Sashe 15
Naga Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zuciyata kawai bugu take, musamman da na ji k’amshin turaren Ustaz ya mamaye sitroom d’in. Na yi sallama can k’asan mak’oshi. Shima a k’asan mak’oshin ya amsa yana sakin ajiyar zuciyar da tasa na d’ago na kalleshi. Jallabiya ce bak’a wuluk a jikinsa, yau bai saka Alkyabba ba. Kansa dai da farin Ihrami. Idanunsa sanye da farin glass da ya k’ara fito da kyan fuskarsa. “Shigo ki zauna..” Kamar ba zan shiga ba. Sai dai na shiga na zauna a kujerar da take nesa da shi. “Dawo wannan kujerar bana son magana da k’arfi, I feel headache zuwan na dole ne..” Na kalli kujerar da take kallon tasa na tashi na koma na zauna fuskata a tsuke ina wasa da yatsun hannuna. Shiru ya yi kansa a k’asa kafin na ji muryarsa mai cike da rauni yana furta “Ba gaisuwa AYSHA?” Sai na ji kunya ta kamani na d’ago kamar dole na ce “Ina wuni?” Bai amsa ba, wani kallo kawai yake jifana da shi da yasa yanayin jikinsa sauyawa, sai naga ya lumshe ido yana murza goshinsa ya furta “Gaya min laifina Ayshatu? Kike hukunta ni da wannan sigar, na kira waya kin yi rejecting text no answer, makaranta kin k’i zuwa, gaya min me ya faru?” Shiru na masa kawai idanuna na zubar da hawaye da zan iya a lokacin kai tsaye zan furta masa ya janye maganar aurena, amma wallahi na kasa ya min wani irin kwarjini da ba zan iya kallon idanunsa na furta masa hakan ba. Gashi a k’asan zuciyata wata irin soyayyarsa mai zafi ce take sake ragargazar zuciyar. Kallona dai yake kafin na ji ya sake kiran sunana. Kiran da naji har tsakiyar raina. “AYSHA! D’ago ki kalleni ina son mu yi maganar gaskiya, bana son k’unbiya k’unbiya kuma….
Zan baki tarihin kai na da baki tab’a tambaya ba, zan sanar da ke waye ni da k’arfin soyayyarki a zuciyata, idan kin amince da aurena to, idan kuma kin ji ban kwanta miki ba bayan sanin wanene ni sai na k’yaleki na yi fatan Allah ya ha’da kowa da rabonsa….
Ahmad Sulaiman Saeed shine
Cikakken sunana, sunan da iyaye suka saka min, sunan da kowa ya san ni da shi. Sai dai a yanzu a makarantar ku da gidanmu na ji sun canja min suna zuwa Ustazun Aysha….”
Jin abinda ya fa’da ya saka ni saurin d’agowa ina kallonsa. D’aga min kai ya yi “Banda tambaya har sai na gama, abu guda da na sani ina jin da’din Sunan da aka canja min, ina kuma fata ya ‘dore har abada idan da alheri a cikin zama na da ke…
Mu uku kacal na gani a gidan mu, nima ban san dalilin da yasa suka zab’i su haifemu mu ukun ba kamar a k’asar turawa duk da dai d’abiun turawan suke amfani da su… na so a ce gidanmu muna da yawa kamar yarda nake sha’awar duk wani babban gida ya kasance, sai dai hakan bata samu ba. Amma na ce alwashin duk matar da na aura sai ta haifa min yara bila adadin ina son naga y’ay’ana sun kai hamsin…” waro idona na yi ina kallonsa ya ‘d’aga min kai “Don haka sai ki shirya dafatan Allah ya bamu masa albarka….” Runtse idona na yi saboda tsananin kunya a raina nake raya sai kace nace masa zan aureshi?
Ahmad Sulaiman Sa’eed shine Babba, sai Khadija Sulaiman Sa’eed wanda kafin a haifeta sai da na shekara goma cif. Itama tsakaninta da d’an autanmu shekaru goman ne, shi yasa na ce miki su iyayena rayuwar turawa suke ko don a can k’asar masu jajayen kunnuwan suka taso. Mahaifina ya da’de yana aiki a Canada kafin ya dawo Nigeria ya kafa kasuwanci.
