← Book details Matar Gwamna Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 48

Sashe 21

Matar Gwamna Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A cikin mota suna hanyar su ta dawowa Madam Bintu ta fara rarrashin aminiyarta tareda yi mata alƙawarin za su keta chan kudancin ƙasar domin su samu wani bokan daban.
Tunda suka baro wajen boka Bilkisu ta kasa magana. Na farko saboda ta san abinda Bokan ya faɗa gaskiya ne dan an mata kashedi akan cewa baƙin aljani da ke yiwa macijinta hidima baya son kishiya. Na biyu kuma haka kawai bayan sun fito daga jejin ta ji ƙirjinta na mata wani irin nauyi kamar wanda aka ɗauki ƙaton dutsi aka ɗaura a kai.

A wannan yanayi suka ƙarisa cikin gari, sai dai tun a hanya suka lura cewa akwai wani abu da ke faruwa a garin musamman da suka isa dai dai anguwar Gwamna.

Motocin da suka yi tozali da shi a gidan shi ya tabbatar wa Bilkisu cewa akwai matsala...

Suman zaune Bilkisu ta yi lokacin da mahaifiyarta da Hajiya Umma suka sanar da ita rasuwan da aka yi. Ƙauyen da suka je babu network shiyasa duk kiran da ake mata tun faruwan abin baya shiga.

"Wasa kuke min right?" Bilkisu ta faÉ—a bayan ta iya buÉ—e bakinta.

Jagora suka mata har inda aka shimfiɗa gawar mamacin wanda kallo ɗaya zaka yi kasan cewa gawar yaro ce. Addu'a aka ce ta yi masa amma sai ta kama ƙoƙarin buɗe likkafanin tana faɗin ba abinda ya samu babyn ta, wai bacci yake yi, nan da nan aka fara ƙoƙarin riƙeta, Hajiya Umma kuwa abin ya zo mata har wuya ta kama Bilkisu ta tsinke ta da mari tana faɗin
"Ki nitsu ki masa addu'a dan Allah, wannan abinda kike ba dawo da shi zai yi ba"

Jikin Bilkisu ya shiga ɓari saboda ta gani, tabbas ta ga tabon saran da ke goshin gawar ɗanta Sa'ad Junior.

17

Tunda aka fita da gawar Junior Bilkisu ta rufe kanta a ɗakin yaron ta ƙi fitowa, anyi bugun duniyar nan, an mata magana amma ta ƙi buɗe ɗakin. Ƙarshe sai barinta aka yi kamar yadda Hajiya Umma ta faɗa. Har ga Allah mutuwa da ciwo amma kuma sanin cewa macijin Bilkisu ne ya kashe mata ɗa yasa ko kaɗan Hajiya Umma bata tausaya mata ba, idan da hali ma titsiyeta zata yi da duka har sai ta huce baƙin cikin dake ranta, sai dai kuma Junior ya tafi kenan babu abinda za ayi ya dawo duniyar, sai dai haƙuri kawai.

Asiya ce ke karɓan gaisuwa a madadin Bilkisu. Itama ɗin da ka kalleta kasan tana cikin tashin hankali saboda ita ce ta fara ganin gawar Junior.
Ta tsorata matuƙa lokacin da ta shiga ɗakin yaron dan ta masa wanka ta same shi ƙwance a ƙasa baya motsi. Kumburin goshinsa da tabon cizo guda biyu a goshin ya sa Asiya tayi zargin saran maciji ne, koda aka kai shi asibiti report ɗin da suka bayar ya nuna cewa gubar maciji ce ta kashe shi. Babu wanda ya san lokacin da abin ya faru kuma tunda abin ya faru Gwamna yasa a dubo masa macijin Bilkisu ya kashe amma babu ita babu dalilinta. Abin haushin ma kuma ita kanta Bilkisun anyi ta kiranta amma duka nambobinta basa shiga, ba a san inda taje ba balle yaushe za ta dawo. Anyi jinkirin jana'izar saboda ita ne, wanda Asiya da mahaifiyar Bilkisun ne suka nemi hakan a wajen Gwamna, awa biyu daya bayar akan idan Bilkisu bata zo ba za a kai yaron sai gata nan a sama.

