Sashe 28
Naga Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wata litinin abubuwan suka fara faruwa tsakanina da Ustaz, litinin d’in ana saura kwana hu’du a fara bikin. Na san anan yake shan ruwa in dai ya yi azimi. Shirin bikin bai hanani tashi na fara shirya masa abin shan ruwa ba, duk da yinin
Ranar sam bai kira ni ba. Nima kuma na shiga busy shi yasa ban kira shi ba. Azimin ne nima a bakina, amma haka na daure na fara shirin yi masa abin bu’de baki. Kunun kwakwa nake son masa, rashin ganin flavour ya saka ni fitowa daga kitchen d’in zuwa d’akin Mami. A bakin k’ofa na tsaya ganin ba Riga a jikinta tana shafa mai. “Shigo” na ji ta ce. Kamar ba zan shiga ba sai kuma na shiga kaina a k’asa. Tsaki ta zabga tana furta “wani munafuncin kuma kika tsuro da shi na tsayawa a bakin k’ofa?” Girgiza kai na nayi na ce “Aa naga kina saka kaya ne..” ta d’an yi tsaki kafin ta ja towel ta rufe k’irjinta “Yau kika saba gani na ba riga?” Na girgiza kai. “Flavour nake so Mami zan saka a kunun kwakwa..” na furta don son barin d’akin. “Yana gidan Uban Ahmad…” Mami ta furta cikin wata irin murya mai bayyana tsananin b’acin rai. Na d’ago ina kallonta idona yana kawo ruwa, ta iso gaba na cikin b’acin rai ta ce “Kike kallo na, na ce yana gidan Ubansa Sulaiman Sa’eed ba, ko da abinda zaki yi?” Hawaye ne kawai suka shiga zuraro min na saka k’afa da sauri na juya na bar d’akin jikina har rawa yake yi. Da k’yar na koma kitchen na k’arasa girkin a gaggauce na fa’da wanka. A raina ina jin ko me Mami zata yi ba zan rabu da Ahmad ba, amma fa zuciyata sai suya take yi.
Shima bayan magribar da yazo sai naga fuskarsa sam ba annuri, kallona kawai yake da k’yar ma ya amshi cup d’in da ba zuba masa Kunun, naga yana kurb’a a hankali kamar yana shan magani, idonsa da suka jirkita zuwa brown colour a kaina. Kawai sai na samu kaina da rushewa da kuka. Bai hana ni kukan ba kamar yarda bai fasa kallona ba, abin mamaki shima sai naga gangarowar hawaye a nasa idon. “Me ya sameki?” Ya ce cikin wata irin murya da yasa na d’ago ina kallonsa… ban amsa masa ba illa cigaba da kukan da na yi, ya saka hannunsa ya mik’o min “Zo ki gaya min…” Ji na yi ba zan iya masa musu ba na isa wajensa jikina a sanyaye na zube a gabansa. Durk’ushe wa ya yi a gabana ya d’ora cup d’in kunun a bakina.
A hankali na fara sipping. “Gaya min damuwarki?” Ya furta min a hankali. Na ce “Kai zan tambaya Ustaz, kai zan tambaya ji fa k’walla a idonka. Kana cikin damuwa yau gaba d’aya fa ko kira na baka yi ba…” ya saka hannunsa a goshina yana murzawa a hankali bayan ya jani jikinsa bakinsa ya saka a saman nawa yana lasar lips d’ina. Kafin ya lumshe idonsa yana cigaba da shafa goshin nawa ya furta “Ki yi shiru baki da lafiya ga kanki nan yayi zafi jijiyarsa ta tashi.” Ni da kaina na yarda ba ni da lafiya sai dai shima na ji nasa hannun shima ya ‘d’au zafin. Tafin hannunsa na kama na rungume a fuskata ina shak’ar k’amshin turarensa na furta “Ustaz kai ma jikinka zafi.” Idonsa a lumshe ya d’aga min kai. “Bani da lafiya ne AYSHA, wani irin ciwo zuciyata take min, ina kika je jiya da daddare, na kikkira wayarki baki d’aga ba?” Girgiza kai na yi ina mamakin furucinsa na furta “Ina zan je ban gaya maka ba, kaima ka san ba inda zan iya zuwa.” Still idonsa a lumshen ya sunkuya ya sunbaci tsinin hancina ya janye ni daga jikinsa sai naga ya mik’e yana kallona ya furta “Good night, idan kinga baki ji sauk’i ba ki fa’da a gida a kaiki asibiti..” Da mamaki na ce masa “Baka ci abincin ba ai?” “Am okay.” Ya fa’da yana fita da sauri kamar har a lokacin da k’walla a idonsa. Na mik’e zuciyata na bugawa na shige cikin d’aki duk hankalina a tashe.