Mahaifina su Talatin ne a gidansu ba zan iya jero miki su ba, sai dai na san mutanene masu zumunci masu son kuma auren zumunci, nima bijirewa na yi na musu tsallen baka’dai na gaya musu AYSHA kawai zuciyata take so. A d’akin su Abba na akwai Umma Amina itace Babba sai Umma Jamila, Daddynmu sai Abba Kabeer, Abba Ali, Abba Naseer da Umma Shatu.. autarsu kenan kuma mate d’ina ce mai sunan Ayshata…
A gidansu Umma na kuwa su Ashirin ba biyu ne, sai dai a d’akinsu su biyar ne kacal. Ramla Mahaifiyar Ahmad Sulaiman, sai Saudat Tasleem, Taiba da Nihad. Nan fa wai su mahaifiyarsu balarabiya shi yasa ta sakawa yaranta sunan larabawa don Kakata buzuwar Yamen ce.. sai kin hankali da su idan muka yi aure don mutane ne masu felek’e da iyayi na gaske.
Duka karatu na tun daga matakin yarinta har na girma, na yi su ne a lebanon school, sai da na gama secondary sannan na tuburewa Daddy na ce Jami’atul Madeena za’a kai ni. Ya so ya bujire don shi burinsa na zama iyalen Elizabeth ni kuma na ce nawa burin na zama dangin King Fahad ne, an kai ruwa rana kafin ya amincewa buk’atata na tattara na tafi Jami’atul Madeena ban kuma dawo ba sai a waccan shekarar… Ina isowa Nigeria na tsunduma aikin k’wadago ina ha’dawa da noma da kiwo da kuma safara daga can k’asashen waje zuwa tamu k’asar.
Ranar da na fara ganinki, rana ce mai matuk’ar girma a wajena, da ba zan manta da ita ba. Kamar ba zan fita daga gida ba saboda hadari da ya lullub’e sararin samaniya sai dai wayar da Kabeer yake min ta isheni na zuwa ganin wani gida da Zan gani a layinku. Na mik’e na shiga wanka kamar ba zan yi kwalliya ba sai dai na samu kaina da tsara kwalliya ashe zan ha’du da matata ne…
Ina tsaye da abokina na dinga jin zuciyata na wani irin harbawa. Mamaki ya isheni na juya don ganin dalili sai idona ya fa’da kan wata zuk’ek’iyar yarinya doguwa fara mai suffar larabawa. Numfashina ne ya kusa d’aukewa duk da na Yi matuk’ar daurewa wajen yi miki kallon da shari’a ta amince da shi kallo guda. Sai da kika wuce sannan na saki ajiyar zuciya ina kallon Kabeer na furta “Wacece wannan?” Kabeer dariya ya yi sosai yana cewa “Ai kuwa in dai sonta ka ke ka dace da macen k’warai, Saliha managarciya da kowa ke so.. duk layin nan ba nutsuwar yarinyar can wallahi…” na d’an yi dariya ina furta “Dalilinka na cewa haka Kabeer?” “Saboda kai daga gani shigarta ka san ta ha’da duk qualities d’in da ake son mace ta gari ta zama..” ya furta yana kallona cikin son tabbatarwa. Dariya na yi nace “Idan kuma Basaja take fa?” Kabeer ya ware ido ya ce wallahi ba wani Basaja idan baka amince ba kuma ka yi bincike..” “Bincike ya zama dole Kabeer, don aure nake son mu yi ta zame min Uwar yara na kaga kuwa dole na binciki sahihancin tarbiyyarta..” Kabeer ya jinjina min kai. “Ina tabbatar maka Ahmad duk binciken da zaka yi akan yarinyar nan magana guda zaka samu Mai tarbiyya ce…” Na saki ajiyar zuciya ina d’aga kai na windownku na hango kamar ana lek’e jikina kuma ya bani ke ce ko?” Waro ido na yi ina kallonsa. Ya saki murmushi yana d’aga min gira. “A jikina na san ke ce, na san kuma kema kin fa’da soyayyata daga yanayin yarda idanunmu suka sark’e da juna…”
Daga ranar na kafa d’anbar bincike ka’in da Na’in. Shine dalilin da yasa na je har makarantarku neman koyarwa. Kuma daga ranar kullum a kan idona kike tafiya makaranta duk da ba na bari ki ganni, na kuma lura duk sanda kika zo wucewa sai kin dinga d’an juyowa kina dubawa. Ina sane na dinga miki duk tambayoyin da nake miki a aji sai na samu kina da matsananciya kunya. Wannan ma ya sake k’ara miki k’ima a idona.
