Sashe 17
Matar Gwamna Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Asiya na gida tana zoom call da 'yan study group ɗinta na chan Kuru wannan mummunan labari ya risketa. A gaggauce ta shirya ta nufi Asibiti. Bilkisu Kachallah kawai aka bawa damar ganinsa tun fitowar likitoci daga ɗakin da aka kwantar da shi. Asiya na zuwa securities da su ke tsaron ƙofar su ka bata damar shiga duk da kuwa Bilkisu ta bada umurnin kada su bari wani ya shigo ɗakin.
Asiya ta bishi da ido tun daga tafin ƙafarsa da ke lulluɓe har zuwa goshinsa.
Bilkisu na durƙushe da gwiwowinta ƙasa ta riƙe hannunsa ganin an saka masa oxygen dan taimaka masa wajen numfashi ya ƙara birkitata. Ba abinda ya ke zuwa mata irin ace yanzu mi zai faru idan Saifuddeen ya mutu.
Lokacin da ta tuno da yadda aka yi ya hau kan mulki sai ta firgita sosai. Ba dai za a samu maimaita tarihi ba ne a jihar. Gwamna ya mutu mataimakinsa ya hau kan kujera.
"Nooo" ta furta da ƙarfi ba tareda ta lura da Asiya da ta shigo ɗakin ba.
A ɓangaren Asiya kuwa wani tunani ne ya faɗo mata wanda ya sata zubda ƙwalla. Saboda wannan mata ta rabu da mijinta tsawon watanni, yanzu idan ya rasu babu abu ɗaya na shi da ta ke da shi sai dai ta rayu da tarin dana sani. Ko kyakykyawan zama irin ta ma'aurata ba su taɓa yi ba. Idan Bilkisu ta kashe shi ba ta da asara tunda ga 'ya'ya har uku ta haifa masa zata kallesu ta ji daɗi.
"Zan fita da shi gobe" Asiya ta faÉ—a bayan ta share hawayen da ke fiskarta.
Bilkisu ta juyo ta kalleta amma bata yi magana ba sai kawai ta juyar da kanta ta cigaba da kallon Gwamna da ke kwance.
Sai yamma lis Gwamna ya farfaɗo. Ikon Allah ne kawai ya kiyaye shi bai samu shanyewar ɓarin jiki ba faɗuwar da yai. Likitocin kansu sun yi mamakin farfaɗowansa ba tareda wata babbar matsala ba sai ciwon kai da ciwon ƙirji da ke damunsa.
Bilkisu ta saƙa, ta raya, ta auna komai. Mafita ɗaya ce kawai shine ta bari Asiya ta fitar da Gwamna waje jinya. Abu ɗaya ta sa a ranta shine Asibiti za a kai shi dan duba lafiyar jikinsa ba wai dan ya samu waraka daga ɗaurin da ta masa ba shiyasa ma ta yiwa ɗaya daga cikin bodyguard ɗinta magana akan ta raka Asiya ta tabbatar komai ya tafi dai-dai. Ba dan tana cikin tsaka da wasu ayyuka ba da ita da kanta za ta raka Gwamna. Amma idan ayyukanta su ka yi sauƙi za ta je ta duba shi.
Washegari da safe ƙarfe bakwai ta wuce kaɗan ta yi musu a airport ne, har da Bilkisu aka zo tareda yaransa biyu. Sai a lokacin ne ma Asiya ta ga Junior, yaron kaman ba ɗan shekara bakwai ba gaba ɗaya ya ƙyamushe bashi da walwalar da ta san shi da shi da, yadda ya ke yi ma tamkar bai taɓa sanin Asiya ba a rayuwarsa wannan ya ba Asiya mamaki sosai.
A wheelchair aka tura Gwamna har cikin jirgi saboda ba shi da ƙarfin jiki, tunda ya farfaɗo ɗinma baya magana sai dai ya girgiza kai kawai ko ya zubawa mutum ido.
