Sashe 15
Matar Gwamna Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ta ya zan ɗauke ka mijina bayan ba ka taɓa kwatanta adalci a kaina ba. Ta ya zan ba ka matsayin miji bayan kana take hakkin talakawan da ke ƙasan ka. Kana so in zauna da kai fushi da tsinuwar talakawa yana bin ka duk inda ka shiga? Kana tunanin kai kaɗai tsinuwarsu zai shafa? Zai shafeni, zai shafi 'ya'yan ka da duk wani na kusa da kai. Ba zan iya zama da miji kamar ka ba"
Gwamna yai murmushi ganin kyakykyawar fiskarta ya bayyana a idonsa.
"Gara da ki ka tafi Asya, gara da kika rabu da ni. I hope idan bana nan tsinuwar zai tsaya a kaina ni kaÉ—ai"
Hannunsa na rawa ya sake harsashin bindigar...
12
"Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'oun. Dan Allah kar ka harba, Dan Allah miji na kar ka harba"
Asiya tana maganar tana takowa a hankali idanunta na zubda hawaye.
"Kar ki matso inda na ke"
Ta tsaya chak da tafiyar cikin kuka ta ce " idan ka harba ka san mi zai faru?. Nima bindigar zan É—auka na harbe kaina sai kawai akai mu wutan tare.
"Mijina Idan kana ganin ka ci amanar mutane nima na ci amanar aurena. Idan ka kashe kan ka saboda kana ganin shine mafita to nima zan kashe kaina saboda ba zan iya rayuwa ba tare da kai ba "
"Asya" ya kira sunanta da muryar shi mai rauni. Sai kuma ya ajiye bindigar a ƙasa ya fashe da kuka. Da sauri Asiya ta ƙarisa wajensa ta rungume shi itama ta saka kukan mai tsuma zuciya.
Allah ne ya kawota a dai-dai wannan lokaci, domin ɗazu da Gwamna ya harbi kansa harsashi ne babu a cikin bindigar, lokaci guda ya ji gwiwarsa ta yi sanyi amma shaiɗan ya cigaba da tunzura shi sai ya ji wani ƙarfin gwiwa ya dawo masa nan da nan ya jawo akwatin bindigar ya ciro harsashi guda ya saka cikin bindigar.
"I love you Saifuddeen Sa'ad Kachallah" Asiya ta faÉ—a dai-dai kunnensa.
"Ni Azzalumi ne Asya"
" shhhhh. Kai mutumin kirki ne, kanada niyya mai kyau a jihar nan. Allah yana tare da kai idan ka nemi taimakonsa, ka yi nisa da shi My love, ka yi nisa da mahaliccinka shiya sa komai ya lalace a ƙarƙashinka.
"Kin guje ni Asya, kin ce ba za ki zauna da ni ki raɓi tsinuwar talakawa ba. Ki bar ni kawai na je na amshi laifina a wajen Allah"
"No my love, ba zan taɓa gudun ka ba, duk abinda na ke ina yi ne dan na taimakeka. I love you Excellency, ba zan taɓa rabuwa da kai ba. Daga yanzu i promised to be honest with you, respect you and always support you. Ba za ka je gaban Allah kana Azzalumi ba ka ji. We can fix this ka ji, akwai sauran shekara uku a gaban ka"
"Shekara biyu da wata tara Asya"
Asiya ta saka dariya tana bubbuga bayansa ta ce " yes Excellency, cikin shekara biyu da wata tara da suka rage zamu gyara komai. Da taimakon Allah za mu yi iya ƙoƙarinmu wajen ganin mun tafiyar da jihar nan bisa gaskiya da adalci"
Gwamna ya ɗago kanshi ya ƙurawa Asiya ido kaman a ranan ya fara kallonta.
"Asya kina nufin..."
"Yes Excellency, ni da kai za mu gyara jihar nan Insha Allah"
Gwamna ya sake jawota jikinsa yana jin wani sabon son ta na shiga jikinsa.
