Sashe 19
Ba Ni Da Laifi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Motan Aaryan na hango tana matsowa har yayi parking ya fito, ya rame ya koma wani iri, kallo daya za'ayi mashi a gane yana cikin damuwa sosai, kallon Mahmud nayi sai kuma nayi taking steps zuwa inda Aaryan yake, kamar zaiyi kuka yace,
"Baby kiyi hakuri ina cikin damuwa, ke kadai nike son gani shiyasa nazo amma idan baki so bazan k'ara zuwa ba...".
Da sauri na girgiza kai, yace,
"Na gode...".
Sai kuma yayi shiru yana kallona, ji nayi an kwasheni da mari, Yaa Ahmad ne, ya k'ara kwasheni da mari sannan ya nuna min kofa, da gudu na wuce gida ina kuka....
*ba ni da laifi*
*Mariam, Mahmud and Aaryan love saga*
*By sl rimi family's*
*one love*
*BA NI DA LAIFI*
*By sl rimi family's*
*Update Of June, 2019*
In dedicated to our lovely sis late mariam sl rimi, we are still missing you, may your gentle soul rest in peace, Aallah ya jiqanki, Aallah ya gafarta maki, Aameen
*Eid mubarak our greatest Deena babie, Aallah ya albarkaci rayuwarki, wish you all the best....*
*Hope kinyi sallah lafiya Fateema, our greatest small cute hajja, wish you all the best....*
Page. 17
Ban san abun da ya faru ba, lokacin da Yaa Ahmad ya shigo ya tusani gaba kamar zai dokeni, ya hau ni da fad'a ta inda ya shiga bata nan yake fita ba, nayi shiru, saida ya k'ara kwasheni da mari saboda yana magana nayi mashi shiru, na fashe da kuka, yace,
"Indai taurin kai zaki nuna min, tou kadan kika gani, na rabaki da wancen saurayin amma kinki ko, tou zakiji a jikinki ne".
Sai kuma yayi min wani kallo kamar zaiyi kwollo da ni, yayi kwafa ya fice, Ummy tana daga gefe amma bata ce komai ba, sai ma ta mik'e ta wuce dakinta, na mik'e na dauki buta na wanke fuskata sannan na wuce daki na zauna ina shafa fuskata ina feeling yadda fingers dinshi suka kwanta, indai akan Aaryan ne saidai a kasheni, ta dalilina yake cikin damuwa, sam bashi da laifi, saboda ni bazan bari ya rasa ranshi ba....
Washe gari bayan na dawo daga school na tadda sister din Abbanmu tazo, Inna safiya, nasan halinta bata san raini ko kadan, wanka nayi sannan naci abinci, ita da Yaa Ahmad suka tusani gaba suna min fad'a, nidai shiru nayi ina sauraronsu, Yaa Ahmad yace,
"Inna kin ganta nan ta rainani na rabata da wannan saurayin amma taki daina kulashi...".
Inna tace, "Ahhh tou wa ya sani ko asiri yayi mata".
Yaa Ahmad yace, "Babu asirin da yayi mata, taurin kaine kawai da raina mutane da tayi, bata jin maganar kowa sai tashi...".
Inna tace, "Wannan wani irin ja'irin yaro ne yake zuwa yana hure mata kunne, idona idonshi sai naci mashi mutunci".
Yaa Ahmad yace, "Kuma yasan an saka mata biki amma bai fasa zuwa ba itama bata fasa fita ba, idan yazo inyi duka inyi fad'a amma saboda taurin taki daina kulashi...".
Inna tace, "Ai duk laifinku ne kuka zuba mata idanu tana abun da ranta yake so, a fili kuke nuna kun fi sonta, k'anwarta tayi aure amma ita tana zaune wai boko...".
Sai kuma tayi min dak'uwa tace,
"Keh Maryamu uwaki, nace uwarki, k'anin nawa yayi maki miji shine kikeyi mashi haka, wato so kike shi daya da ya rage min ki karasa min dashi, tou kinyi kadan, kaji ja'ira mai manyan kunnuwa...".