Asiya tana riƙe da hannun Gwamna jirginsu ya lula sararin samaniya. Fiye da rabin tafiyar su ma Gwamna yayi shi cikin bacci ne.
Tun da Bilkisu ta gaya mata za su tafi tare ne da Mistika sai kawai ta kira Colonel Modi ta roƙe shi alfarma.
Suna sauka a filin jirgin NewYork aka kama Mistika aka tafi da ita bincike sai sunbatu ta ke tana faɗin tare ta ke da tawagar Governor Kachallah amma babu wanda ya saurareta. Tun shirinsu na farko dama mutum huɗu Asiya ta booking mu su, ƙaninta Ɗayyibu da ya samu scholarship karatu a ƙasar Morocco shekaran da ta wuce sai kuma Al'amin ɗan Fatima Kachallah babbar 'yar Alhaji Sani Kachallah...
Bilkisu na zaune a office M Sani ya shigo cikin wata Shaddah blue mai yauƙi. Tunda Bilkisu ta sa aka bashi Commisioner of Youths and Sports yake tsula tsiyarsa a jihar Congo. Dududu shekarunsa ashirin da bakwai ne amma kuma abinda ya ke idan mutum ya ji sai ya tsorata da duniya.
"Boss ya naga kin yanƙwane ne. Ko tun yanzu kin fara kewar Gwamna ne?"
"Muhammad ba za ka gane ba, idan Saifuddeen ya mutu asirina zai tonu a jihar nan"
M Sani ya bushe da dariya yace " shine kike son bawa kan ki hawan jini"
Bilkisu ta jefe shi da mugun kallo
"Think of it this way, idan Uncle ya mutu wa kike ganin zai zama Gwamna a jihar nan?"
Bilkisu ta zaro ido waje.
M Sani yai murmushi sannan yace "idan ya mutu you can easily become the governor of the state"
Ganin bata fahimci maganarsa ba ya sa shi faÉ—in " idan Aka rantsar da mataimakin Gwamna akan kujera kina ganin wa zai É—auko a matsayin deputy É—in sa?. Ba kya ganin kina zama mataimakiyar Gwamna za ki iya hallaka shi ki haye kujerar ko kuma ki sa yai resign na dole. Ya kike gani idan aka kira ki da GOVERNOR BILKISU SANI KACHALLAH?"
Wani murmushi ne ya suɓucewa Bilkisu dan har ta hasko kanta zaune a ofishin Gwamna zaune akan kujerar da ke da daraja ta farko a gaba ɗaya jihar wato first citizen of the state.
"You can make things easy tun yanzu, za ki iya sawa Mistika ta kashe shi a chan kinga waccar yarinyar dole ta dawo ta yi takaba"
"Muhammad Sani!" Bilkisu ta faɗa tana miƙewa tsaye, idonta ya fara rikiɗewa yana komawa na maciji wanda hakan ke faruwa a duk lokacin da ta ke cikin tsananin ɓacin rai.
M Sani ya sha jinin jikinsa dan har sai da ya saki fitsari kaÉ—an.
Ta fi minti biyu kafin ta iya dawowa dai-dai.
"Zan iya yin komai akan mulki amma banda taɓa lafiyar mijina da 'ya'yana. Idan lokacin Saifuddeen ya cika i will mourn him amma ba zan taɓa kashe shi ba, duk wanda ya taɓa lafiyarsa ma sai na ga ƙarshen sa a doron ƙasa"
"Tuba na ke Boss. Ki gafarta min" M Sani ya faÉ—a a tsorace.
"Leave!" Bilkisu ta faÉ—a da kakkausar murya.
14
Sati guda Gwamna yai a Asibiti ya fara samun sauƙi, kullum Asiya tana cikin tofe shi da addu'o'i bayan magungunan da ya ke sha. Tabbas hasashenta yayi gaskiya dan kuwa Gwamna yana fama da depression, jifan da aka mishi ya taɓa shi sosai. Duk lokacin da aka masa maganar abin sai hankalinsa ya tashi.
