← Book details Garkuwa Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 45

Sashe 27

Garkuwa Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Gaba É—aya su suka maida kallonsu kan Hajia Mama nan take LamiÉ—o da Galadima da Abba suka É—iga ayar tambaya a kanta.
itako ganin bawai magana Jafar É—in keyiba sai bata damuba bata kuma fahimci cewa sun zargi meyafaru ba kuma basu gane me. Jafar É—in yake cewa ba da hakan ba.
Hajia mama kuwa cikeda da karfin hali irin nata na makiran mugaye mata tafara tafa hannu tana masar kwalla tana faÉ—in
"Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un Jafar me nake gani haka me yasami Mamey'n ku? kayi magana mana".

Sai kuma tasaki kuka mai haÉ—e da salati.
LamiÉ—o ne yaÉ—anyi gyaran murya ganin Mamey'n tafara motsawa alamar tafarka daga nannauyan Baccin da take mikewa tayi zaune tare da zuba musu ido.
Da sauri suka É—an matso gareta kana duk suka mai da hankalin su kanta.
Suna ce mata sannu Aisha, Amman shiru ba amsa.
Cikin tsananin sauri da tsoro Abba ya matso kusa da ita tare da zubawa yatsun kafarta ido mamaki cike da kiÉ—ima yake kallon yatsun kafarta da suka fara sauya kamannin halitta suka koma kamar na tsuntsu.

Cike da alhini suma su LamiÉ—o suke kallon yatsun kafar nata, hankali a tashe.
Cikin gigita Abba ya kamo hannunta tare da nunawa LamiÉ—o murya a daburce yace.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun LamiÉ—o kalli yatsunta".
wani matsanancin tashin hankalin ne yakuma dabaibayesu lokacin da suka ga yatsun hannunta yafara komawa irinna fiffiken tsuntsu.
Gaba ki É—aya su haÉ—a baki sukayi wajan furta "innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un hasbullahu wani'imalwakin". Sabida tsananin firgici da tashin hankali gaba É—aya jikinsu rawa yakeyi.

Cikin matsanan cin tashin hankali LamiÉ—o da cushewar tunani LamiÉ—o ya juyo ya kalli Galadima murya a hargitse yace.
"Subahanallahi maza a kira Malam Musa yanzu nan".
Cikin hanzari Galadima ya amsa da. "To". Kana yajuya da sauri yafita.

Kan kace me labari yabaza masarautar JoÉ—o,
Batare da bata lokaci ba sakon kiran da LamiÉ—o yayiwa Malam Musa ya isa gareshi.

Cikin ƴan daƙiƙu malam Musa ya iso cikin masarautar Joɗa Lamiɗo yabada umurnin a shigo dashi har cikin ɗakin Mamey.

Yana shiga kallonta malam Musa yayi cikin tashin hankali ya girgizata kai kana yakallesu LamiÉ—o yace.
"Sihirine a kamata mai haÉ—e da tsafi kuma daga yanzu zuwa ko yaushe ko wanne lokacin zata iya juyewa daga mutun ta dawo tsunsuwa".
Salati suka É—auka baki É—ayansu nan kuma É—akin yakacame da koke-koke su Jamil da Jalal Affan Ummi Jafar yayin da duk muryar Hajia Mama yafi amo wajen kuka da shiga tashin hankali ziraran miraran.
(uhum makircin mugu kenan.)
(Sai daifa akwai kishiyoyi na gari da matsalar kishiya kan sasu kukan gaske wlh.)

Ranar kuwa wannan masarautar taga tashin hankali mara misaltuwa,
Jiƙe-jiƙe da hayaƙi da shafe-shafen magungun gargajiya babu wanda malam Musa baiba, kiɗima yasa sun mance da suyi amfanin da ayatul shifa.
Ganin anyi duk abinda za'ayi na gargaji abin yaci tura ne yasa hankalin.
Dr Aliyu yakasa ƙwanciya gani yake ko wata cutarce ta da ban haka yasa ya fitadaga ɗakin yatafi part ɗin sa,
kiran wasu manyan likitoci a bokansa.
Yasanar musu koda wani shawarin da zasu basu bayan sun gama wayar kuwa.
Kayan ai kinsa ya É—auko yakomo É—akin Mamey'n yayi iya gwaje-gwajen sa babu abinda ya gane na wani cuta ko wani abu.
Cikin takaici Malam Musa yace.
"Kama bar gwada ta babu wani cuta face sihiri".
Daga karshe dai dole ya hakura.
Ranar babu wanda ya rumtsa kusan a tsaye suka kwana nan cikin É—akin Mamey'n ganin yadda gaba É—aya kamannin halittarta ke juyewa, Gimbiya Aminatu tayi kuka iya kuka.
LamiÉ—o ya kira Jadda ya sanar mishi halin da ake ciki tashin hankali iya tashin hankali Jadda da Sitti sun shigeshi nan suka fara shirin tahowa.