Tun daga ranar Ustaz ya canja gaba d’aya, baya kira na sai dai na kira shi. Khadija ma har waya take min ta ce sun rasa kansa a gida. Amsa guda nake bata nace nima anan d’in ban san me ke damunsa ba. Sau tari ma idan na kira shi cewa yake yana busy ya kashe wayar. Tun jikina na bani bakomai har nazo na yarda tabbas akwai wani abin da Ustaz yake b’oye min.
Mami kuwa hankalinta kwance cikin zallar farin ciki take gudanar da shiryen shiryen bikin. Dukiya yake kashe min bata wasa ba, lamarin har ya fara firgita tunani na. Kullum kulawa take bani ta musamman. Na yi wani irin fitinannen kyau da kowa ya gani sai ya tanka.
Ranar da za’a kamu, sanda aka min kwalliya wallahi idan ba fa’da aka yi ba zata zaka yi India ce, Saboda fitinannen kyan da na yi a cikin Indian dress d’in da aka min complete kwalliyarsu. Jikina a rufe yake ruf. Duk da fuskata da walwala sai dai sab’anin zuciyata da take cike da takaicin Ustaz na rashin kulawa da ya kamata ya bani, musamman a irin wannan lokacin da amarya da ango suke buk’atar zuwansa.
Mai kwalliya na gama min Mami ta shigo wajen. Wani irin bu’de baki ta yi ta furta “Wow! Ya subhanallah Ayshata haka kika dawo? Fatabarakallahu Ahsanul
Khaleek’in, Tabbas Allah ya yi halitta…” murmushi kawai na saki ina kallon yarda Mamin ta rungume ni a jikinta ana d’aukarmu hotuna ko ta ina. Na so ace Ustaz ne a madadinta.
“Sai ki kirashi ku tafi.” Mami ta furta fuskarta a d’an tsuke kamar ba ita ta gama dariya yanzu ba. Wayata na d’auka na fara kiransa ta dinga ringing bai d’aga ba kamar yarda ya saba a kwanakin nan. A fusace na ji ya yi furucin “Wai menene?” Mamaki ya kamani jin tambayar rainin hankalin da ya yi min, na dinga kallon wayar ina son na tabbatar da gaske daga shine. “Na gama shiryawa” na furta a hankali. “Ki ce Mami ta kai ki.” Ya furta yana katse wayar. Ido na d’an ware kafin na sake danna wayar na tura masa text “Amma dai ka san kai ya kamata ka kai ni ko?” Ban zaci zai dawo min da amsa ba, sai naga ya turo min da “To ki jira…” na d’ago ina kallon Mami da suke magana da mai kwalliya ta kalleni itama ta ce “Ya taho?” Na d’aga kaina kawai ina furta “Eeh ga shi nan.”
Tun a mota nake kallon yanayin Ustaz d’ina tamkar ba shi ba, fuskarsa murtuk babu annuri ko ka’dan a cikinta, na zata zai yaba kwalliya ta sai dai ko kallona bai yi ba. Ya ja mota muka tafi bayan Asma ta shiga. Hankali ne tashe nake kallonsa na ce “Baka da lafiya ne Ustaz?” Bai ko kalleni ba balle ya amsa min, ya cigaba da driving zuwa inda ake gudanar da shirin. Shiru motar tafiya kawai muke kamar kurame sai sautin k’ur’an da yake cikin motar cikin suratun nisa’i.
Muna isa wajen Dinnerr Asma ta fita. Ni kuwa kasa fita na yi ina bin Ustaz da kallo da idanuwana da suke kawo ruwa. “Ya dai?” Ya furta yana d’an Cijan bakinsa da kawar da kai, na san kwallar da ke idonsa ce baya son na gani. Hannunsa kawai na kama k’am cikin nawa. Na furta “Gaya min ustaz, gaya min ko laifi na maka na baka hak’uri bana son irin wannan horon da kake min zuciyata ba zata ‘dauka ba…” cigaba ya yi da danna wayarsa idanunsa duk sun ka’da sun yi wani iri. “Baka da lafiya ko?” Na fa’da ina son lalubar k’wayar idonsa. A fusace ya ce “K’alau nake Ayshatu, just go and live me alone….” Kallonsa nake yi idonsa a runtse kafin na janye hannuna a hankali na fice daga motar idona na zubar da k’walla ban damu da b’acin kwalliyar ba damuwata sanin wani laifi na yiwa Ustazun Aysha..
𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️NA GA RAYUWA…21.
Ina neman alfarma Don Allah da Manzonsa 😭🤲 don Allah ku shiga link ɗin nan ku yi mana voting MIKIYA WRITERS ASSOCIATION
https://www.facebook.com/share/p/ChZaudpRhnBicHZ5/?mibextid=C7JYKg
Idan kun shiga zai nuna requesting ana yin approving sai ku danna mini don Allah.
Masoya Ustazun Aysha. A nuna mata kara… Daga kungiyata abar alfaharina. In dai kuna son na cigaba da rubutu cikin da’din rai…
Ganin irin yawan mutanen da suka zo wajen kamun biki na, ya wanke min duk wani b’acin rai na da bak’in cikin dake nuk’urk’usar zuciyata. Wani farin ciki ya ziyarce ni, da na tuna duka wa’dannan mutanen sun zo ne saboda ni. Zuciyata ta yi haske walwala da fara’ar fuskata suka dawo. Mai hoto ce ta dinga d’aukata duk inda na saka k’afa, har zuwa sanda na isa wajen zama na. K’awayena suna bina a baya. A haka na zauna ina ta sakin murmushi. Ki’dan larabawa ne kawai yake tashi a wajen, da wani irin k’amshin turaren wuta masu da’din gaske. Ba’a rawa kowa yana wajensa a zaune sai mai gabatar da shirye shiryen bikin ce kawai a tsaye a filin wajen, tana ta yiwa manyan bak’i barka da zuwa. Kowa yana zaune cikin aji kai daga gani ka san mutane ne masu aji da wanda ilimi ya ratsa su suka halarci wajen. Ba wani hayaniya kowa yana zaune a inda aka tanadar masa ya zauna ya hanyar ganin Table no. D’insa a card d’insa.
An ci an sha, kowa ya yi nak, an kuma yi barkwanci Malamai mata suka yi wa’azi sosai. Bayan tsawon lokaci aka tashi daga wajen. Dangin Ustaz ma sun zo sun kuma yi min kamu akan ku’di masu daraja. Ustaz ne ya mayar da ni gida bayan an tashi sai dai ko kallon arziki bai ha’dani da shi ba balle magana ta fatar baki. Tattarashi na yi na watsar don ni sam ban san wani laifi guda da na yi masa ba.
Sai sha biyun dare na kashe wayata saboda naga da gaske dai Ustaz bai kira ba.
Ranar sam bai kira ni ba. Nima kuma na shiga busy shi yasa ban kira shi ba. Azimin ne nima a bakina, amma haka na daure na fara shirin yi masa abin bu’de baki. Kunun kwakwa nake son masa, rashin ganin flavour ya saka ni fitowa daga kitchen d’in zuwa d’akin Mami. A bakin k’ofa na tsaya ganin ba Riga a jikinta tana shafa mai. “Shigo” na ji ta ce. Kamar ba zan shiga ba sai kuma na shiga kaina a k’asa. Tsaki ta zabga tana furta “wani munafuncin kuma kika tsuro da shi na tsayawa a bakin k’ofa?” Girgiza kai na nayi na ce “Aa naga kina saka kaya ne..” ta d’an yi tsaki kafin ta ja towel ta rufe k’irjinta “Yau kika saba gani na ba riga?” Na girgiza kai. “Flavour nake so Mami zan saka a kunun kwakwa..” na furta don son barin d’akin. “Yana gidan Uban Ahmad…” Mami ta furta cikin wata irin murya mai bayyana tsananin b’acin rai. Na d’ago ina kallonta idona yana kawo ruwa, ta iso gaba na cikin b’acin rai ta ce “Kike kallo na, na ce yana gidan Ubansa Sulaiman Sa’eed ba, ko da abinda zaki yi?” Hawaye ne kawai suka shiga zuraro min na saka k’afa da sauri na juya na bar d’akin jikina har rawa yake yi. Da k’yar na koma kitchen na k’arasa girkin a gaggauce na fa’da wanka. A raina ina jin ko me Mami zata yi ba zan rabu da Ahmad ba, amma fa zuciyata sai suya take yi.