Therapist ɗinsa musulmi ne mai suna Dr Ayyub Khan dan haka bayan taimako na fannin kimiyya yana bashi shawarwari da kuma amfani da magungunan musulunci, dan tun zuwansu ya tuntuɓi wani abokinsa mutumin Egypt wanda ke da sani akan Ɗibbun Nabawiy (medicine of the prophet) su ke aiki tare wajen ganin Saifuddeen Kachallah ya samu lafiya.
A hankali Gwamna ya fara dawo da walwalarsa har ta kai yana ɗan magana har ya sa baki idan Asiya da su Al'amin suna hira. Sakewa da ya ke ya ƙara saurin samun sauƙinsa.
Satin su huɗu cur a ƙasar Gwamna har ƙiba ya ɗan yi saboda yana samun bacci da kwanciyar hankali yadda ya dace.
Wasu lokaci Asiya ta kan shirya mu su fita strolling da yamma ko kuma da sassafe.
Yau ma fitar su ka yi da dare bayan sun yi sallar Isha, kasancewa ana yanayi na sanyi dukkan su sun yiwa jikinsu tanadin sanyi. Gwamna na sanye da wandon jeans baƙi, black turtle neck shirt da kuma navy blue jacket, hannayensa sanye da baƙin safa. Itama Asiya irin shigar ta sa ta yi banbancin nata jacket ɗin dogo ne sannan ita ta ɗaura brown scarf a wuyanta kanta kuma sanye da baƙar turban. Hannunsu sarƙe cikin na juna su ke tafiya, labarin zuwanta Saudiyya ta ke bashi wannan yasa ya maida hankalinsa kan ta sosai bai ma lura da ya hau hanya ba sai da ya ji ihunta ta jawoshi da ƙarfi.
"Ya Allah!" Ta faɗa tana dafe ƙirjinsa. Shi kuma mai motar da ya kusa buge Saifuddeen bai tsaya ba sai ma ihunsa da suka ji yana faɗin "fuck off man"
Asiya ta bishi da daƙuwa tana faɗin "Ashole"
Kafin ta juyo Gwamna ya jawota jikinsa ya rungumeta tsam a ƙirjinsa. Turawa babu ruwansu dan haka kowa harkan gabansa ya ke babu wanda ya kula da su.
"Excellency abakin titi fa mu ke" ta faɗa da wata ƙaramar murya wanda rabon da ta masa irin wannan har ta manta. Bai saketa ba sai da suka yi kusan minti biyar a gefen titi rungume da juna and all that matters a lokacin shine zuciyoyinsu na bugawa ne da soyayyar junansu.
Lokacin da suka koma hotel suite É—insu kusan dare ya raba, su kan mazan tuni sun yi bacci, ba kamar ÆŠayyibu ma wanda sanyin garin ke damunsa baya ma wani fita sosai.
Ba su fi minti biyar da kwanciya ba ta ji hannunsa a cikinta. Shafa mata ciki ya fara a hankali hakan ya sa tsikar jikinta ya fara tashi. Ya matso da ita jikinsa yana shafa cikinta zuwa chan ƙasan maranta. A hankali kuma ya sa bakinsa a wuyanta yana kissing ɗinta a hankali chan kuma ya juyo da fiskarta ya haɗe bakinsu. Ta yi kewarsa sosai shiyasa jikinta ya shiga mazari lokacin da ya fara yawo da hannayensa a saman ƙirjinta. Kafin ta ankara ya rabata da wandon pyjamas ɗinta ya fara wasa da cinyoyinta.
Ganin wasan na su ya fara wuce gona da iri yasa ta fara ƙoƙarin janye jikinta amma yai mata kane-kane bai bata dama ba. A hankali ya fara shigarta wannan ya sa Asiya ta furta addu'ar saduwa a fili "Bismillah, Allahumma Jannibnash-shayɗaana, wa jannibish shayɗaana ma razaqtanaa"
Shima sai ya faɗi "Bismillah" a fili sannan ya tura ciki da ɗan ƙarfi wannan yasa Asiya ta ƙanƙameshi tana cize leɓe...