Can gabanin kiran sallar asuba lamari ya ƙara munana dan a lokacin suffar Mamey ta gama juyewa izuwa na tsunsuwar Boleru a gabana a gabansu Lamiɗo a gaban mafiya yawan al'ummar Masarautar Joɗa.
nan take kuwa Abba ya yanke jiki yafaÉ—i yasuma.
Cikin kiÉ—ima Dr Aliyu yayi kansa yafara bashi taimakon gaggawa.
Mamey kuwa da yanzu takoma tsuntsuwa fara kaÉ—a fiffikenta tayi alamun son tashi take.

Ai kuwa tamkar al'mara sai gashi ta tashi firr ta fire tabi ta window dake a buÉ—e tayi tacikin Garden tashige cikin tawagarsa tsuntsayen dake wurin.

Innalillahi Jamil Jalal kuwa suma sumewa sukayi.
Cikin hanzari da kiÉ—ima LamiÉ—o da Galadima suka zo jikin window nan suka hango ta ta sauka cikin tsuntsayen kawai sai suka fashe da kukan tsoron al'amarin duniya.

Wani irin kuka Hajia Mama tasaka tana faÉ—in "wayyo Allah na waishin meke faruwa damune kam".
sai kawai ta yanke jiki tafaÉ—i ta kakkafe idanunta kamar wacce ta suma.

Ranar Hajia Mama haka tawuni tana kuka ta rungume Jamil da Jalal dasuke keta kuka kamar ransu zai fita.

Jadda da Sitti da Umaymah da Aunty Juwairiyya da babanta duk a ranar sukazo.
An kamo tsuntsuwar Boleru suna killaceta, yayinda aketa tururuwan zuwa ganin tsuntsuwar.

Ido da ido da Gimbiya Saudatu tazo da yake sokuwace.
Sai cewa tayi.
"Allah sarki wato al'haƙi kuikuyo ko sharrinta ya dawo kanta, ohoho larabawa an zama tsuntsuwar Boleru".
Toh fa daga nanne Magautan su Sheykh duk suka samu suka fake suka laɓe a bayanta.

Su kuwa haka sukaci gaba da kukan Hajia Mama ko uwartace ta mutu sai haka, duk wanda yaganta sai ta bashi tausayi akasin LamiÉ—o da Galadima da suka sa zargi a kanta duk abin da take shirine da zallar iya tuggu munafurci da makirci.

Tun daga lokacin tsuntsuwar nan ko ince Mamey ko yaushe sai ana kamata ita kuwa tana firewa tana komawa cikin tsuntsaye Æ´an uwanta.
Al'amarin ya magaga ya tada hankalin kowa.
Ana kamata zata zille ta fire ta koma cikin Garden ta zauna cikin tsuntsayen cikin masarautar JoÉ—a.

Duk wannan tashin hankali da ake ciki Sheykh Jabeer bashida labari dan lokacin yana karatu a jami'ar Madina sai dai kwata-kwata a lokacin hankalinsa yakasa ƙwanciya idan yakira wayar Mamey'n sai asa Aunty Rahma ta ɗauka tayi mishi mgn wanda ita kuma dama lokacin sun zo suna nan da Mamma.
Yadda Hajia Mama ke nuna tashin hankali tane yasa suka yarda da ita.

Wannan juyewar Mamey shine.
Sanadin da Jadda ya samu hawan jini kenan.

A ranar da dare Umaymah Mamma Aunty Rahma Aunty Juwairiyya Sitti duk sun gaza bacci, sun sa tsuntsuwar Boleru a gaba Magauta na musu dariya.

Sai da asubane sun kabbarta yin salla asuba, tsuntsuwar ta tashi ta fire, Bata tsaya cikin masararutar Joɗa bama ta fuskanci ƙasar Cameroon ta nausa tayi can yankin Yahunde.

Ɓacewar tsuntsuwar nan shi yafi tada musu hankali.
Anyi neman duniya har an gaji.
Ba ita ba dalilinta har dai aka ruggumi ƙaddara.