Hakan yasa kai tsaye naje gida da buk’atar azo min neman izinin fara zuwa zance wajenki. A take Abba ya ce wallahi in dai nine nake sonki ya ba ni ke, sai dai zai rok’i alfarmar a barki ki gama secondary saura shekara guda. Ba wanda ya ja da haka sai dai ni ba haka na so ba, na so a ce a yi bikin cikin wata biyu idan yaso ki k’arasa makarantar a gida na. Mommy ce ta dinga tausata. Abin kamar almara kullum Aysha k’ara min wutar sonki ake.. Yau da na ganki kina kuka a makaranta da k’yar na k’arasa musu karatun da nake musu. Allah ne ka’dai ya kai ni gida. Na dinga rok’on Daddy yazo a d’aura aure kawai amma ya k’i ya ce dole a bi maganar Abbanki ko shine ba zai aurar da y’arsa bata gama secondary ba. Still yanzu ma nazo naga kina kuka, AYSHA ki gaya min gaskiya ba kya son auren ne?”
Ajiyar zuciya na sauke a hankali na d’aga kai na. Waro ido ya yi har yana mik’ewa ya iso gaba na a tsayen da yake hannayensa a k’irji ya furta “Ki gaya min gaskiya, da gaske ba kya so na, idan Kika sake tabbatar min zan hak’ura…” Jikina ne yake rawa na sake d’aga kai na.. Zama ya yi yana rik’e kansa naga sai murza goshinsa yake. Sai kuma na ji cikin sark’akkiyar murya ya furta “Ki furta da bakin ki, cewa ba kya so na…” Na d’aga leb’ena a hankali ina kallon k’wayar idonsa muryata na rawa na furta “Na ba yanzu zan yi aure ba sai na yi ko degree ne, am too young to marry…..”
Ga mai son next page ya duba shafina na arewa zai samu page d’aya ko biyu bayan wannan.
Page 11 @ ArewaBooks Danna link d’in nan Zai kai ka har page 11.
https://arewabooks.com/chapter?id=669d122dc1b845b878dad215
Saboda yawan complain d’inku yasa na yi haka… dafatan za’a ni ha’din kai.
Group 1 and 2 ya cika ga group 3 nan wanda bai samu ba ya shiga.
𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️
[8/5, 1:21 PM] Nazeefah Nashe: https://chat.whatsapp.com/HfGu1Pozgx9IxjCYqW7ZCZ
NA GA RAYUWA♥︎♥︎♥︎
𝒩𝒶𝓏ℯℯ𝒻𝒶𝒽 𝒩𝒶𝓈𝒽ℯ★✍️
Free Book.. MIKIYA WRITERS ASSOCIATION
Arewabooks @nazeefah
https://chat.whatsapp.com/HfGu1Pozgx9IxjCYqW7ZCZ
Wattpad@Nazeefah381
08033748387.
★★★★★ 𝒫𝒶ℊℯ 12
Zan baki tarihin kai na da baki tab’a tambaya ba, zan sanar da ke waye ni da k’arfin soyayyarki a zuciyata, idan kin amince da aurena to, idan kuma kin ji ban kwanta miki ba bayan sanin wanene ni sai na k’yaleki na yi fatan Allah ya ha’da kowa da rabonsa….
Ahmad Sulaiman Saeed shine
Cikakken sunana, sunan da iyaye suka saka min, sunan da kowa ya san ni da shi. Sai dai a yanzu a makarantar ku da gidanmu na ji sun canja min suna zuwa Ustazun Aysha….”