Yaa Ahmad yace,
"Mahmud ba ya da damuwa, kowa yabon halinshi yake amma ita a fili take nuna bata sonshi, zai tako yazo zance wurinta amma wancen saurayin yana zuwa zata tsallakeshi ta wuce wurinshi...".
Inna tace, "Lallai Maryamu kin giga...".
Wayata dake kuguna ce ta soma tsuwwa na zura hannu na jawota tareda kangawa a kunne, daga daya bangaren Aaryan yace,
"Mariam kiyi hakuri...".
Nace, "Aaryan ya aka yi?".
Da damuwa yace,
"Ina kofar gidanku yanzu haka...".
Nace, "Kadda ka damu Aaryan...
Alright then gani nan fitowa...".
Da mamaki suke kallona, na mik'e tareda zura long hijab na tsallakesu na fita waje tareda zura takalma na fice, Aaryan ne jingine da motarsa, suit ne sanye a jikinsa da alama daga wurin aiki yake, tausayinshi naji saboda yadda ya koma wani iri, na karasa tareda tsayawa gefenshi, da damuwa ya dubeni yace,
"Mariam kiyi hakuri daga wurin aiki nike ina son komawa gida amma ban ci komai ba, bana san su fahimci halin da nike ciki, baby ke kadai ce zaki iya tursasani inci abinci, baby koda ni kaina bazan iya tursasa kaina ba".
Before inyi uttering word naji saukar mari a kuncina wanda ya gigitani na fashe da kuka, Yaa Ahmad ne, ya nuna min kofa yace,
"Wuce....".
Na wuce da gudu na shige gida karo naci da Inna tana fitowa, na shige ciki da gudu na zube a kasa ina kuka, shigowa sukayi....
Yaa Ahmad ya kwasheni da mari sannan yace,
"Don kin raina mu shine muna maki fad'a kika tsallakemu kika wuce wajenshi wato ga kanin Abba yazo kadda kik'i zuwa ya tsine maki albarka...".
Inna dake tsaye gefe tana maida lumfashi, da alama ranta ya b'aci sosai, a fusace ta tureshi tace,
"Matsa ka bani wuri, wannan shine duka, ai wannan ba duka bane, miye a hannunta?".
Da sauri Yaa Ahmad ya kalli expensive android dake hannuna yace,
"Gidan uban wa kika sameta?".
Nayi shiru, yace,
"Tambayarki nike...".
Inna tace, "Bakya ji yana maki magana".
Yace, "Inna wannan wayar tana da tsada sosai da sosai, ta linka wayata kudi sau goma ko ma fiye da haka".
Inna tasa salati tana sallallami, yace,
"Koda bata fad'a nasan wancen saurayin ne ya bata ita".
A fusace Inna ta mik'o min hannu tace,
"Kawota nan...".
Da sauri yace,
"Tunda ta amsa kibar mata, ai ta rainamu ne, duk gidan nan babu wanda yasan da wayar nan...".
Na lura da wani abu, yasan idan ta amshi wayar daddak'ata zatayi shiyasa yace mata haka, tayi mashi wani kallo tace,
"Tou ai shikenan amma yau sai na cire mata wannan taurin kan da takeji dashi".
Sannan ta jani dakin Abba ta kulleshi tayi min dukan tsiya, kuka kawai nike, naji jiki, na had'a majina, ta bud'e dakin ta fito tana bala'i ta barni kwance ina kuka, ta dage tana bala'i wata maganar kai tsaye da Ummy take, tace,
"Ai rashin mutunci ne ya hanata magana, ita da d'iyarta uwayen son abun duniya, tou daga ke har ita kunyi kadan, aikin banza, aikin wofi...".