"Hasbiyallaahu Laa'ilaaha Illa Huwa Alaihi Tawakkaltu wa Huwa Rabbul Arshil Azim"
Asiya ta fara maimaitawa da ƙarfi a kunnensa.
Gwamna ya buÉ—e baki zai maimaita abinda ta ce amma bakinsa yai nauyi.
Asiya ta cigaba da maimaita addu'ar tana yi tana shafa kansa. Ganin ya kasa maimaita addu'ar sai yai shiru yana sauraronta chan kuma sai barci ya É—auke shi.
Duk da yayi barci Asiya bata dena karanto addu'ar ba.
Banko ƙofar aka yi da ƙarfi wannan yasa hankalin Asiya ya koma kan ƙofar. Ba ta yi mamakin ganin matar da ke tsaye bakin ƙofar ba.
Idanunsu na haɗuwa Bilkisu Kachallah ta ji tsikar jikinta ya tashi. Ta yi saurin janye idonta ta maida shi kan bindigar da ke gefen ƙafar Asiya.
"Mi ya same shi?. Mi kika masa?" Bilkisu ta faɗa a kiɗime tana ƙarasowa wajensu da sauri.
Ta janye Gwamna daga jikin Asiya da ƙarfi sai ta ga ya faɗi yijif.
"What did you do to him?"
"Bacci ya ke"
Asiya ta bata amsa a taƙaice.
"Ki fita ki bamu waje" Bilkisu ta faÉ—a da muryar umurni.
"Ina ganin ke ce ya dace ki yi hakan"
"What!"
"Yes Bilkisu, ki bamu waje"
Mamakin ƙarfin gwiwar Asiya ta yi a wani ɓangare kuma tunanin yaushe zuwanta gari?, mi ta zo yi? da ma wasu tambayoyin su suka hanata magana.
Bayan fitan Bilkisu daga É—akin kiran COS ta yi ta ce su haÉ—u a chan gidan gwamnati.
A falonta ya sameta ta ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya tana karkaɗa shi cike da bala'i.
"Boss"
"You are very stupid Lamara. Ni zaka raina wa hankali, dama Asiya tana Nigeria ka ce min ta fita ƙasar waje"
"Boss ban san ya aka yi..."
Bilkisu ta wurgeshi da kofin glass da ke kan centre table, kofin ya samu kafaɗarsa ya faɗi ƙasa ya tarwatse.
"When i give you assignment you execute it perfectly. Taya za ka bani report cewa Asiya ta tafi Stanford yin masters ɗinta bayan tana ƙasar nan. How dare you lie to me"
Idanunta suka kaÉ—a su ka juya zuwa idon maciji ta fara huci.
Nan da nan Lamara yai ƙasa da gwiwowinsa ya shiga bada haƙuri.
Bayan ta dawo hayyacinta sannan ta umurce shi daya zauna ya gaya mata gaskiyar inda Asiya ta je.
Tana jin sunan makarantar jikinta ya bata akwai abinda Asiya ke shirya mata amma koma minene tana dai-dai da ita.
Abu na farko da za ta yi shine ta sa a revoking sponsorship ɗinta sai ta ji da uban me za ta yi taƙama idan aka koreta.
Waya ta ɗauka ta kira M Sani dan yanzu ta ƙara jin a ranta cewa dole ta jawo shi jikinta fiye da da, idan har Lamara Damana zai ci amanarta to ɗan Rufaidah Kachallah ba zai ci amanarta ba domin abinda yai Rufaidah shi ya yita, shekara biyu da wata biyar ne tsakaninta da yayartata.
Bayan ta tabbatar da cewa M Sani zai tura saƙonta makarantar sannan ta samu nitsuwar shiga ɗaki dan ta kwanta gobe za ta je ta dawo da Gwamna wannan gida. Idan har saboda jifar sa da aka yi ya ke son kashe kan sa to ya sani ita Bilkisu Kachallah bata shirya zama bazawara ba sannan uwa uba bata shirya sauka daga matsayinta na MATAR GWAMNA ba.
