Sashe 17
Naga Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Tsaf na shirya musu table d’in duk zuciyata ba da’di balle ganin tunda suka shige d’aki basu sake fitowa ba wai bata son k’amshin kayan miya. Mijinta sai wani lallab’ata yake. Haushi ma abin ya bani don haka bayan na yi wanka kawai na fita k’aramin parlorn na kwanta. Ina kallon wani Korean series. Anty Khadija da Ya Muhd suka shigo hannunsu sark’afe cikin na juna sai wani janta yake a jiki, ita Kuma tana sake narke masa. Kunya da takaicin su ma duk suka ha’du suka sake jagule min zuciya ta. Khadija na kallona ta furta “Sannu Aysha..” na amsa mata ina mayar da kaina na kwanta. “My love wallahi duk jikina ciwo yake, so nake ka yi min tausa…” Gani na yi kawai ya sunkuya ya ‘dagata cak tana Zillo tana komai ya fice da ita kamar Babyn roba.
Lumshe idona na yi ina tunanin dama nice da Ustaz a haka, da na tabbata ba wani da zai kai ni farin ciki a duniya. Sai kawai na samu kaina da zurarowar hawaye. K’amshin turarensa da na dinga ji yana sake yawaita ne ya saka ni bu’de lumsassun idanuna…. Da wani irin sauri na mik’e ganin Ustaz ne da Ya Muhd a parlorn. Ustaz d’in a zaune idanunsa akan wayarsa. Hula ce kawai a kaina, itama ta zame don haka gashi na ya bayyana sosai. Kayan jikina kuwa T.shirt ce da ta d’an kamani ka’dan sai siket. Ido na dinga warowa ina k’ank’ame jikina. Sai na lura Ustaz ko kallona bai yi ba, ya cigaba da hirarsu da Yaya Muhd, kamar ma basu san ina wajen ba. “Bari na kawo maka ruwa” Ya Muhd ya mik’ewa yana ficewa. Sai sannan na furta “Ya zaka shigo ba sallama, ai dai ba kyau shiga gidan mutane ba sallama, ga shi nan ka shigo ko Hijab babu a jikina…” Wani irin kallo ya min. Kafin naga ya ‘d’auke kansa ya mayar kan waya ya furta “Ba wajenki na zo ba, kuma mai gidan ne ya bani izinin shigowa.” Raina ne ya sake b’aci a kufule na ce “Sai ka tashi ka fita, ina son zan wuce cikin gida…” “Na hanaki ne?” Ya furta yana zuba min narkakkun idanunsa.. Turo bakina na yi sai ga Ya Muhd ya shigo yana kallona “Tashi ki samo masa snacks a kitchen Malama…” Ji na yi kamar na yi ihu. Na kalleshi na ce “To ka bani Hijab d’ina a cikin gida…” Tsaki Ya Muhd ya yi kafin ya fice sai ga shi ya dawo da Hijab ‘din ya hurga min. Ina kallo Ustaz ya ‘dan tab’e bakinsa na zura Hijabin na fice da sauri. A kitchen na tsaya ina mayar da ajiyar numfashi dafatan Allah yasa Ustaz aurena yazo sake nema.. Ban dawo daga hayyacina ba sai da Ya Muhd ya shigo kitchen d’in yana wurga min harara ya furta “Ki zuba abinci ki kai masa Malama ki ha’da da snacks.” Ya fice da sauri.
