← Book details Exiled Prince Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 61

Sashe 1

Exiled Prince Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤
(LOVE MEETS POWER ) 👑🔥

( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )

STORY & WRITTEN BY : MEERAH 👑🔥

BOOK ________3 ✍📚🔥

P A G E 1 🥀 ❤

▪MALIK

kai tsaye part din shi ya nufa da ita , sam bai damu da mutanan da ke cikin masarautar ba , ya san kuma su na kallon shi amma bai sauke ta ba
ya na shiga part din shi ya wuce kai tsaye floor na hudu da ita

su na shigowa parlourn ya sauke ta saman kafafun ta
ya na sauke ta ko ta yi sauri za ta bar wajen
taku daya ta yi ya damko kugun ta ya juyo ta su na fuskantar juna ya ce mata " ina kuma za ki je ? "

" Ka sake ni wanka zan je na yi " ta fada ta na matse gera
sai da ya karewa face din ta kallo da kyau sannan ya sake ta a hankali ba tare da ya ce mata komai ba
da sauri ta juya ta fara takawa ta shige corridor ta nufi bedroom din su
sai da ya ga ta shiga cikin corridor din sannan shi ba ya tako a hankali ya bi bayan ta ya shiga bedroom din su

ko da ya shiga kai tsaye Dressing room ya wuce ,
jim kadan ya fito hannun shi rike da wata yar karamar box Red color ya karaso bakin gado ya ajiye ta
sannan ya juya ya nufi toilet , a bakin kofar ya tsaya ya kai hannu ya yi mata knocking
bai jira amsar ta ba ya ce " Ga kaya nan na fido miki saman gado " ya na gama fadar haka ya juya ya fice bedroom din

sai da ta dauki wajen good 45 minutes kafin ta fito da ga cikin toilet ta na daure da towel a kirjin ta

kai tsaye gadon ta nufa har ta kai hannu za ta dauki box din ya ajiye
ta jiyo Muryar shi ya na sallama a bayan ta
slowly ta dago ta juya ta amsa mishi sallamar shi ta na murmushi

a hankali ya ke takowa cikin dakin ya na sanye da kayan barcin shi farare kal , sai tashin qamshi ya ke
gaban ta ya karaso ya tsaya ya sa hannayan shi cikin aljihun wandon shi ya ce mata " Sai yanzu ki ka yi Niyyar fitowa "

wani cool murmushi ta saki kafin ta matso kussan shi ta zagayo da hannayan ta a bayan shi ta kontar da kan ta saman chest din shi
a hankali ya sauke ajiyar zuciya har sai da ya lumshe idanun shi
wata yar karamar dariya ta yi kafin ta ce " ni ma na yi kewar ka sosai "

da sauri ya bude idanun shi ya sunkuyo ya kontar da kan shi saman shoulder din ta ya ce " ta ya ki ka San na yi kewar ki ? "

" Ummm na ji a jiki na " ta fada ta na lumshe idanun ta

a hankali ya kai lips din shi ya manna mata kiss saman shoulder sannan ya yi mata saman wuya
yar karamar dariya ta yi ta na neman ta janye jikin ta da ga nashi

da sauri ya fido hannayan shi , ya zagayo da su a kugun ta ya matse ta tsam a jikin shi
" baby sake ni na saka kayana , na fara jin sanyin " ta fada mishi cikin sanyin murya

a kunne ya rada mata " don't worry I'm here I'll warm you up " ya na gama fadar haka ya sa hannu ya ja towel din jikin ta da karfi ya fadi kassa
a hankali ya sa hannu ya daga ta cak ya karaso wajen gadon ya kontar ta ita , sannan ya mike ya cire kayan jikin shi ya bar short sannan ya Haye saman gadon ya mata runfa da fafadar kirjin shi

AL'AMARIN MALIK SAI INAYA , NI DAI NA KOMA DA GA GEFE HAR SU KAMALLA

▪WASHE GARI ( PRISON )

▪MALIK

Zaune ya ke a cikin Cell din Hakim saman gadon shi , ya daura laptop saman cinyoyin shi ya juyawa Hakim ita ya na kallo

sai da ya share wajen ten minutes kafin Hakim ya yi sauri ya ce " Ga ta nan , ita ce , a ranar da mu ka shigo kassar Turkey "

da sauri Malik ya juyo da laptop din gaban shi , ya na kallon Hall din Airport din , cike ta ke da mutane amma ya iya gano Hakim , ya na tare da wata budurwa da a shekaru ba za ta wuce 20 years ba ta na sanye da Abaya blue color ta yafa veil din ta a kai

slowly Malik ya dago kai ya kali hakim ya ce " ka tabbata two weeks ku ka yi a Turkey ? "

da sauri hakim ya ce mishi " i'm sure "