Bilkisu ta rungume hoton Junior tana sheshsheƙar kuka haɗe da sunbatu. Rabon da ta yi wani magana mai tsayi da yaron ta manta, tun kafin dawowar Gwamna. Shine magajin Saifuddeen shine magajinta abinda ta sakawa ranta kenan tun ranan data haife shi, kai tunma da aka yi scanning aka ce mata namiji zata haifa. Yanzu gashi nan ya tafi ya barta, bata da magaji...

*

Mutuwar Junior ya kawo wani sauyi a tattare da Gwamna dama iyalinsa gaba ɗaya. A ɓangaren Bilkisu tunda aka yi rasuwan ta tare a ɗaki, har aka gama gaisuwan uku bata fita daga ɗakin ta ba, a daren ranan rasuwan ne ta fito daga ɗakin Junior idanunta a kumbure ta wuce nata ɗakin ba tareda ta amsa gaisuwar kowa ba. Hatta manyan mata ire-iren matan Gwamnoni dana senatoci da suka zo yi mata gaisuwa babu wanda ta sakewa fiska wannan yasa mutane ke tunanin mutuwar yaron ya taɓa mata ƙwaƙwalwa.
Shi kan shi Gwamna dauriya yake amma zuciyarsa tana cikin ƙuna. Maganar sanadin mutuwar yaron ya tsaya ne iya cikin gida, duk dama akwai wata ƙaramar gidan jarida da suka wallafa cewa Sa'ad Junior ya rasu ne sakamakon harbin maciji. Hakan yasa Mai magana da yawun Gwamna ya fito ya ƙaryata jaridar wannan yasa maganar bata yi tsayi ba aka tsaida tasirinta a cikin mutane...

Yanzu hankalin kowa ya karkata ne kan naɗin sabon sarki. Kowa ya baza ido yaga wa za a naɗa. Wasu ɓangare na matasa har sun shirya zanga-zanga da tarzoma da za su yi idan har aka naɗa Alhaji Sani Kachallah a matsayin sarki.

Alhaji Sani Kachallah bai da sha'awar neman takarar sarautar gidansu. Amma kuma a ɗan tsurkukin kwanakin rasuwan sarki munafukan mutane suka cusa masa wannan ra'ayi, tun yana kauda kai har ta kai shaiɗan ya samu galaba a kansa. Chan cikin zuciyarsa ya sani cewa Saifuddeen ba zai taɓa naɗa shi sarki ba, amma wannan sabon buri dake cinsa ya raya masa cewa babu wanda ya kamata Saifuddeen ya naɗa sarki sai shi!.

*

Kwanaki shauku da rasuwan Junior aka naɗa sabon sarkin garin Congo. Sarki Ya'aqub shine zaɓin gama-garin talakawa dama mutanen da su ke son zaman lafiya da cigaban gari. Duk da cewa shi ɗin ɗa ne ga ƙanin Sarki mai rasuwa amma hakan bai hana shi samun sarautan gidan su ba, abu uku su suka saka mutane suka yi ra'ayinsa sama da asalin ɗan sarki mai rasuwa wato Yarima Isma'il. Na farko an masa shaidar baya shan giya tun daga samartakarsa har zuwa yanzu da yake shekaru arba'in da bakwai a duniya. Babu wani daya taɓa yi masa shaidar shan giya a bayyane ko a ɓoye cikin abinda ya bayyana wa makusantansa, sai dai Allah ne kaɗai masanin gaibu.
Na biyu ya kasance masanin addini kuma kyawawan halayensa su suka fi bayyana wa mutane. Na uku shine yana da yawan kyauta, tun yana saurayi wannan shaida ya ke binsa. Ba kamar Yarima Isma'il ba wanda a ɗan shekaru biyun ƙarshe na mahaifinsa ya fara ƙoƙarin jawo mutane jikinsa tareda ƙoƙarin sake aljihunsa wa talakawa...

