Sashe 29
Naga Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da Asuba kuwa ina kunna wayata kiransa ya shigo. Na saki ajiyar zuciya na saka hannu na amsa kiran cikin matuk’ar farin ciki, don rabon da ya yi min kira irin wannan har na manta. “Hello Habeeby…” Na kira shi da sunan da ban tab’a kiransa da shi ba. Madadin ya amsa sai ji na yi ya yi k’aramin tsaki ya furta “Ina ki ka je jiya da daddare, ba kira wayarki a kashe?” Zuciyata ta wani yunk’oro da tsananin b’acin rai na ce “Ina kuwa zan je da daddare? Wace irin tambaya ce wannan barci nake ji shi yasa na kashe wayar na kwanta… na san ba kira zaka yi ba shi yasa ban ma saka a kai ba.” “Kada ki raina min hankali mana, ki mayar da ni wani sokon namiji wanda bai san abinda yake yi ba, ke…….”
D’if na kashe wayar da sauri, jin mamakin furucinsa, a muryarsa nake jin wani b’acin rai wanda na tabbatar har k’asan zuciyarsa yake. Ba zai yiwu na cigaba da waya da shi ba, don nima tawa zuciyar a hassale yake shi yasa na kashe. Na runtse idona ina jin wayar tana ta ringing kuma na san Ustaz ne don ringing d’insa daban ne. Hannu na saka na d’au wayar ba rubuta masa gajeran sak’o.
“Allah ya huci zuciyar manya, ka yi hak’uri Habibeey idan zuciyarka ta yi sanyi ka kira ni. Ina tura masa na kashe wayar gaba ‘d’aya cikin wani irin tashin hankali naji hawaye na zubo min daga idona. Me na yiwa Ustaz me zafi haka da nake hango jin haushina a tsakiyar k’wayar idonsa?
Ranar ne aka yi Dinnerr bikina a AMANI… Shima tsaf aka tsantsara min kwalliya ta cikin Black material wanda zab’in Ustazuna ne, kwalliyar ta min kyau matuk’a da gaske. Stone peach ne a jikin material d’in don haka aka min amfani da Shoe and clutch peach sai sark’ar wuyana ta zallar Zinare zubin English golden. Baa min kwalliya ba ranar saboda hawaye ya k’i barin idona ba kuma hawayen komai bane, sai na rabuwa da gidanmu Abba na Ummana, da Mami na. Ga su Ya Usman ma duk wai yau zamu yi ban kwana, zan tafi rayuwar da kowa yake gaya min sai hak’uri. Zuciyata ta yi rauni sosai musamman da aka kai ni wajen Abba mu yi sallama. Abba ya d’ago cikin jarumta ya saki murmushin da na tabbatar na k’arfin hali ne. Hannu yasa ya ya fito ni jikin sa. Muryarsa cike da k’arfin hali ya ce “Matso AYSHA ta….” Na matsa kuwa jikinsa na kafa kaina a saman cinyarsa ina zubar da wani irin hawaye. Hannu ya saka ya bubbuga baya na alamar rarrashe cikin wani irin furuci ya ce. “Ki yi hak’uri Ayshatu na, haka kowace mace ta gada kuma shine abin alfaharin ta. Aysha, ina son ki yiwa mijinki biyayya kwatankwacin biyayyar da Rabi’atul Adawiyya ta yiwa Mijinta, ko ki samawa zuri’ar gidanku k’ima da daraja a idanun Mijinki. Ba na son AYSHA ki yi abinda Mijin ki zai tsaneki har ta kai ga yazo yana dana sanin aurenki. Alhamdulillah ina alfahari da iyayenki mata ina so kuma ki yi koyi da su. Na fi son a fito min da gawar Ki daga gidan Ahmad Aysha, haka shine cikar burin Uba na gari, musamman da ke ke ka’dai ce d’iyata Mace da Allah ya bani. Soyayyar da nake miki ce ta saka na aurar da ke da k’ananun shekaru ba k’iyayya ba, Saboda na san Ahmad mutum ne na k’warai zai kuma rik’e min ke tsakaninsa da Allah. Ki kiyaye Ayshan Mami Allah ya miki albarka.” Ameen na ji jama’ar parlorn sun amsa Daga haka Abba ya ja hannuna ya damk’a min Alkur’ani ya saka min wata jaka mai kyau a gefena. “Alk’ur’ani ya zamo abokin hirarki, sallaya ta zama inda zaki sujjada ki kaiwa Allah kukanki, bana son kawo k’ara, mutuniyar kirki bata fiye kai k’arar Mijinta ba gudun b’ata masa suna. Kin ji ko?” Na d’aga kai ina jin zuciyata kamar zata tafasa saboda tsananin b’acin rai.