A dai-dai wannan gaɓa zoben hannun Bilkisu ya kawo wani jan haske kamar wuta sai kuma ya disashe hasken ya ɓace ɓat. Da ke bacci ta ke bata ga abinda zoben yai ba.
Asiya ta bishi da ido tun daga tafin ƙafarsa da ke lulluɓe har zuwa goshinsa.
Bilkisu na durƙushe da gwiwowinta ƙasa ta riƙe hannunsa ganin an saka masa oxygen dan taimaka masa wajen numfashi ya ƙara birkitata. Ba abinda ya ke zuwa mata irin ace yanzu mi zai faru idan Saifuddeen ya mutu.
Lokacin da ta tuno da yadda aka yi ya hau kan mulki sai ta firgita sosai. Ba dai za a samu maimaita tarihi ba ne a jihar. Gwamna ya mutu mataimakinsa ya hau kan kujera.
"Nooo" ta furta da ƙarfi ba tareda ta lura da Asiya da ta shigo ɗakin ba.
A ɓangaren Asiya kuwa wani tunani ne ya faɗo mata wanda ya sata zubda ƙwalla. Saboda wannan mata ta rabu da mijinta tsawon watanni, yanzu idan ya rasu babu abu ɗaya na shi da ta ke da shi sai dai ta rayu da tarin dana sani. Ko kyakykyawan zama irin ta ma'aurata ba su taɓa yi ba. Idan Bilkisu ta kashe shi ba ta da asara tunda ga 'ya'ya har uku ta haifa masa zata kallesu ta ji daɗi.
"Zan fita da shi gobe" Asiya ta faÉ—a bayan ta share hawayen da ke fiskarta.
Bilkisu ta juyo ta kalleta amma bata yi magana ba sai kawai ta juyar da kanta ta cigaba da kallon Gwamna da ke kwance.
Sai yamma lis Gwamna ya farfaɗo. Ikon Allah ne kawai ya kiyaye shi bai samu shanyewar ɓarin jiki ba faɗuwar da yai. Likitocin kansu sun yi mamakin farfaɗowansa ba tareda wata babbar matsala ba sai ciwon kai da ciwon ƙirji da ke damunsa.
Bilkisu ta saƙa, ta raya, ta auna komai. Mafita ɗaya ce kawai shine ta bari Asiya ta fitar da Gwamna waje jinya. Abu ɗaya ta sa a ranta shine Asibiti za a kai shi dan duba lafiyar jikinsa ba wai dan ya samu waraka daga ɗaurin da ta masa ba shiyasa ma ta yiwa ɗaya daga cikin bodyguard ɗinta magana akan ta raka Asiya ta tabbatar komai ya tafi dai-dai. Ba dan tana cikin tsaka da wasu ayyuka ba da ita da kanta za ta raka Gwamna. Amma idan ayyukanta su ka yi sauƙi za ta je ta duba shi.
Washegari da safe ƙarfe bakwai ta wuce kaɗan ta yi musu a airport ne, har da Bilkisu aka zo tareda yaransa biyu. Sai a lokacin ne ma Asiya ta ga Junior, yaron kaman ba ɗan shekara bakwai ba gaba ɗaya ya ƙyamushe bashi da walwalar da ta san shi da shi da, yadda ya ke yi ma tamkar bai taɓa sanin Asiya ba a rayuwarsa wannan ya ba Asiya mamaki sosai.
A wheelchair aka tura Gwamna har cikin jirgi saboda ba shi da ƙarfin jiki, tunda ya farfaɗo ɗinma baya magana sai dai ya girgiza kai kawai ko ya zubawa mutum ido.
Asiya tana riƙe da hannun Gwamna jirginsu ya lula sararin samaniya. Fiye da rabin tafiyar su ma Gwamna yayi shi cikin bacci ne.
Tun da Bilkisu ta gaya mata za su tafi tare ne da Mistika sai kawai ta kira Colonel Modi ta roƙe shi alfarma.