Dama bata shiri da Ummy duk da kuwa kyautatawa da take masu, gani suke ta mallake Abba ta hanashi aure, komai ya samu ita da yaranta, surutu sosai sukayi akan fitar da Ayan karatu kasar waje, Ummy dai tana jinta amma bata ce komai ba, na fito na rarrafa na shige dakina, na jima sannan na fito na jawo ruwa na hada da na zafi na shiga bayi na gasa jiki don na daku iya dakuwa, na bugu iya buguwa, na fito tareda shigewa daki na dauko wayata na dannawa Aaryan call yana picking nace,
"Kana ina?".
Daga daya bangaren Aaryan yace,
"Na kasa tafiya, ina akan titin unguwarku, mariam yunwa nikeji sosai".
Nace, "Yanzu zan fito, kadda ka tafi, kaji".
Daga daya bangaren yace,
"Tou baby...".
Tausayi ya bani na mik'e na zura hijab tareda shiga kitchen na dauki kwanon tuwona na zuba mashi miya na fice, ina karasawa bakin titi na hango motarshi na karasa, Yaa Ahmad na hango daga gefe, da sauri na shige tareda rufo motan, Aaryan da ya d'aura kanshi akan starry ya dago yana kallona, da sauri nace,
"Kaga ja motar daga unguwar nan".
Babu musu yayi mata key ya hau titi saida yayi tafiya sosai sannan nace,
"Ka tsaya nan....".
Babu musu ya gangara gefen titi yayi parking, na bud'e kwanon tareda daukar cokali nace,
"Ka daina zama da yunwa kaji".
Aaryan ya gyad'a kai kawai, na ciko spoon da tuwo nasa miya sannan na nufi bakinsa dashi, babu musu ya bud'e baki na saka mashi, ina feeding dinshi yana kallona, saida na tabbatar ya koshi sannan na rufe kwanon nace,
"Akwai ruwa a motarnan?".
Ya girgiza kai, nace,
"Then kawo kudi in siya maka".
Ya zaro wallet dinsa daga pocket din trouser ya mik'o min na zari naira dubu na fita tareda tsallake titi na shiga wani canteen na siya mashi ruwan rubber, lokacin gab ake da fara kiran sallar magrib shiyasa suke sauri-sauri su rufe canteen, na amshi change na tsallako na bud'e motar na shiga na dauki wallet din na saka mashi changing kudin sannan na mik'a mashi ya saka a pocket din wandonsa, na mik'a mashi gorar ruwan nace,
"Ka kuskure bakinka...".
Babu musu ya amsa ya b'alle murfin motar ya fita ya kuskure bakinsa sannan ya shigo tareda mik'o min gorar ruwan na amsa na b'alle murfin tareda kafa mashi ruwan a baki yasha ya koshi har saida ya ture gorar ruwan sannan na maida murfin na ajiyeta na dubeshi nace,
"Ka maidani gida, lokacin sallar magrib gab yake...".
Aaryan ya gyad'a kai sannan a hankali yace,
"Mariam kiyi hakuri bana jin dadin dukan da yake maki saidai babu yadda zanyi brother dinki ne...".
Sai kuma ya ja motan, yayi parking motan a daidai santar gidanmu kallonshi nayi sannan na juya na b'alle murfin motan na fita tareda maida murfin motan na rufe na wuce ina taking steps a sanyaye, tausayi Aaryan yake bani, ina shiga na tarar dashi a tsaye, Yaa Ahmad ne, nayi crossing dinshi zan wuce ya jawoni tareda kwasheni da mari, kwanon dake hannuna ya subuce sauran tuwon da ya rage a ciki ya b'are a kasa, Inna dake gefe ta saki salati tace,
"Ina kikaje da abinci?".
Yace, "Saurayi ta dauki abincinta ta kaimawa".
Inna tace, "Dalla matsa ka bani wuri ko kuma in had'a da kai, ai har da kai aka taru aka zuba mata idanu tana tsula tsiyarta...".