Ranar kam Ustaz k’in zuwa ya yi ya kai ni wajen dinner, kiran duniya ya k’i d’agawa k’arshe ma sai ya kashe wayar tasa gaba d’aya. Jan bakina na yi na tsuke ban gayawa kowa ba sai su Mami ne suka tafi dani wajen dinner.
Wannan shine labari na da duk wata soyayya da muka gudanar da Ustaz.
Hawayene ya gangaro daga idona na mik’e daga saman kujerar da nake ina bin d’akin Abba na da kallo. Tunani ne ya shiga yi min suntiri a zuciyata so nake na gano dalilin da yasa duk son da Ustaz yake min ya riki’de ya koma zazzafar k’iyayyar da ta kasa b’oyuwa a ransa har ta kai shi ga furta min kalmar saki a daren auren mu. Daren da Ustaz ya da’de yana gaya min ya ci buri iri iri a kansa. Burin ganin Aysharsa a zahirin Aysharsa ba tare da shamakin tufafi ba. Sai ga shi daren yazo mana a wani irin hagunce da namu burin. Menene sila? “MAMIN KI!” Na ji zuciyata ta amsa min a tsawace..
Da sauri na runtse idona ina girgiza kai da k’arfin gaske. Daidai sanda aka bu’de k’ofar d’akin aka shigo. Na dawo hayyacina ina binsu da kallo cikin dishi dishin idona. Yaya Muhammad, Ya Sadik, Ya Umar, fuskarsu a murtuke ba fara’a suke zubo min ido. Suka shigo cikin wani irin taku da yake nuna zallar b’acin ran da suke ciki. Zuciyata ta shiga bugu da k’arfin gaske na dinga bin su da kallo ina kallon yarda suka dogara k’afafunsu akan kujerar suka zagaye ni da idanunsu…
Wani irin kallo suke jifana da shi, wanda na rasa a mizanin da zan saka kallon nasu. Na san dai kallo ne na Allah wadaran halinki…
Sautin zuciyata ya sake bugu da k’arfin gaske jin Ya.Muhd ya kira sunana da sark’akkiyar muryarsa. “AYSHA! Gaya mana laifin me kika yiwa Ahmad ya sake ki a daren farko? Kada kice mana bakomai don hakan ma kin san ba zai yiwu ba. Ba auren k’iyayya aka muku ba, Ustaz kuma bai d’ora miki iddarsa ba balle a ce auren d’and’ano ya yi da ke? Me kika masa?” Ya fa’da a tsawace.
Hawaye ne kawai yake kwarara daga ido na. Na shiga masa rantsuwa da a idonsa ka’dai na san rantsuwa ta ba inda ta je. Na ba shi labarin abinda na sani dangane da canja min da Ustaz ya yi a kwanaki ka’dan da Suka rage na bikin mu.
“Mak’aryaciyar banza, wa kike tunanin zai yarda da wannan tatsuniyar taki? Ta yaya kike tunanin mutum ya aureki yana tsananin son ki Sannan ya sake ki a daren da aka d’aura muku aure? Dole akwai wani abu ki gaya min gaskiya kawai… kada ki bari zargin da nake a zuciyata ya tabbata don ni zuciyata na gaya min tabbas ke da uwarki sun san komai, Mami ba, tabbas akwai saka hannunta a cikin lamarin haka nake ji a raina….