***
Da dare zazzaɓi mai ƙarfi ya rufe Gwamna. Yadda jikinsa yai zafi ka ce idan ka fasa ƙwai ka zuba a ƙirjinsa zai soyu tas har ma ya ƙone. Asiya ta shiga banɗaki ta ɗauko bokiti ta saka ruwa sannan ta ɗauko ƙanƙara a chan falonsa ta zo ta jefa a ciki ta dinga tsoma towel a ciki tana matsewa tana shafe ilahirin jikinsa da shi. Lokacin da ta taɓa ƙafarsa saurin ɗauke hannunta ta yi dan tsananin zafi. Tana cikin shafa masa towel ta ji ya fara sunbatu cikin baccinsa.
"Ku yi haƙuri, ni ba Azzalumi bane. Ku yi haƙuri kada ku tsine min, ku yi haƙuri"
Hawaye ya sakko mata dai dai lokacin da ta dafe goshinsa tana karanto masa Ayatul Kursiyyu.
Gaskiya ta so kanta dayawa, tana sane da cewa akwai sihiri a jikinsa amma ta shure ƙafa ta wuce makaranta, ɗaukan fansa kawai ta saka a gaba ta manta cewa yana buƙatar taimakonta. Idan da ace duk watannin da ta ɗauka ta yi su ne cikin nema masa magani ƙila da ya samu waraka tuntuni, ƙila ma ba za a kai matsayin da su ke yanzu ba.
Ba abinda za ta ce sai dai Alhamdulillah kawai tunda Allah bai ba shi damar idda nufinsa na yin kisan kai ba.
Wani abu daya ƙara saka mata zubar hawaye shine tunanin bayan sihiri Gwamna yana fama da ciwon damuwa. He is depressed, akwai yiwuwar zai iya samun matsalar ƙwaƙwalwa duba da irin maganganun da yai ɗazu da kuma magagin bacci da ya ke yi.
Ta cigaba da shafe masa jiki da ruwan sanyi har zuwa Asuba lokacin da zazzaɓin ya sauka.
Da safe Gwamna ya buɗe ido ya kalleshi kwance kan gado gefensa Asiya da kuma likitan da ya ke ƙoƙarin ɗaura masa ruwa.
"Asya" ya kira da dasashshiyar murya.
"Excellency ya jiki?"
Shima Likitan na shi Dr Haruna ya tambayi lafiyarsa.
"Kai na ciwo Asya" ya faÉ—a yana binta da ido.
Hannunsa ta kamo ta kissing har sau biyu sannan ta ce " Insha Allah zai dena"
Bayan Likita ya gama saka ruwan Asiya ta biyo bayansa dan ta ji ƙarin bayani daga gare shi. Da Asuba Gwamna ya farka ta taimaka masa ya miƙe zai je banɗaki sai kawai ya riƙe kan sa ya yanki jiki ya faɗi ya suma wannan yasa hankalin Asiya ya tashi har ta kira likitan sa.
"Hajiya Asiya gaskiya Gwamna yana buƙatar hutu sosai, sannan ya kamata ya rage tunani, jininsa ya hau sosai kuma gaskiya hakan na barazana ga lafiyar sa. Idan ya cigaba da tafiya a haka zai iya faɗuwa ya shiga coma koma ya faɗi ya..."
"On whose authority kika kira Likita gidan nan?"
Muryan Bilkisu ya katse Dr Haruna
"Good Morning Mrs Kachallah"
"Dr Haruna bana tunanin yau ranan check up na Gwamna ne"
"Gwamna patient ɗina ne, inada damar zuwa duba shi idan ya buƙaci hakan"
Bilkisu ta kalli Asiya ta ce "Leave us"
Asiya ta yi murmushin yaƙe sannan ta koma ɗakin Gwamna, ba wai ta bi umurninta bane dama dai tana son komawa ɗaki dan ta ga Gwamna.