Shima bayan magribar da yazo sai naga fuskarsa sam ba annuri, kallona kawai yake da k’yar ma ya amshi cup d’in da ba zuba masa Kunun, naga yana kurb’a a hankali kamar yana shan magani, idonsa da suka jirkita zuwa brown colour a kaina. Kawai sai na samu kaina da rushewa da kuka. Bai hana ni kukan ba kamar yarda bai fasa kallona ba, abin mamaki shima sai naga gangarowar hawaye a nasa idon. “Me ya sameki?” Ya ce cikin wata irin murya da yasa na d’ago ina kallonsa… ban amsa masa ba illa cigaba da kukan da na yi, ya saka hannunsa ya mik’o min “Zo ki gaya min…” Ji na yi ba zan iya masa musu ba na isa wajensa jikina a sanyaye na zube a gabansa. Durk’ushe wa ya yi a gabana ya d’ora cup d’in kunun a bakina.
A hankali na fara sipping. “Gaya min damuwarki?” Ya furta min a hankali. Na ce “Kai zan tambaya Ustaz, kai zan tambaya ji fa k’walla a idonka. Kana cikin damuwa yau gaba d’aya fa ko kira na baka yi ba…” ya saka hannunsa a goshina yana murzawa a hankali bayan ya jani jikinsa bakinsa ya saka a saman nawa yana lasar lips d’ina. Kafin ya lumshe idonsa yana cigaba da shafa goshin nawa ya furta “Ki yi shiru baki da lafiya ga kanki nan yayi zafi jijiyarsa ta tashi.” Ni da kaina na yarda ba ni da lafiya sai dai shima na ji nasa hannun shima ya ‘d’au zafin. Tafin hannunsa na kama na rungume a fuskata ina shak’ar k’amshin turarensa na furta “Ustaz kai ma jikinka zafi.” Idonsa a lumshe ya d’aga min kai. “Bani da lafiya ne AYSHA, wani irin ciwo zuciyata take min, ina kika je jiya da daddare, na kikkira wayarki baki d’aga ba?” Girgiza kai na yi ina mamakin furucinsa na furta “Ina zan je ban gaya maka ba, kaima ka san ba inda zan iya zuwa.” Still idonsa a lumshen ya sunkuya ya sunbaci tsinin hancina ya janye ni daga jikinsa sai naga ya mik’e yana kallona ya furta “Good night, idan kinga baki ji sauk’i ba ki fa’da a gida a kaiki asibiti..” Da mamaki na ce masa “Baka ci abincin ba ai?” “Am okay.” Ya fa’da yana fita da sauri kamar har a lokacin da k’walla a idonsa. Na mik’e zuciyata na bugawa na shige cikin d’aki duk hankalina a tashe.
Tun daga ranar Ustaz ya canja gaba d’aya, baya kira na sai dai na kira shi. Khadija ma har waya take min ta ce sun rasa kansa a gida. Amsa guda nake bata nace nima anan d’in ban san me ke damunsa ba. Sau tari ma idan na kira shi cewa yake yana busy ya kashe wayar. Tun jikina na bani bakomai har nazo na yarda tabbas akwai wani abin da Ustaz yake b’oye min.
Mami kuwa hankalinta kwance cikin zallar farin ciki take gudanar da shiryen shiryen bikin. Dukiya yake kashe min bata wasa ba, lamarin har ya fara firgita tunani na. Kullum kulawa take bani ta musamman. Na yi wani irin fitinannen kyau da kowa ya gani sai ya tanka.
Ranar da za’a kamu, sanda aka min kwalliya wallahi idan ba fa’da aka yi ba zata zaka yi India ce, Saboda fitinannen kyan da na yi a cikin Indian dress d’in da aka min complete kwalliyarsu. Jikina a rufe yake ruf. Duk da fuskata da walwala sai dai sab’anin zuciyata da take cike da takaicin Ustaz na rashin kulawa da ya kamata ya bani, musamman a irin wannan lokacin da amarya da ango suke buk’atar zuwansa.
Mai kwalliya na gama min Mami ta shigo wajen. Wani irin bu’de baki ta yi ta furta “Wow! Ya subhanallah Ayshata haka kika dawo? Fatabarakallahu Ahsanul
Khaleek’in, Tabbas Allah ya yi halitta…” murmushi kawai na saki ina kallon yarda Mamin ta rungume ni a jikinta ana d’aukarmu hotuna ko ta ina. Na so ace Ustaz ne a madadinta.
“Sai ki kirashi ku tafi.” Mami ta furta fuskarta a d’an tsuke kamar ba ita ta gama dariya yanzu ba. Wayata na d’auka na fara kiransa ta dinga ringing bai d’aga ba kamar yarda ya saba a kwanakin nan. A fusace na ji ya yi furucin “Wai menene?” Mamaki ya kamani jin tambayar rainin hankalin da ya yi min, na dinga kallon wayar ina son na tabbatar da gaske daga shine. “Na gama shiryawa” na furta a hankali. “Ki ce Mami ta kai ki.” Ya furta yana katse wayar. Ido na d’an ware kafin na sake danna wayar na tura masa text “Amma dai ka san kai ya kamata ka kai ni ko?” Ban zaci zai dawo min da amsa ba, sai naga ya turo min da “To ki jira…” na d’ago ina kallon Mami da suke magana da mai kwalliya ta kalleni itama ta ce “Ya taho?” Na d’aga kaina kawai ina furta “Eeh ga shi nan.”
