, ba abinda kuma zai saka ni fasawa. Karatu dai idan ya ce zata yi a gidanta falillahil hamdihi idan ya hanata ma gaba d’aya wallahi ba zan tursasa shi ba. Saboda ku iyayen banza ne ku da zaku saka ta ta yarda ku rarrasheta ku ke sakata ta bijire min? To ku je ku yi na da ku a ga wanda zai ci riba…” Daga haka yaja bakinsa ya tsuke ya kuma wanke hannunsa ya tsoma cikin tuwo ya cigaba da ci. Fuskarsa a ha’de sosai alamar duk abinda ya fa’da har k’asan zuciyarsa hakan yake. Mami ta ture kwanon tuwon da muke ci ni da ita da Umma ta mik’e fuska a ha’de ta fice daga parlorn.
Jikina a sanyaye na mik’e zan bi ta Abba ya saka baki ya kira ni muryarsa a dake. “Dawo Ayshatu, zauna ki ci tuwonki, ba cutar da ke zan yi ba, har ga Allah alheri nake hango miki game da aurenki da Ahmad..” Na d’aga kai na ina wasa da zoben hannuna. “Ki kuma bu’de wayarki ki fara amfani da ita, na san ba zai cutar da ke ba. Ban kuma amince da duk wani tarkacen social media ba…” Na d’aga kaina don shima Ustaz garga’di da ya min kenan. Na san tunda suke ta jaddada min to social media d’in ba abu ba ne mai kyau. Cin tuwon kawai nake ba tare da ina fahimtar d’and’anonsa ba, don dai kada Abba ya yi magana ne na zage na ci tuwon kafin na mik’e cikin mutuwa jiki na haye sama. So nake na je naga Mami da halin da take ciki.
Jikina a sanyaye na murd’a k’ofar d’akinta don bata parlour kamar yarda ta saba zama. A saman gado na sameta hannayenta dafe da k’unci da alama ta yi zurfi cikin tunanin da take. Zama na yi daf da ita ina d’ora kaina a saman kafa’darta. Sai na ji ta saki ajiyar zuciya. Ta rungumoni sosai a jikinta tana furta “Aysha, yanzu kin amince d a auren da Abba zai miki?” K’asa na yi da kaina idona na zubar da k’walla. “Mami kema ki yi hak’uri please…” Janye jikinta ta yi tana sakin wani malalacin murmushi “Na yi hak’uri Aysha? Na yi hak’uri Ustaz ya cuceni ya raba ni da duk wani farin cikina? Ya kuma ruguza min da duk wani shirina a kan ki da na shekara da shekaru ina shiryawa?” Ta girgiza kai tana taune leb’enta ta furta “Wallahi bai isa ba, mu zuba ko ni ko shi?” K’asa na yi da kaina saboda ba zan iya sake cigaba da juriyar kallon idanun Mami ba, don wani abu nake gani a cikin idon… Zamewa ta yi ta kwanta tana mayar da numfashi idanunta a lumshe. “Tashi ki tafi AYSHA, ta shi ki wuce d’akinki…” Ta fa’da a zafafe da sauri kuwa na mik’e ba fice don ban saba ko na ce ban tab’a ganinta a irin wannan yanayin ba… na lura daf take da fara Aljannu…
Da safe har na shirya na gama shirin makaranta Mami bata tashi ba. Hakan yasa na nufi d’akinta ina nocking a hankali. A zafafe ta furta “Waye ne?” “Nice Mami…” ta bu’de k’ofar tana kallona idanunta kuwa da k’yar take lumshe su. Ta ja hannuna tana murzawa a hankali cikin wata irin murya ta furta “Ayshatu…” Na d’ago ina kallonta ta d’an sunkuyar da kai sai kuma ta saki hannun nawa. Tana sakin Malalacin murmushi ta furta “Har kin yi shirin makaranta?” Na d’aga mata kai “Ina kwana Mami?” Amsawa ta yi tana d’an ja baya ta furta “Wuce ki tafi AYSHA, ni ba abinda zaki ce min tunda kin zab’i farin cikin iyayenki a kaina. A jiya na yi takaicin rashin haihuwa da ni na haifeki da kaina na san ba zaki bujire min ba….” Kuka ne yazo min sosai ban san sanda na fa’da jikinta ba na saki wani irin kuka. Mami ta rungumeni sosai a jikinta ina jin yarda take sakin ajiyar zuciya. A kunne ta ra’da min “Kada ki bujire min Aysha, kada ki guje ni zan shiga wani hali AYSHA….” Da k’yar ta zame jikinta daga jikina ta juya bayanta tana furta “Je ki ki rufe min k’ofa…” Jikina a sanyaye na fice daga d’akin nata.