Na sauke ajiyar zuciya. Na ha’da abincin da snacks d’in sannan na shiga d’akin da yake zuciyata na wani irin bugawa. Har na ajiye abincin bai d’ago ba. Na ja na tsaya don na kasa fita daga sitroom d’in. “Zuba ka’dan.” Ya furta cikin wata irin husky voice. Kamar ba zan zuba ba, sai dai na zuba tunda neman sulhu nake. Na ajiye akan table ya d’ago yana kallona kafin ya d’au abincin ya tab’e bakinsa. Na rasa dalilin wannan tab’e baki don haka na fara kallon jikina ko wani abin ya gani ban ga komai. Don haka na koma kujera na zauna. “Ki tashi ki koma ba wajenki na zo ba..” Da wani irin zafin rai na ‘dago ina kallonsa sai naga shi ko kallona ba ya yi tuwonsa kawai yake ci. Haushi ya kamani na mik’e da sauri zan fice daga ‘dakin. Na ji muryarsa a waya yana furta “Aysha, zo ku gaisa da zab’in alheri da Allah ya min, ga matar da za’a aura min aure da ita jibi….” Wani irin rawa jikina ya fara na juya da sauri don ganin matar da yake nuna min a vedio call. Zuciyata ce kawai bata fito ba, Saboda tashin hankali. Ya mik’a min wayar ba tare da ya kalleni ba. Take hankali yazo min kada a yi abin kunya na karb’e wayar ina kallon kyakykyawar yarinyar a cikin waya sai sakar min murmushi take. Yarinya kamar ita ta k’era kanta fara jajir da ita. Idan ma zata girmeni da ka’dan ne. “Sannu Aysha..” ta furta cikin zak’in muryarta. Kokawa na dinga yi da numfashi na na ja iska da k’yar na fesar ina k’ak’aro murmushi na ce “Sannunki…” ta lumshe ido tana furta “Yaushe zamu ha’du ki taya ni shirin biki?” Ji nayi kamar na k’unduma mata zagi. Na ha’diye wani abu da ya tsaya min a mak’oshi na ce “Ki yi hak’uri ina school ba ni da time, Allah ya sanya alheri..” Daga haka na mik’a masa wayar da sauri, ina jin zuciyata na wani irin hantsilowa. Bai karb’i wayar ba ya nuna min gefensa “Ajiye min anan, kin ga zab’in da Allah ya yi min ko? Wani baya auren matar wani, she is my cousin jibi za’a d’aura mana aure don a shekaruna ba zan iya jiranki wani degree ba, duk sanda kika gama degree d’in idan kina da niyyar aure na the door is open…” Ya fa’da yana kurb’ar lemo da min kallon da na tabbatar na rainin hankali ne. “Ba wani aurenka da zan yi, ce maka aka yi ni kuma kwantai zan yi da zan auri Mijin wata, ragowar wata Allah ya kiyaye Mijina zan samu Wallahi nima dallele na aura…” na furta ina huci kamar wacce ta yi tsere. Murmushi ya saki yana yamutsa fuskarsa ya furta “Allah ko? Amma dai kin san ba zaki samu wanda ya fi ni ba… Idan haka kika zab’a Ai shikkenan, ina fatan ita dai kin ganta idan bata fi ki ba, ke ba zaki fita ba…” Ya ‘d’au key d’insa yana furta ki turo Min Muhammad zan ba shi Invitation card d’in Abba ya kai masa…..” “Ba zan turo shi ba ‘din…” na furta kai tsaye idona na cikin nasa, duk wata shakkarsa da nake ji ranar ta kau, Saboda tsananin kishi da ya rufe min ido na. Murmushi ya saki ya furta “Bakomai, bari na kira shi a waya…” Cije leb’ena na yi ina ji yana furta “Muhammad idan ba damuwa d’an fito na baka cards d’in Abba na d’aurin aure na special guests…..” Daga haka ya saka kai ya fice ya bar ni a tsaye kamar statue gaba d’aya naji duniyar na juya min na runtse idonsa sai ga wasu k’walla masu turiri sun fara zubo min.. fuskar budurwarsa still a cikin
Idanuwana……
𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️[8/5, 1:21 PM] Nazeefah Nashe: https://chat.whatsapp.com/HfGu1Pozgx9IxjCYqW7ZCZ
NA GA RAYUWA♥︎♥︎♥︎
𝒩𝒶𝓏ℯℯ𝒻𝒶𝒽 𝒩𝒶𝓈𝒽ℯ★✍️
Free Book.. MIKIYA WRITERS ASSOCIATION
Arewabooks @nazeefah
https://chat.whatsapp.com/HfGu1Pozgx9IxjCYqW7ZCZ
Wattpad@Nazeefah381
08033748387.