Suna sauka a filin jirgin NewYork aka kama Mistika aka tafi da ita bincike sai sunbatu ta ke tana faɗin tare ta ke da tawagar Governor Kachallah amma babu wanda ya saurareta. Tun shirinsu na farko dama mutum huɗu Asiya ta booking mu su, ƙaninta Ɗayyibu da ya samu scholarship karatu a ƙasar Morocco shekaran da ta wuce sai kuma Al'amin ɗan Fatima Kachallah babbar 'yar Alhaji Sani Kachallah...
Bilkisu na zaune a office M Sani ya shigo cikin wata Shaddah blue mai yauƙi. Tunda Bilkisu ta sa aka bashi Commisioner of Youths and Sports yake tsula tsiyarsa a jihar Congo. Dududu shekarunsa ashirin da bakwai ne amma kuma abinda ya ke idan mutum ya ji sai ya tsorata da duniya.
"Boss ya naga kin yanƙwane ne. Ko tun yanzu kin fara kewar Gwamna ne?"
"Muhammad ba za ka gane ba, idan Saifuddeen ya mutu asirina zai tonu a jihar nan"
M Sani ya bushe da dariya yace " shine kike son bawa kan ki hawan jini"
Bilkisu ta jefe shi da mugun kallo
"Think of it this way, idan Uncle ya mutu wa kike ganin zai zama Gwamna a jihar nan?"
Bilkisu ta zaro ido waje.
M Sani yai murmushi sannan yace "idan ya mutu you can easily become the governor of the state"
Ganin bata fahimci maganarsa ba ya sa shi faÉ—in " idan Aka rantsar da mataimakin Gwamna akan kujera kina ganin wa zai É—auko a matsayin deputy É—in sa?. Ba kya ganin kina zama mataimakiyar Gwamna za ki iya hallaka shi ki haye kujerar ko kuma ki sa yai resign na dole. Ya kike gani idan aka kira ki da GOVERNOR BILKISU SANI KACHALLAH?"
Wani murmushi ne ya suɓucewa Bilkisu dan har ta hasko kanta zaune a ofishin Gwamna zaune akan kujerar da ke da daraja ta farko a gaba ɗaya jihar wato first citizen of the state.
"You can make things easy tun yanzu, za ki iya sawa Mistika ta kashe shi a chan kinga waccar yarinyar dole ta dawo ta yi takaba"
"Muhammad Sani!" Bilkisu ta faɗa tana miƙewa tsaye, idonta ya fara rikiɗewa yana komawa na maciji wanda hakan ke faruwa a duk lokacin da ta ke cikin tsananin ɓacin rai.
M Sani ya sha jinin jikinsa dan har sai da ya saki fitsari kaÉ—an.
Ta fi minti biyu kafin ta iya dawowa dai-dai.
"Zan iya yin komai akan mulki amma banda taɓa lafiyar mijina da 'ya'yana. Idan lokacin Saifuddeen ya cika i will mourn him amma ba zan taɓa kashe shi ba, duk wanda ya taɓa lafiyarsa ma sai na ga ƙarshen sa a doron ƙasa"
"Tuba na ke Boss. Ki gafarta min" M Sani ya faÉ—a a tsorace.
"Leave!" Bilkisu ta faÉ—a da kakkausar murya.
14
Sati guda Gwamna yai a Asibiti ya fara samun sauƙi, kullum Asiya tana cikin tofe shi da addu'o'i bayan magungunan da ya ke sha. Tabbas hasashenta yayi gaskiya dan kuwa Gwamna yana fama da depression, jifan da aka mishi ya taɓa shi sosai. Duk lokacin da aka masa maganar abin sai hankalinsa ya tashi.
Therapist ɗinsa musulmi ne mai suna Dr Ayyub Khan dan haka bayan taimako na fannin kimiyya yana bashi shawarwari da kuma amfani da magungunan musulunci, dan tun zuwansu ya tuntuɓi wani abokinsa mutumin Egypt wanda ke da sani akan Ɗibbun Nabawiy (medicine of the prophet) su ke aiki tare wajen ganin Saifuddeen Kachallah ya samu lafiya.