Ya mangareni sannan ya fice, saida Inna ta k'ara likad'a man wani duk'a sannan tayi alwalla ta wuce daki, dakyar na mik'e tareda cire hijab dake jikina na daurata akan igiyar shanya na dauki buta na shiga bayi na fito tareda yin alwalla na wuce daki....
"Baby kiyi hakuri ina cikin damuwa, ke kadai nike son gani shiyasa nazo amma idan baki so bazan k'ara zuwa ba...".
Da sauri na girgiza kai, yace,
"Na gode...".
Sai kuma yayi shiru yana kallona, ji nayi an kwasheni da mari, Yaa Ahmad ne, ya k'ara kwasheni da mari sannan ya nuna min kofa, da gudu na wuce gida ina kuka....
*ba ni da laifi*
*Mariam, Mahmud and Aaryan love saga*
*By sl rimi family's*
*one love*
*BA NI DA LAIFI*
*By sl rimi family's*
*Update Of June, 2019*
In dedicated to our lovely sis late mariam sl rimi, we are still missing you, may your gentle soul rest in peace, Aallah ya jiqanki, Aallah ya gafarta maki, Aameen
*Eid mubarak our greatest Deena babie, Aallah ya albarkaci rayuwarki, wish you all the best....*
*Hope kinyi sallah lafiya Fateema, our greatest small cute hajja, wish you all the best....*
Page. 17
Ban san abun da ya faru ba, lokacin da Yaa Ahmad ya shigo ya tusani gaba kamar zai dokeni, ya hau ni da fad'a ta inda ya shiga bata nan yake fita ba, nayi shiru, saida ya k'ara kwasheni da mari saboda yana magana nayi mashi shiru, na fashe da kuka, yace,
"Indai taurin kai zaki nuna min, tou kadan kika gani, na rabaki da wancen saurayin amma kinki ko, tou zakiji a jikinki ne".
Sai kuma yayi min wani kallo kamar zaiyi kwollo da ni, yayi kwafa ya fice, Ummy tana daga gefe amma bata ce komai ba, sai ma ta mik'e ta wuce dakinta, na mik'e na dauki buta na wanke fuskata sannan na wuce daki na zauna ina shafa fuskata ina feeling yadda fingers dinshi suka kwanta, indai akan Aaryan ne saidai a kasheni, ta dalilina yake cikin damuwa, sam bashi da laifi, saboda ni bazan bari ya rasa ranshi ba....
Washe gari bayan na dawo daga school na tadda sister din Abbanmu tazo, Inna safiya, nasan halinta bata san raini ko kadan, wanka nayi sannan naci abinci, ita da Yaa Ahmad suka tusani gaba suna min fad'a, nidai shiru nayi ina sauraronsu, Yaa Ahmad yace,
"Inna kin ganta nan ta rainani na rabata da wannan saurayin amma taki daina kulashi...".
Inna tace, "Ahhh tou wa ya sani ko asiri yayi mata".
Yaa Ahmad yace, "Babu asirin da yayi mata, taurin kaine kawai da raina mutane da tayi, bata jin maganar kowa sai tashi...".
Inna tace, "Wannan wani irin ja'irin yaro ne yake zuwa yana hure mata kunne, idona idonshi sai naci mashi mutunci".
Yaa Ahmad yace, "Kuma yasan an saka mata biki amma bai fasa zuwa ba itama bata fasa fita ba, idan yazo inyi duka inyi fad'a amma saboda taurin taki daina kulashi...".
Inna tace, "Ai duk laifinku ne kuka zuba mata idanu tana abun da ranta yake so, a fili kuke nuna kun fi sonta, k'anwarta tayi aure amma ita tana zaune wai boko...".
Sai kuma tayi min dak'uwa tace,
"Keh Maryamu uwaki, nace uwarki, k'anin nawa yayi maki miji shine kikeyi mashi haka, wato so kike shi daya da ya rage min ki karasa min dashi, tou kinyi kadan, kaji ja'ira mai manyan kunnuwa...".