★★★★★ 𝒫𝒶ℊℯ 13
Tabbas bata inda zan ha’da kaina da matar da zai aura, ta fi ni komai kyau ilimi wayewa, da kuma gata, daga ganin gidansu inda ta d’au hoton in dai ba y’ar feck life ba ce to na san Ubanta yafi Abba ku’di nesa ba kusa ba. Me ya ja min? Na ce na fasa auren Ustaz gashi nan na jawowa kai na sakiyar da ba ruwa.
Da k’yar na mik’e na fita cikin gida, daidai lokacin da na ji Motar Ustaz ta fita daga gidan a guje. Na lek’a ta window sai naga Yaya Muhd ya shigo gidan . Fuskarsa a ha’de yake kallona. Kafin naga ya yi k’aramin tsaki ya shige bedroom d’insa. Da alama haushina yake ji ta yarda nayi watsi da duk abinda suke so na zab’i farin cikin Mami fiye da nasu. Wayata na jawo na fara kiran Ustaz da sauri amma wayar na ringing Ustaz bai ‘d’auka ba. Na ja tsaki ina cilla wayar kan kujera tare da zama dab’ar ina rik’e kaina da naji yana sara min da k’arfin gaske. Idona na lumshe amma still Ustaz da Amaryarsa nake hangowa a wani yanayi na soyayya. Zuciyata ta dinga bugu da k’arfin gaske. Wasu hawaye masu zafi suka dinga zubo min. Ban san sanda na ja wayar na danna masa msg ba. “Ka ‘d’aga wayar magana za
Mu yi….” In seconds ya dawo min da amsa “It’s too late, ki yi barci zan yi magana da safe, yanzu muna discussing da amaryata ne.” Na yi cilli da wayar ina jin wani d’aci har a mak’wagoro na. Cije leb’e na kawai nake yi ina mamakin wulk’ancin da Ustaz yake son ya fara min.
Da dai naga babu sarki sai Allah, sai kawai na mik’e da sauri na nufi bedroom ‘din da nake, direct washroom na shige na sakarwa kaina shower da kayana a jiki da komai, burina naji abinda nake ji ‘din ya ragu. Sai dai ba abinda ya ragun daga zafin zuciya da nake ji. Na ‘d’auro alwala na shiga sallah ba ji ba gani…
Lumshe idona na yi ina tunanin dama nice da Ustaz a haka, da na tabbata ba wani da zai kai ni farin ciki a duniya. Sai kawai na samu kaina da zurarowar hawaye. K’amshin turarensa da na dinga ji yana sake yawaita ne ya saka ni bu’de lumsassun idanuna…. Da wani irin sauri na mik’e ganin Ustaz ne da Ya Muhd a parlorn. Ustaz d’in a zaune idanunsa akan wayarsa. Hula ce kawai a kaina, itama ta zame don haka gashi na ya bayyana sosai. Kayan jikina kuwa T.shirt ce da ta d’an kamani ka’dan sai siket. Ido na dinga warowa ina k’ank’ame jikina. Sai na lura Ustaz ko kallona bai yi ba, ya cigaba da hirarsu da Yaya Muhd, kamar ma basu san ina wajen ba. “Bari na kawo maka ruwa” Ya Muhd ya mik’ewa yana ficewa. Sai sannan na furta “Ya zaka shigo ba sallama, ai dai ba kyau shiga gidan mutane ba sallama, ga shi nan ka shigo ko Hijab babu a jikina…” Wani irin kallo ya min. Kafin naga ya ‘d’auke kansa ya mayar kan waya ya furta “Ba wajenki na zo ba, kuma mai gidan ne ya bani izinin shigowa.” Raina ne ya sake b’aci a kufule na ce “Sai ka tashi ka fita, ina son zan wuce cikin gida…” “Na hanaki ne?” Ya furta yana zuba min narkakkun idanunsa.. Turo bakina na yi sai ga Ya Muhd ya shigo yana kallona “Tashi ki samo masa snacks a kitchen Malama…” Ji na yi kamar na yi ihu. Na kalleshi na ce “To ka bani Hijab d’ina a cikin gida…” Tsaki Ya Muhd ya yi kafin ya fice sai ga shi ya dawo da Hijab ‘din ya hurga min. Ina kallo Ustaz ya ‘dan tab’e bakinsa na zura Hijabin na fice da sauri. A kitchen na tsaya ina mayar da ajiyar numfashi dafatan Allah yasa Ustaz aurena yazo sake nema.. Ban dawo daga hayyacina ba sai da Ya Muhd ya shigo kitchen d’in yana wurga min harara ya furta “Ki zuba abinci ki kai masa Malama ki ha’da da snacks.” Ya fice da sauri.