Ji muka yi an turo k’ofar da k’arfin gaske, an shigo, idanuna suka fa’da cikin na Mami da suka ka’da suka yi jajur. “Umar! Ni kake zargi da mutuwar auren Aysha?” Ta furta a tsawace idanunta suna zubar da hawaye… Umar ya cije bakinsa yana jijjiga kai ya furta “Ai ba abin mamaki ba ne, tunda kowa ya san kina adawa da auren….” “Faruk!” Umma ta fa’da a tsawace tana nuna shi da yatsa. Tashin hankalin da kake son ka jawo mana kenan a gidan nan. Ta yaya kake tunanin Fateema zata cutar da Aysha ta hanyar kashe mata aure? Kada na sake ji… bana so wani irin zancen banza ne wannan..? Kana cikin hayyacinka kuwa…
Gani muka yi Mami ta juya zata fita daga ‘dakin, sai dai shigowar Abba ya hanata don da k’arfi ya turo k’ofar shima idanunsa akan Umma ya furta wai menene?” Nan Umma ta shiga ba shi labari Mami dai bata ce komai ba illa ficewa da ta yi tana hawaye. Madadin Abba ya yi fa’da sai naga ya girgiza kai ya kalli su Ya. Muhd ya furta “Ku tafi masallaci Muhammad an yi sallah.” Suka fice a hankali. Umma ta dubeshi yana zama yana danna waya ta ce “Amma ka barsu suka fita baka wa Umar fa’dan abinda ya yi ba?” Jingina ya yi da kujera yana lumshe idonsa ya furta “Nima ina tunanin da Umar yake….” Ba shiri Umma ta zauna tana furta “A’a Abban Aysha kada ka fara irin wannan maganar don Allah…” wani kallo ya mata kafin ya cije bakinsa. Ya furta “Ina zargi na ce, kuma tabbas idan na tabbatar da zargina wallahi sakinta zan yi, ina jiran feedback d’in Ahmad, mun yi waya da mahaifinsa ya gaya min su basu san labarin sakin ba, amma sun yi waya da Ahmad ya sanar masa yana airport d’in Abuja zai wuce egypt, amma Babansa ya dakatar da shi ya ce ya juyo lalle a daren nan zai zo ya gaya mana koma menene…” Umma jikinta a salub’e ta mik’e tana furta “Allah ya kyauta.” Ta bar ‘d’akin. abba ya sake d’agowa a karo na biyu yana kallona ya furta “Kin tabbata baki san komai ba?” Na d’aga masa kai na. Ya girgiza kansa shima ya mik’e ya fice daga d’akin. Tausayin kaina ya sake kamani. Kuka nake sosai ba wanda ya sake bi ta kaina, tun bayan da Umma ta shigo ta kawo min tea ta rutsa ni sai da na shanye. Sannan ta fice daga d’akin.
Har dare gidanmu tsit ba wani mai walwala, y’an biki tuni suka watse bayan an sanar musu ba wani abu bane, Ustaz ne tafiyar gaggawa ta same shi.
D’if na kashe wayar da sauri, jin mamakin furucinsa, a muryarsa nake jin wani b’acin rai wanda na tabbatar har k’asan zuciyarsa yake. Ba zai yiwu na cigaba da waya da shi ba, don nima tawa zuciyar a hassale yake shi yasa na kashe. Na runtse idona ina jin wayar tana ta ringing kuma na san Ustaz ne don ringing d’insa daban ne. Hannu na saka na d’au wayar ba rubuta masa gajeran sak’o.
“Allah ya huci zuciyar manya, ka yi hak’uri Habibeey idan zuciyarka ta yi sanyi ka kira ni. Ina tura masa na kashe wayar gaba ‘d’aya cikin wani irin tashin hankali naji hawaye na zubo min daga idona. Me na yiwa Ustaz me zafi haka da nake hango jin haushina a tsakiyar k’wayar idonsa?