A kitchen na tarar da Umma na tana ta aikinta ita ka’dai. Sai na ji duk ban ji da’di ba don koda yaushe tare suke aikinsu da Mami. Da wayona dai ba zan tab’a cewa ga ranar da suka yi aiki ba tare ba. Kallo guda ta min ta d’auke kanta tana amsa gaisuwata. Na juya zan fice ta furta “Ba zaki k’arya ba ne?” “Umma na k’oshi…” Umma ta bi ni da kallo mai kama da harara tana furta “Ki yi ta k’oshin mana Aysha? Cikin wa? Kin zata ni d’in uwarki ce da zan ta bin ki ina lallab’aki, kin bi kin k’i ki kwantar da hankalinki balle na uwarki ya kwanta sai kace a kan ki aka fara auren early marriage, sanda Ubanki ya auro ni 15yrs nake, ban ma kai ki ba me ya same ni? Mahaifinki dai kaifi d’aya ne, ba mai saka shi ba mai hana shi don haka ki nutsu ki san abinda ki ke. Ban tab’a jin kan Fateemah da Abbanku sai a yanzu da take son ta bujire masa, me ye ribarki idan kin haddasa sab’ani a tsakaninsu? Na ce meye ribarki AYSHA?” Shiru na mata ina bulbular da hawaye. Me yasa Umma zata ga laifina ce mata na yi bana son Ustaz? Bata san nafi kowa son haka ba? Tashin hankalin Mami ne kawai bana so nake b’oye hakan a raina.. “wuce ki bani wuri, ki shirya bujire masa kece zaki wahala don kin san ko magagin mutuwa kike Ubanki sai ya sadaki da gidan mutumin nan…” Na ja k’afata na fice daga kitchen d’in zuciyata a k’untace ranar na isa makaranta.
𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️[8/5, 1:21 PM] Nazeefah Nashe: NA GA RAYUWA♥︎♥︎♥︎
𝒩𝒶𝓏ℯℯ𝒻𝒶𝒽 𝒩𝒶𝓈𝒽ℯ★✍️
Free Book.. MIKIYA WRITERS ASSOCIATION
Arewabooks @nazeefah
Wattpad@Nazeefah381
08033748387.
★★★★★ 𝒫𝒶ℊℯ 9
Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/LSB89Dp71pHETB3hpaWohR
“Kamar ya?” Abba ya furta yana saka k’wayar idonsa cikin ta Mami. Amma sam yau Mamin wannan kallon na Abba na da alama bai ratsa ta ba, don tab’e bakinta ta yi murya a sama ta furta “Kamar komai ma Abban Aysha.. Ta yaya za’a aura mat Uztaz hakan na nufin makarantar da na ci buri akanta ba zata yi ba kenan? Wani Ustaz ne zai bar matarsa tana yawo a titi fisabilillah, da ma wani d’an boko ne da sauk’i. Amma wannan ha’din sam bai ha’du ba, in dai za’a min adalci akan Aysha a tuna bani da wata da nake gani a matsayin y’ata a bar Aysha ta yi karatu…” Ta fa’da idanunta suna zubar da k’wallar da ta sanya duk jikina sanyi. Amma ban hango sanyin gwiwa a wajen Abba ba, kamar yarda na hango shi a wajen Umma, don a raunane ta ce “Abban Aysha ka yi hak’uri ka janye maganar auren nan….” wani kallo ha hurgawa Umman da ya sata shiru da bakinta tana kallon Mamin a raunace. “Ba zan janye ba, har abada kuwa, don ba zan ga samu naga rashi ba, wani irin solob’iyon Uba kuke so na zama? Allah ya kawowa y’ata nagartaccen Mijin da kowane Uba yake fata sai na masa butulci sabida wani karatun boko na banza da na wofi. Mutumin da ko y’ay’a d’ari yake so za’a ba shi a rana guda, duka ta tsallake ya ce Aysha ce ta masa Aysha yake son aure sai na zuba masa k’asa a ido, Saboda wata maganar banza da wofi. Ita ka’dai ce fa y’ata mace da nake fatan ta yi dace da Mijin k’warai.. ko yanzu yake so na tsame ta a boko na mata aure wallahil azeem na shiryawa haka, ba abinda kuma zai saka ni fasawa. Karatu dai idan ya ce zata yi a gidanta falillahil hamdihi idan ya hanata ma gaba d’aya wallahi ba zan tursasa shi ba. Saboda ku iyayen banza ne ku da zaku saka ta ta yarda ku rarrasheta ku ke sakata ta bijire min? To ku je ku yi na da ku a ga wanda zai ci riba…” Daga haka yaja bakinsa ya tsuke ya kuma wanke hannunsa ya tsoma cikin tuwo ya cigaba da ci. Fuskarsa a ha’de sosai alamar duk abinda ya fa’da har k’asan zuciyarsa hakan yake. Mami ta ture kwanon tuwon da muke ci ni da ita da Umma ta mik’e fuska a ha’de ta fice daga parlorn.
Jikina a sanyaye na mik’e zan bi ta Abba ya saka baki ya kira ni muryarsa a dake. “Dawo Ayshatu, zauna ki ci tuwonki, ba cutar da ke zan yi ba, har ga Allah alheri nake hango miki game da aurenki da Ahmad..” Na d’aga kai na ina wasa da zoben hannuna. “Ki kuma bu’de wayarki ki fara amfani da ita, na san ba zai cutar da ke ba. Ban kuma amince da duk wani tarkacen social media ba…” Na d’aga kaina don shima Ustaz garga’di da ya min kenan. Na san tunda suke ta jaddada min to social media d’in ba abu ba ne mai kyau. Cin tuwon kawai nake ba tare da ina fahimtar d’and’anonsa ba, don dai kada Abba ya yi magana ne na zage na ci tuwon kafin na mik’e cikin mutuwa jiki na haye sama. So nake na je naga Mami da halin da take ciki.