Na sauke ajiyar zuciya. Na ha’da abincin da snacks d’in sannan na shiga d’akin da yake zuciyata na wani irin bugawa. Har na ajiye abincin bai d’ago ba. Na ja na tsaya don na kasa fita daga sitroom d’in. “Zuba ka’dan.” Ya furta cikin wata irin husky voice. Kamar ba zan zuba ba, sai dai na zuba tunda neman sulhu nake. Na ajiye akan table ya d’ago yana kallona kafin ya d’au abincin ya tab’e bakinsa. Na rasa dalilin wannan tab’e baki don haka na fara kallon jikina ko wani abin ya gani ban ga komai. Don haka na koma kujera na zauna. “Ki tashi ki koma ba wajenki na zo ba..” Da wani irin zafin rai na ‘dago ina kallonsa sai naga shi ko kallona ba ya yi tuwonsa kawai yake ci. Haushi ya kamani na mik’e da sauri zan fice daga ‘dakin. Na ji muryarsa a waya yana furta “Aysha, zo ku gaisa da zab’in alheri da Allah ya min, ga matar da za’a aura min aure da ita jibi….” Wani irin rawa jikina ya fara na juya da sauri don ganin matar da yake nuna min a vedio call. Zuciyata ce kawai bata fito ba, Saboda tashin hankali. Ya mik’a min wayar ba tare da ya kalleni ba. Take hankali yazo min kada a yi abin kunya na karb’e wayar ina kallon kyakykyawar yarinyar a cikin waya sai sakar min murmushi take. Yarinya kamar ita ta k’era kanta fara jajir da ita. Idan ma zata girmeni da ka’dan ne. “Sannu Aysha..” ta furta cikin zak’in muryarta. Kokawa na dinga yi da numfashi na na ja iska da k’yar na fesar ina k’ak’aro murmushi na ce “Sannunki…” ta lumshe ido tana furta “Yaushe zamu ha’du ki taya ni shirin biki?” Ji nayi kamar na k’unduma mata zagi. Na ha’diye wani abu da ya tsaya min a mak’oshi na ce “Ki yi hak’uri ina school ba ni da time, Allah ya sanya alheri..” Daga haka na mik’a masa wayar da sauri, ina jin zuciyata na wani irin hantsilowa. Bai karb’i wayar ba ya nuna min gefensa “Ajiye min anan, kin ga zab’in da Allah ya yi min ko? Wani baya auren matar wani, she is my cousin jibi za’a d’aura mana aure don a shekaruna ba zan iya jiranki wani degree ba, duk sanda kika gama degree d’in idan kina da niyyar aure na the door is open…” Ya fa’da yana kurb’ar lemo da min kallon da na tabbatar na rainin hankali ne. “Ba wani aurenka da zan yi, ce maka aka yi ni kuma kwantai zan yi da zan auri Mijin wata, ragowar wata Allah ya kiyaye Mijina zan samu Wallahi nima dallele na aura…” na furta ina huci kamar wacce ta yi tsere. Murmushi ya saki yana yamutsa fuskarsa ya furta “Allah ko? Amma dai kin san ba zaki samu wanda ya fi ni ba… Idan haka kika zab’a Ai shikkenan, ina fatan ita dai kin ganta idan bata fi ki ba, ke ba zaki fita ba…” Ya ‘d’au key d’insa yana furta ki turo Min Muhammad zan ba shi Invitation card