Tun a mota nake kallon yanayin Ustaz d’ina tamkar ba shi ba, fuskarsa murtuk babu annuri ko ka’dan a cikinta, na zata zai yaba kwalliya ta sai dai ko kallona bai yi ba. Ya ja mota muka tafi bayan Asma ta shiga. Hankali ne tashe nake kallonsa na ce “Baka da lafiya ne Ustaz?” Bai ko kalleni ba balle ya amsa min, ya cigaba da driving zuwa inda ake gudanar da shirin. Shiru motar tafiya kawai muke kamar kurame sai sautin k’ur’an da yake cikin motar cikin suratun nisa’i.
Muna isa wajen Dinnerr Asma ta fita. Ni kuwa kasa fita na yi ina bin Ustaz da kallo da idanuwana da suke kawo ruwa. “Ya dai?” Ya furta yana d’an Cijan bakinsa da kawar da kai, na san kwallar da ke idonsa ce baya son na gani. Hannunsa kawai na kama k’am cikin nawa. Na furta “Gaya min ustaz, gaya min ko laifi na maka na baka hak’uri bana son irin wannan horon da kake min zuciyata ba zata ‘dauka ba…” cigaba ya yi da danna wayarsa idanunsa duk sun ka’da sun yi wani iri. “Baka da lafiya ko?” Na fa’da ina son lalubar k’wayar idonsa. A fusace ya ce “K’alau nake Ayshatu, just go and live me alone….” Kallonsa nake yi idonsa a runtse kafin na janye hannuna a hankali na fice daga motar idona na zubar da k’walla ban damu da b’acin kwalliyar ba damuwata sanin wani laifi na yiwa Ustazun Aysha..
𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️NA GA RAYUWA…21.
Ina neman alfarma Don Allah da Manzonsa 😭🤲 don Allah ku shiga link ɗin nan ku yi mana voting MIKIYA WRITERS ASSOCIATION
https://www.facebook.com/share/p/ChZaudpRhnBicHZ5/?mibextid=C7JYKg
Idan kun shiga zai nuna requesting ana yin approving sai ku danna mini don Allah.
Masoya Ustazun Aysha. A nuna mata kara… Daga kungiyata abar alfaharina. In dai kuna son na cigaba da rubutu cikin da’din rai…
Ganin irin yawan mutanen da suka zo wajen kamun biki na, ya wanke min duk wani b’acin rai na da bak’in cikin dake nuk’urk’usar zuciyata. Wani farin ciki ya ziyarce ni, da na tuna duka wa’dannan mutanen sun zo ne saboda ni. Zuciyata ta yi haske walwala da fara’ar fuskata suka dawo. Mai hoto ce ta dinga d’aukata duk inda na saka k’afa, har zuwa sanda na isa wajen zama na. K’awayena suna bina a baya. A haka na zauna ina ta sakin murmushi. Ki’dan larabawa ne kawai yake tashi a wajen, da wani irin k’amshin turaren wuta masu da’din gaske. Ba’a rawa kowa yana wajensa a zaune sai mai gabatar da shirye shiryen bikin ce kawai a tsaye a filin wajen, tana ta yiwa manyan bak’i barka da zuwa. Kowa yana zaune cikin aji kai daga gani ka san mutane ne masu aji da wanda ilimi ya ratsa su suka halarci wajen. Ba wani hayaniya kowa yana zaune a inda aka tanadar masa ya zauna ya hanyar ganin Table no. D’insa a card d’insa.
An ci an sha, kowa ya yi nak, an kuma yi barkwanci Malamai mata suka yi wa’azi sosai. Bayan tsawon lokaci aka tashi daga wajen. Dangin Ustaz ma sun zo sun kuma yi min kamu akan ku’di masu daraja. Ustaz ne ya mayar da ni gida bayan an tashi sai dai ko kallon arziki bai ha’dani da shi ba balle magana ta fatar baki. Tattarashi na yi na watsar don ni sam ban san wani laifi guda da na yi masa ba.
Sai sha biyun dare na kashe wayata saboda naga da gaske dai Ustaz bai kira ba.