A hankali Gwamna ya fara dawo da walwalarsa har ta kai yana ɗan magana har ya sa baki idan Asiya da su Al'amin suna hira. Sakewa da ya ke ya ƙara saurin samun sauƙinsa.
Satin su huɗu cur a ƙasar Gwamna har ƙiba ya ɗan yi saboda yana samun bacci da kwanciyar hankali yadda ya dace.
Wasu lokaci Asiya ta kan shirya mu su fita strolling da yamma ko kuma da sassafe.
Yau ma fitar su ka yi da dare bayan sun yi sallar Isha, kasancewa ana yanayi na sanyi dukkan su sun yiwa jikinsu tanadin sanyi. Gwamna na sanye da wandon jeans baƙi, black turtle neck shirt da kuma navy blue jacket, hannayensa sanye da baƙin safa. Itama Asiya irin shigar ta sa ta yi banbancin nata jacket ɗin dogo ne sannan ita ta ɗaura brown scarf a wuyanta kanta kuma sanye da baƙar turban. Hannunsu sarƙe cikin na juna su ke tafiya, labarin zuwanta Saudiyya ta ke bashi wannan yasa ya maida hankalinsa kan ta sosai bai ma lura da ya hau hanya ba sai da ya ji ihunta ta jawoshi da ƙarfi.
"Ya Allah!" Ta faɗa tana dafe ƙirjinsa. Shi kuma mai motar da ya kusa buge Saifuddeen bai tsaya ba sai ma ihunsa da suka ji yana faɗin "fuck off man"
Asiya ta bishi da daƙuwa tana faɗin "Ashole"
Kafin ta juyo Gwamna ya jawota jikinsa ya rungumeta tsam a ƙirjinsa. Turawa babu ruwansu dan haka kowa harkan gabansa ya ke babu wanda ya kula da su.
"Excellency abakin titi fa mu ke" ta faɗa da wata ƙaramar murya wanda rabon da ta masa irin wannan har ta manta. Bai saketa ba sai da suka yi kusan minti biyar a gefen titi rungume da juna and all that matters a lokacin shine zuciyoyinsu na bugawa ne da soyayyar junansu.
Lokacin da suka koma hotel suite É—insu kusan dare ya raba, su kan mazan tuni sun yi bacci, ba kamar ÆŠayyibu ma wanda sanyin garin ke damunsa baya ma wani fita sosai.
Ba su fi minti biyar da kwanciya ba ta ji hannunsa a cikinta. Shafa mata ciki ya fara a hankali hakan ya sa tsikar jikinta ya fara tashi. Ya matso da ita jikinsa yana shafa cikinta zuwa chan ƙasan maranta. A hankali kuma ya sa bakinsa a wuyanta yana kissing ɗinta a hankali chan kuma ya juyo da fiskarta ya haɗe bakinsu. Ta yi kewarsa sosai shiyasa jikinta ya shiga mazari lokacin da ya fara yawo da hannayensa a saman ƙirjinta. Kafin ta ankara ya rabata da wandon pyjamas ɗinta ya fara wasa da cinyoyinta.
Ganin wasan na su ya fara wuce gona da iri yasa ta fara ƙoƙarin janye jikinta amma yai mata kane-kane bai bata dama ba. A hankali ya fara shigarta wannan ya sa Asiya ta furta addu'ar saduwa a fili "Bismillah, Allahumma Jannibnash-shayɗaana, wa jannibish shayɗaana ma razaqtanaa"
Shima sai ya faɗi "Bismillah" a fili sannan ya tura ciki da ɗan ƙarfi wannan yasa Asiya ta ƙanƙameshi tana cize leɓe...
A dai-dai wannan gaɓa zoben hannun Bilkisu ya kawo wani jan haske kamar wuta sai kuma ya disashe hasken ya ɓace ɓat. Da ke bacci ta ke bata ga abinda zoben yai ba.