Jin abinda ya fa’da ya saka ni saurin d’agowa ina kallonsa. D’aga min kai ya yi “Banda tambaya har sai na gama, abu guda da na sani ina jin da’din Sunan da aka canja min, ina kuma fata ya ‘dore har abada idan da alheri a cikin zama na da ke…
Mu uku kacal na gani a gidan mu, nima ban san dalilin da yasa suka zab’i su haifemu mu ukun ba kamar a k’asar turawa duk da dai d’abiun turawan suke amfani da su… na so a ce gidanmu muna da yawa kamar yarda nake sha’awar duk wani babban gida ya kasance, sai dai hakan bata samu ba. Amma na ce alwashin duk matar da na aura sai ta haifa min yara bila adadin ina son naga y’ay’ana sun kai hamsin…” waro idona na yi ina kallonsa ya ‘d’aga min kai “Don haka sai ki shirya dafatan Allah ya bamu masa albarka….” Runtse idona na yi saboda tsananin kunya a raina nake raya sai kace nace masa zan aureshi?
Ahmad Sulaiman Sa’eed shine Babba, sai Khadija Sulaiman Sa’eed wanda kafin a haifeta sai da na shekara goma cif. Itama tsakaninta da d’an autanmu shekaru goman ne, shi yasa na ce miki su iyayena rayuwar turawa suke ko don a can k’asar masu jajayen kunnuwan suka taso. Mahaifina ya da’de yana aiki a Canada kafin ya dawo Nigeria ya kafa kasuwanci.
Mahaifina su Talatin ne a gidansu ba zan iya jero miki su ba, sai dai na san mutanene masu zumunci masu son kuma auren zumunci, nima bijirewa na yi na musu tsallen baka’dai na gaya musu AYSHA kawai zuciyata take so. A d’akin su Abba na akwai Umma Amina itace Babba sai Umma Jamila, Daddynmu sai Abba Kabeer, Abba Ali, Abba Naseer da Umma Shatu.. autarsu kenan kuma mate d’ina ce mai sunan Ayshata…
A gidansu Umma na kuwa su Ashirin ba biyu ne, sai dai a d’akinsu su biyar ne kacal. Ramla Mahaifiyar Ahmad Sulaiman, sai Saudat Tasleem, Taiba da Nihad. Nan fa wai su mahaifiyarsu balarabiya shi yasa ta sakawa yaranta sunan larabawa don Kakata buzuwar Yamen ce.. sai kin hankali da su idan muka yi aure don mutane ne masu felek’e da iyayi na gaske.
Duka karatu na tun daga matakin yarinta har na girma, na yi su ne a lebanon school, sai da na gama secondary sannan na tuburewa Daddy na ce Jami’atul Madeena za’a kai ni. Ya so ya bujire don shi burinsa na zama iyalen Elizabeth ni kuma na ce nawa burin na zama dangin King Fahad ne, an kai ruwa rana kafin ya amincewa buk’atata na tattara na tafi Jami’atul Madeena ban kuma dawo ba sai a waccan shekarar… Ina isowa Nigeria na tsunduma aikin k’wadago ina ha’dawa da noma da kiwo da kuma safara daga can k’asashen waje zuwa tamu k’asar.
Ranar da na fara ganinki, rana ce mai matuk’ar girma a wajena, da ba zan manta da ita ba. Kamar ba zan fita daga gida ba saboda hadari da ya lullub’e sararin samaniya sai dai wayar da Kabeer yake min ta isheni na zuwa ganin wani gida da Zan gani a layinku. Na mik’e na shiga wanka kamar ba zan yi kwalliya ba sai dai na samu kaina da tsara kwalliya ashe zan ha’du da matata ne…
Ina tsaye da abokina na dinga jin zuciyata na wani irin harbawa. Mamaki ya isheni na juya don ganin dalili sai idona ya fa’da kan wata zuk’ek’iyar yarinya doguwa fara mai suffar larabawa. Numfashina ne ya kusa d’aukewa duk da na Yi matuk’ar daurewa wajen yi miki kallon da shari’a ta amince da shi kallo guda. Sai da kika wuce sannan na saki ajiyar zuciya ina kallon Kabeer na furta “Wacece wannan?” Kabeer dariya ya yi sosai yana cewa “Ai kuwa in dai sonta ka ke ka dace da macen k’warai, Saliha managarciya da kowa ke so.. duk layin nan