← Book details Exiled Prince Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 61

Sashe 8

Exiled Prince Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

washe baki ta yi ta na zaro idanu ta ce " da gaske yaya Abdoul ? "
gyada mata kai ya yi a hankali ya na shirin magana ya ga ta tashi da gudu ta bar wajen da sauri Tesnim ta ce mata " Yi a hankali " ta na gama fadar haka ta ga Inaya ta rage gudun ta na tafiya da sauri
dama Abdoul wayo ya yi mata dan ta ba shi wuri ya yi magana da tashi babyn

sai da ya ga ta kurewa ganin su , sannan ya tashi ya koma saman sofar da Tesnim ke zaune
da sauri ta matsa ta na fadin " kai malam minene haka , tashin min da ga nan "

ya na kallon cikin idanun ta ya ce " okay give me a map "

cikin rudu ta ce mishi " map ? "

gyada mata kai ya yi kafin ya ce " yeah a map , because i keep getting lost in your eyes "

Ba ta san lokacin da ta bushe da dariya ba , har wadanan fararen hakwaren nata su ka fito
shi kuma Abdoul ya na ganin ta fara dariya ya saki wani cool murmushi ya na kallon , sai da ya ga ta tsagaita dariyar ta sannan ya mike ya na cewa " na gama Mission di ta "

kallon shi ta yi ta na daga gera guda ta ce " Wace mission ? "
" make you smile , you've got a cute smile " ya na gama fadar haka ya kashe mata ido guda ya fara takawa ya bar wajen

da kallo ta raka har sai da ya yi dan nisa kafin ta juya ta na ci gaba da sakin murmushi
kamar da ga sama ta jiyo Muryar Rouksar ta na fadin " Tes , ba dai kin fada soyayyar wannan dirty boy ba ? "

a hankali Tesnim ta juya kai ta kali Rouksar da ke tsaye a bayan ta ta nade hanayan ta a kirji
mikewa Tesnim ta yi kafin ta tako ta karaso wajen Rouksar ta riko hannun ta , ta na cewa " wassa ne kawai ya ke min , mu je yanzu " ta fada ta na fara takawa ta na janye da Rouksar kamar rakoumi da akala

▪MALIK

konce ya ke saman katafaren bed din shi , da ga shi sai short da singlet , ya na fuskantar ceiling ya lumshe idanun shi ya daura hannu guda saman forehead ya tafi duniyar tunanin shi

ya na a haka kawai ya ji an konto saman shi a jiki , a hankali ya dago hannu ya daura saman bayan ta ba tare da ya bude idanun shi ba ya ce " ina ki ka tsaya ? "

a hankali ta dago da ga jikin ta mike zaune saman kugun shi ta na turo dan bakin nan nata ta ce " ta ya a ka yi ka san ni ce ? "

slowly ya ware idanun shi , sai saman face din ta ko
a hankali ya dago hannun ya daura saman kumatun ta ya ce " Kin san qamshin turaren ki na daban ne , Ko a ina na jiyo shi zan iya gane shi "

wani dan karamin murmushi ta saki kafin ta sa hannu ta cire Alkyabar jikin ta , ta tila saman chair
" baby zan shiga na yi wanka " ta fada ta na kokarin tashi da ga saman shi

da sauri ya riko ta ya na cewa " kin gama da ni ne ? "
" kamar ya ? " ta tambayeshi ta na daga gera guda
bai ce mata komai ba ya kai hannun shi a bayan ta ya zuge zip din gown din ta , sannan ya dawo da hannayan shi kassa ya fara tataro gown din ta ya yi sama da ita ya cire mata ita sannan ya tila ta saman Chair saman Alkyabar ta

turo mishi dan bakin nan nata ta yi ta na cewa " yaya Zayd ni ka kyale ni wanka na ke son na je na yi , ba ka ga lokacin sallat ya kusa ba "

" eh na gani , and so what ? duk dai wayon ki ba za ki bar wajen nan ba , ko da wankan ki ka shiga za ki fito ki tardo ni " ya fada ya na kokarin cire mata bra