Lokacin da ta shiga ɗakin yana rigingine da filo ya ƙurawa bangon ɗakin ido kaman mai kallon TV.
"My love za ka iya yin sallar Asuba yanzu ko kuwa sai ruwan ya ƙare za ka yi"
"Zan yi yanzu, ban yi sallar Magariba da Isha ba jiya"
Gwamna yai murmushi ganin kyakykyawar fiskarta ya bayyana a idonsa.
"Gara da ki ka tafi Asya, gara da kika rabu da ni. I hope idan bana nan tsinuwar zai tsaya a kaina ni kaÉ—ai"
Hannunsa na rawa ya sake harsashin bindigar...
12
"Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'oun. Dan Allah kar ka harba, Dan Allah miji na kar ka harba"
Asiya tana maganar tana takowa a hankali idanunta na zubda hawaye.
"Kar ki matso inda na ke"
Ta tsaya chak da tafiyar cikin kuka ta ce " idan ka harba ka san mi zai faru?. Nima bindigar zan É—auka na harbe kaina sai kawai akai mu wutan tare.
"Mijina Idan kana ganin ka ci amanar mutane nima na ci amanar aurena. Idan ka kashe kan ka saboda kana ganin shine mafita to nima zan kashe kaina saboda ba zan iya rayuwa ba tare da kai ba "
"Asya" ya kira sunanta da muryar shi mai rauni. Sai kuma ya ajiye bindigar a ƙasa ya fashe da kuka. Da sauri Asiya ta ƙarisa wajensa ta rungume shi itama ta saka kukan mai tsuma zuciya.
Allah ne ya kawota a dai-dai wannan lokaci, domin ɗazu da Gwamna ya harbi kansa harsashi ne babu a cikin bindigar, lokaci guda ya ji gwiwarsa ta yi sanyi amma shaiɗan ya cigaba da tunzura shi sai ya ji wani ƙarfin gwiwa ya dawo masa nan da nan ya jawo akwatin bindigar ya ciro harsashi guda ya saka cikin bindigar.
"I love you Saifuddeen Sa'ad Kachallah" Asiya ta faÉ—a dai-dai kunnensa.
"Ni Azzalumi ne Asya"
" shhhhh. Kai mutumin kirki ne, kanada niyya mai kyau a jihar nan. Allah yana tare da kai idan ka nemi taimakonsa, ka yi nisa da shi My love, ka yi nisa da mahaliccinka shiya sa komai ya lalace a ƙarƙashinka.
"Kin guje ni Asya, kin ce ba za ki zauna da ni ki raɓi tsinuwar talakawa ba. Ki bar ni kawai na je na amshi laifina a wajen Allah"
"No my love, ba zan taɓa gudun ka ba, duk abinda na ke ina yi ne dan na taimakeka. I love you Excellency, ba zan taɓa rabuwa da kai ba. Daga yanzu i promised to be honest with you, respect you and always support you. Ba za ka je gaban Allah kana Azzalumi ba ka ji. We can fix this ka ji, akwai sauran shekara uku a gaban ka"
"Shekara biyu da wata tara Asya"
Asiya ta saka dariya tana bubbuga bayansa ta ce " yes Excellency, cikin shekara biyu da wata tara da suka rage zamu gyara komai. Da taimakon Allah za mu yi iya ƙoƙarinmu wajen ganin mun tafiyar da jihar nan bisa gaskiya da adalci"
Gwamna ya ɗago kanshi ya ƙurawa Asiya ido kaman a ranan ya fara kallonta.
"Asya kina nufin..."
"Yes Excellency, ni da kai za mu gyara jihar nan Insha Allah"
Gwamna ya sake jawota jikinsa yana jin wani sabon son ta na shiga jikinsa.
"Hasbiyallaahu Laa'ilaaha Illa Huwa Alaihi Tawakkaltu wa Huwa Rabbul Arshil Azim"
Asiya ta fara maimaitawa da ƙarfi a kunnensa.
Gwamna ya buÉ—e baki zai maimaita abinda ta ce amma bakinsa yai nauyi.