Sai dai LamiÉ—o da Galadima da Jadda da Umaymah sunci gaba da bincikawa da neman mafita.

Lokacin da Sheykh ya kammala digirin sa na farko yazo.
Nigeria nan ne ake faɗa masa abin da ya faru a lokacin tashin hankalin da kiɗimar rayuwar daya faɗa ciki baya misaltuwa wani babban tashin hankalin kuwa shine daya iske ya Jafar baya magana sai addu'o'in da yin karatun al'ƙur'ani mai girma da kuka, dakuma ya buƙaci yaje yaga Mamey'n shi a yadda take ɗin a tsuntsuwar ta ɗin, nan ake faɗa masa ai tun lokacin da abun yafaru da kwana ɗaya rak ta fire tabar cikin masarautar Joɗa.

Ranar Sheykh kuka kamar karamin yaro ya rungume Jamil Jalal Yah Jafar da tun isowarsa Jafar ɗin ke ƙanƙame da hannun sa yana karatun yana kuka haka sukayi ta kuka Hajia Mama na tayasu.
Ranar tazamo musu tamkar sabuwa.

Tun daga wannan lokacin kuma sai yazamo kamar an cire hankalin Abba'n su a kansu madadin a lokacin ya janyosu jikinshi yazame musu Garkuwa dan suɗan sami sassaucin kunar dake cikin zuciyarsu sai yariƙa nisanta kanshi dasu.
Shi kansa bai san dalilin hakan ba,
duk wannan kuma acikin shirin Hajia Mama ce, kwana É—ayan da tsuntsuwar tayi tafire ma ita takoma gun bokanta tace tanaso tsuntsuwar tabar cikin masarautar gaba É—aya dan taga sun dage da magungunan.
Dariya bokan nata yayi tare da cewa.
"Ke shar-shar banza da kika samu ma ba Addu'o'inku na musulmai sukeyiba ai da tuni sun karya sihirin".
Cikin jin daÉ—i tace.
"Aini gaba ta kaini da hankalin su baije ga canba".

Lamiɗo kuwa lokacin ya ƙara jan Sheykh a jiki sosai.
Sabida bayanin da Malam Musa yayi musu na cewar a sanadin aurensa da ba fulatanar daji mahaifiyarsu zata dawo.
Haka yasa part in da a ka bashi kusa da Garden inda tsuntsayen suke.
aka buÉ—e mishi wata kofa taciki in da daga cikin part É—in direct zai sadashi da cikin Garden É—in.

Bai wani jima sosai a Nigeria ba yakoma Madina sabida jin yakeyi ya tsani ƙasar Nigeria Especially Masarautar Joɗa.
Koda ya koma sosai Æ´an uwan Sitti suka ga canji a rayuwarsa saida aka dage da addu'a kafin ya dawo hayyacinsa.
Daga nan suka ƙara kula ta musamman a kanshi suka zame mishi uwa uba ƙanne yayu sukeyi mishi komai.
Yakanyi shekara uku huÉ—u bai zoba.
Sai dai yana yawan sawa Jadda yazo mishi da Jamil Jalal Yah Jafar da Affan yawanci duk shekara zasu zo sau biyu hajji da umra wani shekaranma sau uku.
Ya maida hankali sa kan karatunsa da addu'a Allah ya baiya mishi Mameynshi a duk inda take ko a tsuntsuwar Boleru shi zaici gaba da rainonta da kula da ita iya rai da mutuwa.

Daga nan yayi master's madadin ya dawo ya haÉ—e. PHD É—insa. daga nan yadawo Nigeria'n bisa tirsasawar LamiÉ—o da Jadda da Galadima da Umaymah dake matsayin Uwa.
Dole ya yarda ya dawo ya sanyawa ƙannensa ido wajen kula da su dakuma tarbiyyan su dakuma neman hamaifiyar su da kula da yayansa yakuma zame musu Garkuwa Da kuma bincikar Magautansu wanda dalilin haka ya samu matakin SS wanda dama shine burinsa to kuma Alhamdulillah ya gane komai Especially da ya samu damar aikin SS wanda dama burinshi kenan a dole Lamiɗo ya sashi karantan likitancin.

A kwai sabo ƙauna tausayi da shaƙuwa da tsama tsakaninshi da kakanun nashi sosai.

Hajia Mama kuwa da gayya ya barta da wayonta ita tanayi mishi kallon biri shi yana mata kallon ayaba.
Chapter 27 · 0% Book details