" To ka bari na je na yi wanka mana " ta fada cike da shagwaba

a hankali ya mike zaune ya jingina bayan shi a jikin forehead din gadon , ya zaunar da ita saman cinyoyin shi
kare mata kallo da kyau ya yi kafin ya ce " da gaske za ki dawo ? " ya kai karshen ya na matse gera

wani dan karamin murmushi ta saki ta na fadin " Da gaske zan dawo "

shiru ya yi ya na kallon ta babu ko kiftawa , sai da ya dauki lokaci a haka kafin ya ce mata " ban yarda ba "
har ta bude baki za ta yi magana kawai ta ji saukar lips din shi saman nata ya cabko lips din ta na kassa
dan zaro idanu ta yi ta na kallon shi , ya lumshe idanun shi ya na kissing din ta cikin konciyar hankali
ta na a haka ta ga ya bude idanun shi a hankali , sai cikin nata ko
daga mata gera guda ya yi allamun minene ?
da sauri ta girgiza mishi kai dan babu bakin maganar

a hankali ya zame bakin shi da ga cikin nata ya koma ya jingina bayan shi a forehead din gadon , ya lumshe idanun shi a hankali kamar mai jin barci ya na ci gaba da kallon ta

wani cool murmushi ta sakin mishi kafin ta ce " baby , mu je na yi maka wanka "

noke mata kafada ya yi allamun ba ya so
turo dan bakin nan nata ta yi ta na shirin magana ya riga ta cewa " ci gaba da turo min dan bakin nan "

da sauri ta katse shi da cewa " Na turo , na turo me za ka yi , ai baki na ne "

" To ke din fa , ta waye ce ? " ya fada ya na daga mata gera guda

turo dan bakin nan nata ta yi ta kauda kai gefe ta na dan karamin gunguni
ta na haka kawai ta yi ya zagayo da hannayan shi a kugun ta ya janyo ta jikin shi , ya kai bakin shi saitin kunnen ta ya yi mata rada ya ce " Ki na zuwa Honey moon ? "

wata yar karamar dariya ta yi kafin ta juyo ta kaleshi ta na cewa " Da gaske baby ? "

gyada mata kai ya yi allamun eh ba tare da ya ce komai ba
a hankali ta sakalo da hanayan ta a wuyan shi ta matso da face din ta ta ce " yaushe za mu tafi "

a hankali ya fara shafa bayan ta ya na cewa " Friday "
dan zaro idanu ta yi ta na cewa " gobe Fa ? "
gyada mata kai ya yi ya na cewa " yeah gobe , fada min ina ki ke son mu je ? "
da sauri ta ce mishi " US ! "
" US ? " ya tambaye ta ya na daga gera guda
gyada mishi kai ta yi ta na shagwabe fuska

a hankali ya kai bakin shi saman kumatun ta ya manna mata kiss sannan ya sauko saman shoulder din ta ya yi mata kiss nan ma ya na cewa " An gama ran ki shi dade , ki na da bukatar wani abu bayan wannan ? "

dan jinkirtawa ta yi kafin ta ce " wanka na ke son na yi "

" okay you can go , but you must kiss me before "

murmushi mai dan sauti ta yi kafin ta kai bakin ta saman kumatun shi ta manna mishi kiss , sannan ta juya saman dayan , sannan ta yi mishi a saman forehead da kuma saman lips din shi kafin ta ce mishi " I really love you baby " ta na gama fadar haka ta sauka da ga saman shi ta sauko gadon ta nufi toilet da gudu

da kallo ya rakata har sai da ta shiga toilet sannan ya bude baki a hankali ya ce " I love you my Cutie " da ga haka ya daga kai sama ya lumshe idanun shi

ya na zaune a haka har ta yi wankan ta , ta fito daure da towel a kirjin ta , kai tsaye dressing room ta wuce
jim kadan ta fito sanye da wata Abaya red color , ta yafo veil din ta a kai ta na taku a hankali ta nufi dressing mirror
duk abun da ta ke ya na kallon ta , sai da ya ga ta tsaya gaban dressing mirror sannan ya sauko da kafafun shi kassa ya mike tsaye ya fara takawa ya nufi toilet ya shiga

jim kadan ya fito sanye da bathrobe , ya na fitowa ya tardo tsaye saman daddumar ta , ta na sallat
bai bi ta kan ta ba ya wuce dressing room , ko two minutes bai yi ba ya fito sanye wani trouser navy blue , da riga white color dai'dai guyiwa ta na da dogayen hannu , a geffen dama an daura wani Tissu Navy blue kamar jacket haka har zuwa guyiwa shi ma , ya saka wasu sneakers farare kal , ya daure wanan lalawsan gashin kan shi a baya ya zubo wasu sirarren gaban goshi sai tashin qamshi ya ke
kai tsaye bedroom din fita ya kama hanyar mosque duk da ya san yanzu sun ma Kamala sallat

▪AFTER SOME MINUTES

zaune su ke a parlourn shi na floor na uku shi da Diya ,
cikin nitsuwa Malik ya ce mishi " Bayan mun Kamala zaman fada ina son na bar kassar nan gobe "
Chapter 8 · 0% Book details