Asiya ta cigaba da maimaita addu'ar tana yi tana shafa kansa. Ganin ya kasa maimaita addu'ar sai yai shiru yana sauraronta chan kuma sai barci ya É—auke shi.
Duk da yayi barci Asiya bata dena karanto addu'ar ba.
Banko ƙofar aka yi da ƙarfi wannan yasa hankalin Asiya ya koma kan ƙofar. Ba ta yi mamakin ganin matar da ke tsaye bakin ƙofar ba.
Idanunsu na haɗuwa Bilkisu Kachallah ta ji tsikar jikinta ya tashi. Ta yi saurin janye idonta ta maida shi kan bindigar da ke gefen ƙafar Asiya.
"Mi ya same shi?. Mi kika masa?" Bilkisu ta faɗa a kiɗime tana ƙarasowa wajensu da sauri.
Ta janye Gwamna daga jikin Asiya da ƙarfi sai ta ga ya faɗi yijif.
"What did you do to him?"
"Bacci ya ke"
Asiya ta bata amsa a taƙaice.
"Ki fita ki bamu waje" Bilkisu ta faÉ—a da muryar umurni.
"Ina ganin ke ce ya dace ki yi hakan"
"What!"
"Yes Bilkisu, ki bamu waje"
Mamakin ƙarfin gwiwar Asiya ta yi a wani ɓangare kuma tunanin yaushe zuwanta gari?, mi ta zo yi? da ma wasu tambayoyin su suka hanata magana.
Bayan fitan Bilkisu daga É—akin kiran COS ta yi ta ce su haÉ—u a chan gidan gwamnati.
A falonta ya sameta ta ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya tana karkaɗa shi cike da bala'i.
"Boss"
"You are very stupid Lamara. Ni zaka raina wa hankali, dama Asiya tana Nigeria ka ce min ta fita ƙasar waje"
"Boss ban san ya aka yi..."
Bilkisu ta wurgeshi da kofin glass da ke kan centre table, kofin ya samu kafaɗarsa ya faɗi ƙasa ya tarwatse.
"When i give you assignment you execute it perfectly. Taya za ka bani report cewa Asiya ta tafi Stanford yin masters ɗinta bayan tana ƙasar nan. How dare you lie to me"
Idanunta suka kaÉ—a su ka juya zuwa idon maciji ta fara huci.
Nan da nan Lamara yai ƙasa da gwiwowinsa ya shiga bada haƙuri.
Bayan ta dawo hayyacinta sannan ta umurce shi daya zauna ya gaya mata gaskiyar inda Asiya ta je.
Tana jin sunan makarantar jikinta ya bata akwai abinda Asiya ke shirya mata amma koma minene tana dai-dai da ita.
Abu na farko da za ta yi shine ta sa a revoking sponsorship ɗinta sai ta ji da uban me za ta yi taƙama idan aka koreta.
Waya ta ɗauka ta kira M Sani dan yanzu ta ƙara jin a ranta cewa dole ta jawo shi jikinta fiye da da, idan har Lamara Damana zai ci amanarta to ɗan Rufaidah Kachallah ba zai ci amanarta ba domin abinda yai Rufaidah shi ya yita, shekara biyu da wata biyar ne tsakaninta da yayartata.
Bayan ta tabbatar da cewa M Sani zai tura saƙonta makarantar sannan ta samu nitsuwar shiga ɗaki dan ta kwanta gobe za ta je ta dawo da Gwamna wannan gida. Idan har saboda jifar sa da aka yi ya ke son kashe kan sa to ya sani ita Bilkisu Kachallah bata shirya zama bazawara ba sannan uwa uba bata shirya sauka daga matsayinta na MATAR GWAMNA ba.