Tun da aka bada sanarwar naɗin sabon sarki gari ya kaure da murna da farin cikin matasa, ta ko'ina sai shagulgula ake domin bayyana farin cikin da ake ciki. A yayin da wasu magoya bayan Yarima Isma'il suka yi yunƙurin tada husuma, sai dai abin bai kai ko'ina ba jami'an tsaro suka tare abin.

Yayinda wannan naɗi ya kawo farin ciki a zukatan mutane shi Gwamna Saifuddeen Kachallah ya wuni ne cikin ƙunci da kuma tsoron abinda zai biyo bayan abinda ya aikata. Kafin wannan rana sun yi magana mai tsayi tareda Alhaji Sani wanda ta kowanni fiska uba yake a gareshi. Cikin maganganunsa ya karkatar da hirar ne zuwa shekaru da dama da suka shige irin yadda shi Alhaji Sani ya nunawa Saifuddeen so da ƙauna sama da 'ya'yansa na cikinsa daga ƙarshe ya sake tunasar da shi cewa wannan kujera da yake kai ta zo gareshi ne bisa shiri da kuma taimako da yai masa.
"Ina fata bazaka watsa min ƙasa a ido ba" maganar ƙarshe da Alhaji Sani yai kenan kafin rabuwar su.
Ashe kwaÉ—ayi da ya gani muraratan a idon matarsa Bilkisu wasu daga cikin makusantansa suma sun fara irin wannan kwaÉ—ayi.
Kwana ɗaya bayan maganarsa da Alhaji Sani sai mahaifiyar Bilkisu ta nemi ganawa da shi kuma bil-haƙƙi ta fito fili ta bayyana manufarta wato idan har ya cika ɗan halak to kujerar sarki ta mijinta ne. Bayan nan ya samu 'yanuwa na kusa da na nesa da suka dinga zuwa suna bashi shawaran naɗa mahaifinsa a matsayin sarki, wasu na ganin wannan zai kawo masa kwarjini da cigaba a harkar siyasar jihar. Sai dai kuma duk ta inda ya duba duk addu'a da istikhara da yai tun kafin rasuwan ɗansa dama bayan nan zuciyarsa bai amince da naɗa Alhaji Sani sarki ba.

A cikin kwanakin da aka ɗauka kafin a bayyana sunan wanda Gwamna ya zaɓa ko sau ɗaya Bilkisu ba ta yi magana da Gwamna ba. Tana nan tana fama da raɗaɗin rashin ƙaramin ɗanta kuma ɗa namiji ɗaya tal data haifa. Sai dai tun kafin a fitar da sanarwar wanda aka naɗa ta riga ta samu labari, sai dai babu wani abu da zata iya yi akai illa ta bi shawaran da wani ɓangare na zuciyarta yake bata.

Cikin dare da Gwamna ya dawo gida a karo na farko cikin sati biyu Bilkisu ta shirya tsaf ta wuce É—akin mijinta. Sai dai ba wai ta je ne domin ta amsa sunan matarsa ba, taje ne domin ta bayyana masa abinda ke ranta.

Gwamna sai daya tsorata da ganinta kwatsam a ɗakinsa, ta sameshi yana ƙoƙarin cire kayan jikinsa domin yai wanka ko zai rage jin nauyi da ciwo da ilahirin jikinsa ke yi. Yadda ya ganta fiska ɗauke da kwalliya da kuma shiga ta alfarma kamar mai shirin zuwa bikin 'yar shugaban ƙasa yasa shi tunanin lallai ba lafiya ba. Yaushe rabon ya ganta da kwalliya?.

"Kayi mamakin ganina ko?"

"Bilkisu it's 1:00 am, a gajiye nake please, koma minene ki bari gobe zamu yi magana"
Chapter 21 · 0% Book details