Yaa Ahmad yace,
"Mahmud ba ya da damuwa, kowa yabon halinshi yake amma ita a fili take nuna bata sonshi, zai tako yazo zance wurinta amma wancen saurayin yana zuwa zata tsallakeshi ta wuce wurinshi...".
Inna tace, "Lallai Maryamu kin giga...".
Wayata dake kuguna ce ta soma tsuwwa na zura hannu na jawota tareda kangawa a kunne, daga daya bangaren Aaryan yace,
"Mariam kiyi hakuri...".
Nace, "Aaryan ya aka yi?".
Da damuwa yace,
"Ina kofar gidanku yanzu haka...".
Nace, "Kadda ka damu Aaryan...
Alright then gani nan fitowa...".
Da mamaki suke kallona, na mik'e tareda zura long hijab na tsallakesu na fita waje tareda zura takalma na fice, Aaryan ne jingine da motarsa, suit ne sanye a jikinsa da alama daga wurin aiki yake, tausayinshi naji saboda yadda ya koma wani iri, na karasa tareda tsayawa gefenshi, da damuwa ya dubeni yace,
"Mariam kiyi hakuri daga wurin aiki nike ina son komawa gida amma ban ci komai ba, bana san su fahimci halin da nike ciki, baby ke kadai ce zaki iya tursasani inci abinci, baby koda ni kaina bazan iya tursasa kaina ba".
Before inyi uttering word naji saukar mari a kuncina wanda ya gigitani na fashe da kuka, Yaa Ahmad ne, ya nuna min kofa yace,
"Wuce....".
Na wuce da gudu na shige gida karo naci da Inna tana fitowa, na shige ciki da gudu na zube a kasa ina kuka, shigowa sukayi....
Yaa Ahmad ya kwasheni da mari sannan yace,
"Don kin raina mu shine muna maki fad'a kika tsallakemu kika wuce wajenshi wato ga kanin Abba yazo kadda kik'i zuwa ya tsine maki albarka...".
Inna dake tsaye gefe tana maida lumfashi, da alama ranta ya b'aci sosai, a fusace ta tureshi tace,
"Matsa ka bani wuri, wannan shine duka, ai wannan ba duka bane, miye a hannunta?".
Da sauri Yaa Ahmad ya kalli expensive android dake hannuna yace,
"Gidan uban wa kika sameta?".
Nayi shiru, yace,
"Tambayarki nike...".
Inna tace, "Bakya ji yana maki magana".
Yace, "Inna wannan wayar tana da tsada sosai da sosai, ta linka wayata kudi sau goma ko ma fiye da haka".
Inna tasa salati tana sallallami, yace,
"Koda bata fad'a nasan wancen saurayin ne ya bata ita".
A fusace Inna ta mik'o min hannu tace,
"Kawota nan...".
Da sauri yace,
"Tunda ta amsa kibar mata, ai ta rainamu ne, duk gidan nan babu wanda yasan da wayar nan...".
Na lura da wani abu, yasan idan ta amshi wayar daddak'ata zatayi shiyasa yace mata haka, tayi mashi wani kallo tace,
"Tou ai shikenan amma yau sai na cire mata wannan taurin kan da takeji dashi".
Sannan ta jani dakin Abba ta kulleshi tayi min dukan tsiya, kuka kawai nike, naji jiki, na had'a majina, ta bud'e dakin ta fito tana bala'i ta barni kwance ina kuka, ta dage tana bala'i wata maganar kai tsaye da Ummy take, tace,
"Ai rashin mutunci ne ya hanata magana, ita da d'iyarta uwayen son abun duniya, tou daga ke har ita kunyi kadan, aikin banza, aikin wofi...".
Dama bata shiri da Ummy duk da kuwa kyautatawa da take masu, gani suke ta mallake Abba ta hanashi aure, komai ya samu ita da yaranta, surutu sosai sukayi akan fitar da Ayan karatu kasar waje, Ummy dai tana jinta amma bata ce komai ba, na fito na rarrafa na shige dakina, na jima sannan na fito na jawo ruwa na hada da na zafi na shiga bayi na gasa jiki don na daku iya dakuwa, na bugu iya buguwa, na fito tareda shigewa daki na dauko wayata na dannawa Aaryan call yana picking nace,
"Kana ina?".