Jikina a sanyaye na murd’a k’ofar d’akinta don bata parlour kamar yarda ta saba zama. A saman gado na sameta hannayenta dafe da k’unci da alama ta yi zurfi cikin tunanin da take. Zama na yi daf da ita ina d’ora kaina a saman kafa’darta. Sai na ji ta saki ajiyar zuciya. Ta rungumoni sosai a jikinta tana furta “Aysha, yanzu kin amince d a auren da Abba zai miki?” K’asa na yi da kaina idona na zubar da k’walla. “Mami kema ki yi hak’uri please…” Janye jikinta ta yi tana sakin wani malalacin murmushi “Na yi hak’uri Aysha? Na yi hak’uri Ustaz ya cuceni ya raba ni da duk wani farin cikina? Ya kuma ruguza min da duk wani shirina a kan ki da na shekara da shekaru ina shiryawa?” Ta girgiza kai tana taune leb’enta ta furta “Wallahi bai isa ba, mu zuba ko ni ko shi?” K’asa na yi da kaina saboda ba zan iya sake cigaba da juriyar kallon idanun Mami ba, don wani abu nake gani a cikin idon… Zamewa ta yi ta kwanta tana mayar da numfashi idanunta a lumshe. “Tashi ki tafi AYSHA, ta shi ki wuce d’akinki…” Ta fa’da a zafafe da sauri kuwa na mik’e ba fice don ban saba ko na ce ban tab’a ganinta a irin wannan yanayin ba… na lura daf take da fara Aljannu…
Da safe har na shirya na gama shirin makaranta Mami bata tashi ba. Hakan yasa na nufi d’akinta ina nocking a hankali. A zafafe ta furta “Waye ne?” “Nice Mami…” ta bu’de k’ofar tana kallona idanunta kuwa da k’yar take lumshe su. Ta ja hannuna tana murzawa a hankali cikin wata irin murya ta furta “Ayshatu…” Na d’ago ina kallonta ta d’an sunkuyar da kai sai kuma ta saki hannun nawa. Tana sakin Malalacin murmushi ta furta “Har kin yi shirin makaranta?” Na d’aga mata kai “Ina kwana Mami?” Amsawa ta yi tana d’an ja baya ta furta “Wuce ki tafi AYSHA, ni ba abinda zaki ce min tunda kin zab’i farin cikin iyayenki a kaina. A jiya na yi takaicin rashin haihuwa da ni na haifeki da kaina na san ba zaki bujire min ba….” Kuka ne yazo min sosai ban san sanda na fa’da jikinta ba na saki wani irin kuka. Mami ta rungumeni sosai a jikinta ina jin yarda take sakin ajiyar zuciya. A kunne ta ra’da min “Kada ki bujire min Aysha, kada ki guje ni zan shiga wani hali AYSHA….” Da k’yar ta zame jikinta daga jikina ta juya bayanta tana furta “Je ki ki rufe min k’ofa…” Jikina a sanyaye na fice daga d’akin nata.
A kitchen na tarar da Umma na tana ta aikinta ita ka’dai. Sai na ji duk ban ji da’di ba don koda yaushe tare suke aikinsu da Mami. Da wayona dai ba zan tab’a cewa ga ranar da suka yi aiki ba tare ba. Kallo guda ta min ta d’auke kanta tana amsa gaisuwata. Na juya zan fice ta furta “Ba zaki k’arya ba ne?” “Umma na k’oshi…” Umma ta bi ni da kallo mai kama da harara tana furta “Ki yi ta k’oshin mana Aysha? Cikin wa? Kin zata ni d’in uwarki ce da zan ta bin ki ina lallab’aki, kin bi kin k’i ki kwantar da hankalinki balle na uwarki ya kwanta sai kace a kan ki aka fara auren early marriage, sanda Ubanki ya auro ni 15yrs nake, ban ma kai ki ba me ya same ni? Mahaifinki dai kaifi d’aya ne, ba mai saka shi ba mai hana shi don haka ki nutsu ki san abinda ki ke. Ban tab’a jin kan Fateemah da Abbanku sai a yanzu da take son ta bujire masa, me ye ribarki idan kin haddasa sab’ani a tsakaninsu? Na ce meye ribarki AYSHA?” Shiru na mata ina bulbular da hawaye. Me yasa Umma zata ga laifina ce mata na yi bana son Ustaz? Bata san nafi kowa son haka ba? Tashin hankalin Mami ne kawai bana so nake b’oye hakan a raina.. “wuce ki bani wuri, ki shirya bujire masa kece zaki wahala don kin san ko magagin mutuwa kike Ubanki sai ya sadaki da gidan mutumin nan…” Na ja k’afata na fice daga kitchen d’in zuciyata a k’untace ranar na isa makaranta.