" yanzu babu wata hanya yadda za ka iya tantance wanda ya saka wannan aikin ? "

" ranka shi dade da na sani da tun da ga farko na fada maka duk lokacin da mu ke haduwa fuskar shi a rufe ta ke " ya fada kamar zai yi kuka

gyada kan shi Malik ya yi kafin ya mike ya ce mishi " Shikenan zan dawo gare ka , an jima " ya na gama fadar haka ya fara takawa ya nufi hanyar fita cell din

har ya kai bakin kofar Hakim ya yi sauri ya ce mishi " ranka shi dade , Muryar shi ina iya gane Muryar shi "

slowly Malik ya juyo ya ce mishi " Za ka iya gane Muryar shi ka tabbata "

gyada mishi kai Hakim ya yi kafin ya ce " na tabbata ranka shi dade , sannan akwai wani bracelet da na taba gani a cikin hannun shi , Bracelet din kamar dai Zanen da ke saman wuyan ka kuma na Gold ne sau biyu ina ganin shi sanye da bracelet din nan "

dan jinkirtawa Malik ya yi kafin ya ce " Shikenan " a takaice sannan ya juya ya fice cell din

kai tsaye Prison din ya baro , ya na fitowa sai saman motocin shi da Diya tsaye a gaban su

ya na isowa Diya ya bude mishi gidan baya ya shiga sannan shi ma ya shiga ya rufo kofar , Driver ya tada motar su ka bar wajen

cikin nitsuwa Malik ya ce ma Diya " Mu je Fada "
gyada mishi kai Diya ya yi kafin ya ce ma Driver ya kai su Fada
ba musu Driver ya juya kan motar su ka nufi hanyar Fada

Fadar ko ta na cike a lokacin duk wanda ke cikin fadar ya na a wajen har Rafik da Aymane wannan karan , Sai surutu su ke

cikin Izza Malik ya shigo Fadar ya na sallama cen kassan makoshi yadda shi kadai ya ji abu ne

su na ganin shi su ka yi tsit su ka mike tsatsaye da sauri su na sunkuyar da kai cikin girmamawa
bai bi ta kan su ya wuce kai tsaye wajen kujerar shi , ya zauna Diya ya koma geffen shi ya tsaya
sai da ya zauna sannan dukkan su su ka zauna su na kallon shi

bai bata lokaci ba ya bude laptop din da ke cikin hannun shi , ya kunna sannan sai saman video din nan da ya gwada wa Hakim
a hankali ya juya laptop din yadda kowa na cikin fadar ke iya gani bai Ce musu komai ba

kowa ya yi shiru ya na kallon Laptop din irin kallon nan na karin bayani
kamar ko Malik ya sani sai ya ce " A cikin video din nan za ku ga saurayin da General Abdallah ya kamo wanda ya harbe Malik , sannan za ku ga Wata Mata a tare da shi "
ya na gama fadar haka ya kashe laptop din ya rufe ta

cikin rudu Hussein ya ce " amma ranka shi dade , me ya kawo zancen wannan videon "

dan jinkirtawa Malik ya yi cikin nitsuwa ya ce " wannan Videon ta na daya da ga cikin abun da zai tabbatar da gaskiyar saurayin nan "

da sauri Mohammed ya mike ya ce " wace gaskiya kuma ran ka shi dade , General Abdallah kai da kan ka , ka kawo saurayin nan ka ce shi ya kashe Malik ko dai batan kai ku ka yi ? "

cikin nitsuwa General Abdallah ya ce mishi " Please Sarkin bayi ka zauna ka ji abun da zai fada "

bai gama rufe bakin shi ba Mohammed ya ce " ka yi hakuri General amma ba zan iya yin shiru ba , yaron nan shi ya kashe Malik me a ke jira har yanzu ba a yanke mishi hukuncin ba , Ku sa baki Jama'a "

ya na gama fadar haka kowane ya shiga fadin Albarkacin bakin shi wasu na cewa a kara bincike wasu kuma su ka goyi bayan Mohammed na cewa a yanke mishi hukuncin yanzu ba sai an jima ba

shi dai Malik shiru ya yi ya lumshe idanun shi ya na sauraron su
cikin bacin rai ya bude idanun shi ya ce " Silence !! " ya fada da karfi duk sai da su ka razana ba shiri kowane ya ja bakin shi ya yi shiru ba

a hankali ya dago kai ya kali Diya
da sauri Diya ya sunkuyo da kan shi ya na sauraron abun da Malik ya rada mishi
Chapter 1 · 0% Book details