← Book details Naga Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 30

Sashe 30

Naga Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 2 min read

Bayan Isha’i Iyayen Ahmad suka zo, Abba ya saka aka shiga da su parlorn sa na cikin gida. Ni dai gaba na kawai fa’duwa yake. Ba su wani da’de ba suka tafi. Sai ga Ya.Umar ya shigo da gudu yana furta “Umma fito Abba ba lafiya jikinsa rawa yake…” Da wani irin sauri Umma ta fito nima ban san sanda na fito daga d’akin Abba ba, na bi bayansu sitroom d’in Abban. Da wani irin tsawa Abba ya ce min “Fice Aysha haihuwar ki ba ta min rana ba, ku d’auka ku dubi hotunan nan ku ga irin b’atancin da cutarwar da ta yiwa nagartar gidan nan…..”

K’afafuna na rawa na zube a wajen ina kallon takardun da Ya Muhammad ya zubo min, ido na ware ganin ba abinda ya b’uya a hoton daga tsiraicina komai na a waje, k’irji and everything gefe guda wani mutum ne zaune kusa da ni yana shafa k’irjina…. Na zunduma wani Uban ihu, ina jin numfashina na neman barin gangar jikina…

Kash! Ina mai baku hak’uri, anan Book 1 ya k’are, sai dai ba zan yi jumurin kawo muku shi a kullum ba ta kafar whatsapp saboda wani dalili mai girman gaske, zan mayar da posting Litinin talata laraba da alhamis. Wato sau hu’du a sati. Sauran ranakun zan dinga posting a arewabooks. Y’an Arewabooks zasu dinga samu kullum In sha Allah. Dafatan za’a min uziri. Na gode sosai.

Masu so arewa ku yi searching @nazeefah ko kuyi searching sunan Book d’in. Labari yanzu aka fara AYSHA bata ga komai ba sai nan gaba. Akwai book 2 akwai Book 3. Ganin rayuwar yana gaba…

𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢✍️
Chapter 30 · 0% Book details