d’in Abba ya kai masa…..” “Ba zan turo shi ba ‘din…” na furta kai tsaye idona na cikin nasa, duk wata shakkarsa da nake ji ranar ta kau, Saboda tsananin kishi da ya rufe min ido na. Murmushi ya saki ya furta “Bakomai, bari na kira shi a waya…” Cije leb’ena na yi ina ji yana furta “Muhammad idan ba damuwa d’an fito na baka cards d’in Abba na d’aurin aure na special guests…..” Daga haka ya saka kai ya fice ya bar ni a tsaye kamar statue gaba d’aya naji duniyar na juya min na runtse idonsa sai ga wasu k’walla masu turiri sun fara zubo min.. fuskar budurwarsa still a cikin
Idanuwana……
𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️[8/5, 1:21 PM] Nazeefah Nashe: https://chat.whatsapp.com/HfGu1Pozgx9IxjCYqW7ZCZ
NA GA RAYUWA♥︎♥︎♥︎
𝒩𝒶𝓏ℯℯ𝒻𝒶𝒽 𝒩𝒶𝓈𝒽ℯ★✍️
Free Book.. MIKIYA WRITERS ASSOCIATION
Arewabooks @nazeefah
https://chat.whatsapp.com/HfGu1Pozgx9IxjCYqW7ZCZ
Wattpad@Nazeefah381
08033748387.
★★★★★ 𝒫𝒶ℊℯ 13
Tabbas bata inda zan ha’da kaina da matar da zai aura, ta fi ni komai kyau ilimi wayewa, da kuma gata, daga ganin gidansu inda ta d’au hoton in dai ba y’ar feck life ba ce to na san Ubanta yafi Abba ku’di nesa ba kusa ba. Me ya ja min? Na ce na fasa auren Ustaz gashi nan na jawowa kai na sakiyar da ba ruwa.
Da k’yar na mik’e na fita cikin gida, daidai lokacin da na ji Motar Ustaz ta fita daga gidan a guje. Na lek’a ta window sai naga Yaya Muhd ya shigo gidan . Fuskarsa a ha’de yake kallona. Kafin naga ya yi k’aramin tsaki ya shige bedroom d’insa. Da alama haushina yake ji ta yarda nayi watsi da duk abinda suke so na zab’i farin cikin Mami fiye da nasu. Wayata na jawo na fara kiran Ustaz da sauri amma wayar na ringing Ustaz bai ‘d’auka ba. Na ja tsaki ina cilla wayar kan kujera tare da zama dab’ar ina rik’e kaina da naji yana sara min da k’arfin gaske. Idona na lumshe amma still Ustaz da Amaryarsa nake hangowa a wani yanayi na soyayya. Zuciyata ta dinga bugu da k’arfin gaske. Wasu hawaye masu zafi suka dinga zubo min. Ban san sanda na ja wayar na danna masa msg ba. “Ka ‘d’aga wayar magana za
Mu yi….” In seconds ya dawo min da amsa “It’s too late, ki yi barci zan yi magana da safe, yanzu muna discussing da amaryata ne.” Na yi cilli da wayar ina jin wani d’aci har a mak’wagoro na. Cije leb’e na kawai nake yi ina mamakin wulk’ancin da Ustaz yake son ya fara min.
Da dai naga babu sarki sai Allah, sai kawai na mik’e da sauri na nufi bedroom ‘din da nake, direct washroom na shige na sakarwa kaina shower da kayana a jiki da komai, burina naji abinda nake ji ‘din ya ragu. Sai dai ba abinda ya ragun daga zafin zuciya da nake ji. Na ‘d’auro alwala na shiga sallah ba ji ba gani…