Ranar ne aka yi Dinnerr bikina a AMANI… Shima tsaf aka tsantsara min kwalliya ta cikin Black material wanda zab’in Ustazuna ne, kwalliyar ta min kyau matuk’a da gaske. Stone peach ne a jikin material d’in don haka aka min amfani da Shoe and clutch peach sai sark’ar wuyana ta zallar Zinare zubin English golden. Baa min kwalliya ba ranar saboda hawaye ya k’i barin idona ba kuma hawayen komai bane, sai na rabuwa da gidanmu Abba na Ummana, da Mami na. Ga su Ya Usman ma duk wai yau zamu yi ban kwana, zan tafi rayuwar da kowa yake gaya min sai hak’uri. Zuciyata ta yi rauni sosai musamman da aka kai ni wajen Abba mu yi sallama. Abba ya d’ago cikin jarumta ya saki murmushin da na tabbatar na k’arfin hali ne. Hannu yasa ya ya fito ni jikin sa. Muryarsa cike da k’arfin hali ya ce “Matso AYSHA ta….” Na matsa kuwa jikinsa na kafa kaina a saman cinyarsa ina zubar da wani irin hawaye. Hannu ya saka ya bubbuga baya na alamar rarrashe cikin wani irin furuci ya ce. “Ki yi hak’uri Ayshatu na, haka kowace mace ta gada kuma shine abin alfaharin ta. Aysha, ina son ki yiwa mijinki biyayya kwatankwacin biyayyar da Rabi’atul Adawiyya ta yiwa Mijinta, ko ki samawa zuri’ar gidanku k’ima da daraja a idanun Mijinki. Ba na son AYSHA ki yi abinda Mijin ki zai tsaneki har ta kai ga yazo yana dana sanin aurenki. Alhamdulillah ina alfahari da iyayenki mata ina so kuma ki yi koyi da su. Na fi son a fito min da gawar Ki daga gidan Ahmad Aysha, haka shine cikar burin Uba na gari, musamman da ke ke ka’dai ce d’iyata Mace da Allah ya bani. Soyayyar da nake miki ce ta saka na aurar da ke da k’ananun shekaru ba k’iyayya ba, Saboda na san Ahmad mutum ne na k’warai zai kuma rik’e min ke tsakaninsa da Allah. Ki kiyaye Ayshan Mami Allah ya miki albarka.” Ameen na ji jama’ar parlorn sun amsa Daga haka Abba ya ja hannuna ya damk’a min Alkur’ani ya saka min wata jaka mai kyau a gefena. “Alk’ur’ani ya zamo abokin hirarki, sallaya ta zama inda zaki sujjada ki kaiwa Allah kukanki, bana son kawo k’ara, mutuniyar kirki bata fiye kai k’arar Mijinta ba gudun b’ata masa suna. Kin ji ko?” Na d’aga kai ina jin zuciyata kamar zata tafasa saboda tsananin b’acin rai.
Ranar kam Ustaz k’in zuwa ya yi ya kai ni wajen dinner, kiran duniya ya k’i d’agawa k’arshe ma sai ya kashe wayar tasa gaba d’aya. Jan bakina na yi na tsuke ban gayawa kowa ba sai su Mami ne suka tafi dani wajen dinner.
Wannan shine labari na da duk wata soyayya da muka gudanar da Ustaz.
Hawayene ya gangaro daga idona na mik’e daga saman kujerar da nake ina bin d’akin Abba na da kallo. Tunani ne ya shiga yi min suntiri a zuciyata so nake na gano dalilin da yasa duk son da Ustaz yake min ya riki’de ya koma zazzafar k’iyayyar da ta kasa b’oyuwa a ransa har ta kai shi ga furta min kalmar saki a daren auren mu. Daren da Ustaz ya da’de yana gaya min ya ci buri iri iri a kansa. Burin ganin Aysharsa a zahirin Aysharsa ba tare da shamakin tufafi ba. Sai ga shi daren yazo mana a wani irin hagunce da namu burin. Menene sila? “MAMIN KI!” Na ji zuciyata ta amsa min a tsawace..
Da sauri na runtse idona ina girgiza kai da k’arfin gaske. Daidai sanda aka bu’de k’ofar d’akin aka shigo. Na dawo hayyacina ina binsu da kallo cikin dishi dishin idona. Yaya Muhammad, Ya Sadik, Ya Umar, fuskarsu a murtuke ba fara’a suke zubo min ido. Suka shigo cikin wani irin taku da yake nuna zallar b’acin ran da suke ciki. Zuciyata ta shiga bugu da k’arfin gaske na dinga bin su da kallo ina kallon yarda suka dogara k’afafunsu akan kujerar suka zagaye ni da idanunsu…
Wani irin kallo suke jifana da shi, wanda na rasa a mizanin da zan saka kallon nasu. Na san dai kallo ne na Allah wadaran halinki…
Sautin zuciyata ya sake bugu da k’arfin gaske jin Ya.Muhd ya kira sunana da sark’akkiyar muryarsa. “AYSHA! Gaya mana laifin me kika yiwa Ahmad ya sake ki a daren farko? Kada kice mana bakomai don hakan ma kin san ba zai yiwu ba. Ba auren k’iyayya aka muku ba, Ustaz kuma bai d’ora miki iddarsa ba balle a ce auren d’and’ano ya yi da ke? Me kika masa?” Ya fa’da a tsawace.