Daga daya bangaren Aaryan yace,
"Na kasa tafiya, ina akan titin unguwarku, mariam yunwa nikeji sosai".
Nace, "Yanzu zan fito, kadda ka tafi, kaji".
Daga daya bangaren yace,
"Tou baby...".
Tausayi ya bani na mik'e na zura hijab tareda shiga kitchen na dauki kwanon tuwona na zuba mashi miya na fice, ina karasawa bakin titi na hango motarshi na karasa, Yaa Ahmad na hango daga gefe, da sauri na shige tareda rufo motan, Aaryan da ya d'aura kanshi akan starry ya dago yana kallona, da sauri nace,
"Kaga ja motar daga unguwar nan".
Babu musu yayi mata key ya hau titi saida yayi tafiya sosai sannan nace,
"Ka tsaya nan....".
Babu musu ya gangara gefen titi yayi parking, na bud'e kwanon tareda daukar cokali nace,
"Ka daina zama da yunwa kaji".
Aaryan ya gyad'a kai kawai, na ciko spoon da tuwo nasa miya sannan na nufi bakinsa dashi, babu musu ya bud'e baki na saka mashi, ina feeding dinshi yana kallona, saida na tabbatar ya koshi sannan na rufe kwanon nace,
"Akwai ruwa a motarnan?".
Ya girgiza kai, nace,
"Then kawo kudi in siya maka".
Ya zaro wallet dinsa daga pocket din trouser ya mik'o min na zari naira dubu na fita tareda tsallake titi na shiga wani canteen na siya mashi ruwan rubber, lokacin gab ake da fara kiran sallar magrib shiyasa suke sauri-sauri su rufe canteen, na amshi change na tsallako na bud'e motar na shiga na dauki wallet din na saka mashi changing kudin sannan na mik'a mashi ya saka a pocket din wandonsa, na mik'a mashi gorar ruwan nace,
"Ka kuskure bakinka...".
Babu musu ya amsa ya b'alle murfin motar ya fita ya kuskure bakinsa sannan ya shigo tareda mik'o min gorar ruwan na amsa na b'alle murfin tareda kafa mashi ruwan a baki yasha ya koshi har saida ya ture gorar ruwan sannan na maida murfin na ajiyeta na dubeshi nace,
"Ka maidani gida, lokacin sallar magrib gab yake...".
Aaryan ya gyad'a kai sannan a hankali yace,
"Mariam kiyi hakuri bana jin dadin dukan da yake maki saidai babu yadda zanyi brother dinki ne...".
Sai kuma ya ja motan, yayi parking motan a daidai santar gidanmu kallonshi nayi sannan na juya na b'alle murfin motan na fita tareda maida murfin motan na rufe na wuce ina taking steps a sanyaye, tausayi Aaryan yake bani, ina shiga na tarar dashi a tsaye, Yaa Ahmad ne, nayi crossing dinshi zan wuce ya jawoni tareda kwasheni da mari, kwanon dake hannuna ya subuce sauran tuwon da ya rage a ciki ya b'are a kasa, Inna dake gefe ta saki salati tace,
"Ina kikaje da abinci?".
Yace, "Saurayi ta dauki abincinta ta kaimawa".
Inna tace, "Dalla matsa ka bani wuri ko kuma in had'a da kai, ai har da kai aka taru aka zuba mata idanu tana tsula tsiyarta...".
Ya mangareni sannan ya fice, saida Inna ta k'ara likad'a man wani duk'a sannan tayi alwalla ta wuce daki, dakyar na mik'e tareda cire hijab dake jikina na daurata akan igiyar shanya na dauki buta na shiga bayi na fito tareda yin alwalla na wuce daki....