ba nutsuwar yarinyar can wallahi…” na d’an yi dariya ina furta “Dalilinka na cewa haka Kabeer?” “Saboda kai daga gani shigarta ka san ta ha’da duk qualities d’in da ake son mace ta gari ta zama..” ya furta yana kallona cikin son tabbatarwa. Dariya na yi nace “Idan kuma Basaja take fa?” Kabeer ya ware ido ya ce wallahi ba wani Basaja idan baka amince ba kuma ka yi bincike..” “Bincike ya zama dole Kabeer, don aure nake son mu yi ta zame min Uwar yara na kaga kuwa dole na binciki sahihancin tarbiyyarta..” Kabeer ya jinjina min kai. “Ina tabbatar maka Ahmad duk binciken da zaka yi akan yarinyar nan magana guda zaka samu Mai tarbiyya ce…” Na saki ajiyar zuciya ina d’aga kai na windownku na hango kamar ana lek’e jikina kuma ya bani ke ce ko?” Waro ido na yi ina kallonsa. Ya saki murmushi yana d’aga min gira. “A jikina na san ke ce, na san kuma kema kin fa’da soyayyata daga yanayin yarda idanunmu suka sark’e da juna…”
Daga ranar na kafa d’anbar bincike ka’in da Na’in. Shine dalilin da yasa na je har makarantarku neman koyarwa. Kuma daga ranar kullum a kan idona kike tafiya makaranta duk da ba na bari ki ganni, na kuma lura duk sanda kika zo wucewa sai kin dinga d’an juyowa kina dubawa. Ina sane na dinga miki duk tambayoyin da nake miki a aji sai na samu kina da matsananciya kunya. Wannan ma ya sake k’ara miki k’ima a idona.
Hakan yasa kai tsaye naje gida da buk’atar azo min neman izinin fara zuwa zance wajenki. A take Abba ya ce wallahi in dai nine nake sonki ya ba ni ke, sai dai zai rok’i alfarmar a barki ki gama secondary saura shekara guda. Ba wanda ya ja da haka sai dai ni ba haka na so ba, na so a ce a yi bikin cikin wata biyu idan yaso ki k’arasa makarantar a gida na. Mommy ce ta dinga tausata. Abin kamar almara kullum Aysha k’ara min wutar sonki ake.. Yau da na ganki kina kuka a makaranta da k’yar na k’arasa musu karatun da nake musu. Allah ne ka’dai ya kai ni gida. Na dinga rok’on Daddy yazo a d’aura aure kawai amma ya k’i ya ce dole a bi maganar Abbanki ko shine ba zai aurar da y’arsa bata gama secondary ba. Still yanzu ma nazo naga kina kuka, AYSHA ki gaya min gaskiya ba kya son auren ne?”
Ajiyar zuciya na sauke a hankali na d’aga kai na. Waro ido ya yi har yana mik’ewa ya iso gaba na a tsayen da yake hannayensa a k’irji ya furta “Ki gaya min gaskiya, da gaske ba kya so na, idan Kika sake tabbatar min zan hak’ura…” Jikina ne yake rawa na sake d’aga kai na.. Zama ya yi yana rik’e kansa naga sai murza goshinsa yake. Sai kuma na ji cikin sark’akkiyar murya ya furta “Ki furta da bakin ki, cewa ba kya so na…” Na d’aga leb’ena a hankali ina kallon k’wayar idonsa muryata na rawa na furta “Na ba yanzu zan yi aure ba sai na yi ko degree ne, am too young to marry…..”
Ga mai son next page ya duba shafina na arewa zai samu page d’aya ko biyu bayan wannan.
Page 11 @ ArewaBooks Danna link d’in nan Zai kai ka har page 11.
https://arewabooks.com/chapter?id=669d122dc1b845b878dad215
Saboda yawan complain d’inku yasa na yi haka… dafatan za’a ni ha’din kai.
Group 1 and 2 ya cika ga group 3 nan wanda bai samu ba ya shiga.
𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️
[8/5, 1:21 PM] Nazeefah Nashe: https://chat.whatsapp.com/HfGu1Pozgx9IxjCYqW7ZCZ
NA GA RAYUWA♥︎♥︎♥︎
𝒩𝒶𝓏ℯℯ𝒻𝒶𝒽 𝒩𝒶𝓈𝒽ℯ★✍️
Free Book.. MIKIYA WRITERS ASSOCIATION
Arewabooks @nazeefah
https://chat.whatsapp.com/HfGu1Pozgx9IxjCYqW7ZCZ
Wattpad@Nazeefah381
08033748387.
★★★★★ 𝒫𝒶ℊℯ 12