Hawaye ne kawai yake kwarara daga ido na. Na shiga masa rantsuwa da a idonsa ka’dai na san rantsuwa ta ba inda ta je. Na ba shi labarin abinda na sani dangane da canja min da Ustaz ya yi a kwanaki ka’dan da Suka rage na bikin mu.
“Mak’aryaciyar banza, wa kike tunanin zai yarda da wannan tatsuniyar taki? Ta yaya kike tunanin mutum ya aureki yana tsananin son ki Sannan ya sake ki a daren da aka d’aura muku aure? Dole akwai wani abu ki gaya min gaskiya kawai… kada ki bari zargin da nake a zuciyata ya tabbata don ni zuciyata na gaya min tabbas ke da uwarki sun san komai, Mami ba, tabbas akwai saka hannunta a cikin lamarin haka nake ji a raina….
Ji muka yi an turo k’ofar da k’arfin gaske, an shigo, idanuna suka fa’da cikin na Mami da suka ka’da suka yi jajur. “Umar! Ni kake zargi da mutuwar auren Aysha?” Ta furta a tsawace idanunta suna zubar da hawaye… Umar ya cije bakinsa yana jijjiga kai ya furta “Ai ba abin mamaki ba ne, tunda kowa ya san kina adawa da auren….” “Faruk!” Umma ta fa’da a tsawace tana nuna shi da yatsa. Tashin hankalin da kake son ka jawo mana kenan a gidan nan. Ta yaya kake tunanin Fateema zata cutar da Aysha ta hanyar kashe mata aure? Kada na sake ji… bana so wani irin zancen banza ne wannan..? Kana cikin hayyacinka kuwa…
Gani muka yi Mami ta juya zata fita daga ‘dakin, sai dai shigowar Abba ya hanata don da k’arfi ya turo k’ofar shima idanunsa akan Umma ya furta wai menene?” Nan Umma ta shiga ba shi labari Mami dai bata ce komai ba illa ficewa da ta yi tana hawaye. Madadin Abba ya yi fa’da sai naga ya girgiza kai ya kalli su Ya. Muhd ya furta “Ku tafi masallaci Muhammad an yi sallah.” Suka fice a hankali. Umma ta dubeshi yana zama yana danna waya ta ce “Amma ka barsu suka fita baka wa Umar fa’dan abinda ya yi ba?” Jingina ya yi da kujera yana lumshe idonsa ya furta “Nima ina tunanin da Umar yake….” Ba shiri Umma ta zauna tana furta “A’a Abban Aysha kada ka fara irin wannan maganar don Allah…” wani kallo ya mata kafin ya cije bakinsa. Ya furta “Ina zargi na ce, kuma tabbas idan na tabbatar da zargina wallahi sakinta zan yi, ina jiran feedback d’in Ahmad, mun yi waya da mahaifinsa ya gaya min su basu san labarin sakin ba, amma sun yi waya da Ahmad ya sanar masa yana airport d’in Abuja zai wuce egypt, amma Babansa ya dakatar da shi ya ce ya juyo lalle a daren nan zai zo ya gaya mana koma menene…” Umma jikinta a salub’e ta mik’e tana furta “Allah ya kyauta.” Ta bar ‘d’akin. abba ya sake d’agowa a karo na biyu yana kallona ya furta “Kin tabbata baki san komai ba?” Na d’aga masa kai na. Ya girgiza kansa shima ya mik’e ya fice daga d’akin. Tausayin kaina ya sake kamani. Kuka nake sosai ba wanda ya sake bi ta kaina, tun bayan da Umma ta shigo ta kawo min tea ta rutsa ni sai da na shanye. Sannan ta fice daga d’akin.
Har dare gidanmu tsit ba wani mai walwala, y’an biki tuni suka watse bayan an sanar musu ba wani abu bane, Ustaz ne tafiyar gaggawa ta same shi.