***
Da dare zazzaɓi mai ƙarfi ya rufe Gwamna. Yadda jikinsa yai zafi ka ce idan ka fasa ƙwai ka zuba a ƙirjinsa zai soyu tas har ma ya ƙone. Asiya ta shiga banɗaki ta ɗauko bokiti ta saka ruwa sannan ta ɗauko ƙanƙara a chan falonsa ta zo ta jefa a ciki ta dinga tsoma towel a ciki tana matsewa tana shafe ilahirin jikinsa da shi. Lokacin da ta taɓa ƙafarsa saurin ɗauke hannunta ta yi dan tsananin zafi. Tana cikin shafa masa towel ta ji ya fara sunbatu cikin baccinsa.
"Ku yi haƙuri, ni ba Azzalumi bane. Ku yi haƙuri kada ku tsine min, ku yi haƙuri"
Hawaye ya sakko mata dai dai lokacin da ta dafe goshinsa tana karanto masa Ayatul Kursiyyu.
Gaskiya ta so kanta dayawa, tana sane da cewa akwai sihiri a jikinsa amma ta shure ƙafa ta wuce makaranta, ɗaukan fansa kawai ta saka a gaba ta manta cewa yana buƙatar taimakonta. Idan da ace duk watannin da ta ɗauka ta yi su ne cikin nema masa magani ƙila da ya samu waraka tuntuni, ƙila ma ba za a kai matsayin da su ke yanzu ba.
Ba abinda za ta ce sai dai Alhamdulillah kawai tunda Allah bai ba shi damar idda nufinsa na yin kisan kai ba.
Wani abu daya ƙara saka mata zubar hawaye shine tunanin bayan sihiri Gwamna yana fama da ciwon damuwa. He is depressed, akwai yiwuwar zai iya samun matsalar ƙwaƙwalwa duba da irin maganganun da yai ɗazu da kuma magagin bacci da ya ke yi.
Ta cigaba da shafe masa jiki da ruwan sanyi har zuwa Asuba lokacin da zazzaɓin ya sauka.
Da safe Gwamna ya buɗe ido ya kalleshi kwance kan gado gefensa Asiya da kuma likitan da ya ke ƙoƙarin ɗaura masa ruwa.
"Asya" ya kira da dasashshiyar murya.
"Excellency ya jiki?"
Shima Likitan na shi Dr Haruna ya tambayi lafiyarsa.
"Kai na ciwo Asya" ya faÉ—a yana binta da ido.
Hannunsa ta kamo ta kissing har sau biyu sannan ta ce " Insha Allah zai dena"
Bayan Likita ya gama saka ruwan Asiya ta biyo bayansa dan ta ji ƙarin bayani daga gare shi. Da Asuba Gwamna ya farka ta taimaka masa ya miƙe zai je banɗaki sai kawai ya riƙe kan sa ya yanki jiki ya faɗi ya suma wannan yasa hankalin Asiya ya tashi har ta kira likitan sa.
"Hajiya Asiya gaskiya Gwamna yana buƙatar hutu sosai, sannan ya kamata ya rage tunani, jininsa ya hau sosai kuma gaskiya hakan na barazana ga lafiyar sa. Idan ya cigaba da tafiya a haka zai iya faɗuwa ya shiga coma koma ya faɗi ya..."
"On whose authority kika kira Likita gidan nan?"
Muryan Bilkisu ya katse Dr Haruna
"Good Morning Mrs Kachallah"
"Dr Haruna bana tunanin yau ranan check up na Gwamna ne"
"Gwamna patient ɗina ne, inada damar zuwa duba shi idan ya buƙaci hakan"
Bilkisu ta kalli Asiya ta ce "Leave us"
Asiya ta yi murmushin yaƙe sannan ta koma ɗakin Gwamna, ba wai ta bi umurninta bane dama dai tana son komawa ɗaki dan ta ga Gwamna.
Lokacin da ta shiga ɗakin yana rigingine da filo ya ƙurawa bangon ɗakin ido kaman mai kallon TV.
"My love za ka iya yin sallar Asuba yanzu ko kuwa sai ruwan ya ƙare za ka yi"
"Zan yi yanzu, ban yi sallar Magariba da Isha ba jiya"