← Book details Alqibla Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 65 OF 69

Sashe 65

Alqibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Murmushi ya saki,sannan ya taso daga inda yake zaune,yaja kujera dab da ita ya zauna har gwiwarsa na gogar tata,hannunsa ya sanya ya dago fuskarta gaba daya,saiya girgiza mata kai alamun
"A'ah"yatsansa guda daya ya sanya ya dinga dauke mata hawayen,murmushi kwance saman fuskarsa,har sai daya goge duk wani hawaye da yayi saura,saiya hada goshinsa da nata suna musayar numfashi,qamshin turarensu na gauraya da juna
"A wancan lokacin kinyi fushi....kin nuna kishi saboda ganina da wata balarabiya.....wadda nake ganinta da muni sosai idan na hada da kyakkyawar fusakarki,da kuma yadda zuciyata ta rayu da sonki......ta samu dukka fara'ata ne da kulawa saboda yabonki da tazomin dashi,ta shaidamin tunda taga shigowarmu taji mun burgeta.....tana son qawance dake,dalilin da yasa ta biyoni kenan har kika ganmu tare....saidai kuma a yanzun gashi kina kuka saboda wata da na taba so na baki labarin mutuwarta...me yasa bakiyi kishin xahra ba?" Ta rasa amsar da zata bashi,amma dole duk me imani yaji a yadda zahra ta rasun ya tabashi,ta riga data wuce zahra ba zata taba dawowa ba,kishi da ita tamkar abun nan da hausawa ke kira da ihu bayan hari ne.

Murmushi ya saka yana cewa
"Na fahimta....amma har yau kinsan ban samu makwafin zahra ba?" Cikin mamaki ta zare fuskarta daga nashi tana duban idanunsa,saiya dage mata dukka girarsa
"Eh....ban sake samun wadda tacemin ALIYYU HAIDAR INA SONKA BA,ban sani ba ko baqinjini gareni?" Dariya sosai ya bata,yanayin yadda yayi maganar ma abun dariya ne,sai tasa hannu ta toshe bakinta,yayin daya harde hannayensa a qirji yana qare mata kallo,dariyarta kadai ta sanyashi farinciki shima,gami da saukar masa da nutsuwa
"Aikam saidai idan har shin haidar din ne baiso a gaya masa ba,a iya sanina akwai daruruwa ko ince dubban mata dake ta dakon randa xai basu dama su furta wannan kalma a gareshi....." Tararta yayi ta hanyar watsa hannayensa,kamar zai saki kuka yace
"Ni dukkansu ban gansu ba,bansan da zamansu ba,zahran hajja kawai na sani,kuma ita kadai nake jira da dakon randa zata gaya min hakan....." Itama bata barshi ya qarashe ba yaji saukar kalaman kamar ruwan sama saman zuciyarsa
"Ya haidar kadai nakeso....shi nake qauna har abada" idanunsa ya ware cikin mamaki yana dubanta
"Say it again please"🙏🏽,duk kunya saita cikata,ta maida kanta wani sashen tana murmushi,sai ganinshi tayi ya koma inda ta maida kan nata
"Please....inason na sake ji" wani qwarin gwiwa ya bata daga cikin idanunshi,saita kalleshi sosai
"Ina son ya haidar,ina sonka...ina sonka" gaba daya ya tattareta cikin jikinsa,ya manta ma suna waje ne,sai data ankarar dashi,ta tabbatar da a 9ja suke da tuni sun tara 'yan kallo,da qyar yayi controlling kansa,ya komqa ya zauna dab da ita,muryarsa cike da wani irin softness ya kamo hannunta ya riqe tsam cikin nasa sannan yace
"Hakan yana nufin....kin mallakamin rayuwarki?,kin zama ni na zama ke?,zakici gaba kuma da kasancewa tawa har abada,munyi amanna wa juna zamu rayu da juna duk rintsi duk kin yarda da wannan?" A kunyace kan irin salon kalaman dake fita daga bakin yayan nata,da salon kallon da yake mata ta gyada masa kai,saiya girgiza kai
"Banison body language.....pls ki gayamin da bakinki"
"Amince.....na amince ya haidar" lightly yayi kissing saman hannunta,ya rasa da wacce kalma zai sake magana,kawai sai yaci gaba da riqon hannunta cikin nashi yana kallon kayarsa kamar za'a qwaceta,har sai da tayi waving hannunta saman fuskarsa
"Bansan me zance miki game dani ba,abu daya zuwa biyu kawai bakina zai iya gaya miki,da kanki zaki dinga bawa kanki amsar irin mijin da kikayi katari dashi,sannan ina miki albishir din cewa......zaki shiga sahun matan da sukafi dukkan mata sa'ar miji a duniya" daga haka ya miqe yana riqe da hannunta,itama saita miqe suka soma takawa cike da wani irin xallar farinciki dake yawo dasu a duniyarsu.

Kwan daya tak suka qara suka fara shirin dawowa,ya bata dama ta siya dukkan abinda take da buqata,siyayya me yawa da batasan me za'ayi dasu ba.

Kamar yadda suka tafi tare haka suka dawo,sun tadda 'yan Tarbarsu danqam suna jiransu,family ne mai cike da hadin kai da qaunar juna,babu wani bambanci da xaka gani tsakaninsu.

Tun a airphort din ta ankare da yadda 'yan gidan nasu keta gulmarta ita da ya zakin,saboda duk inda yayi yana maqale da abarsa,baya jin kunya ko nauyi sam,motsi kadan nata idanunsa da hankalinsa yana kanta.

Da zasu tafin bai bar kowa ya shiga tashi motar ba,zahran ta rasa dalili amma yayi fuska,ta sani dukkansu shakkarsa suke,saboda haka ba wadda ta iya tunkararsa,sai hafsat data rage bata samu waje ba,tayita zagaye tanason tace ya dauketa,amma ta kasa,sai zahran ce ta dubeshi
"Please ya haidar....maman khairat ce bata samu waje ba" ta fada cikin marairaicewa,wani kallo ya watsawa hafsat din ta window,ba shiri ta fara qoqarin juyawa tabar wajen,amma sai zahran ta yaficeta ganin baice komai ba.

Bai tanka musu ba har aka fara tafiya,basuyi nisa da airport din ba ya bawa driver umarnin ya tsaya,saiya fidda kudi tana ajema hafsat din fuska a tsuke
"Sauka ki tari napep ki hau....." Kallonshi duka suyi cikin mamaki,saiya hade rai tsam,zahra ta dubeshi a shagwabe
"Yayaaaaa"
"Shshshshhh...ba gida muka nufa ba,so take muyita yawo da ita?" Mamaki ya kamata,toba gida suka nufa ba ina suka nufa kenan?,tana ji tana gani hafsat din ta sauka ta tari napep su kuma sukaja motarsu suka wuce,sai tayi kicin kicin ita ala dole fushi take dashi,bai tankata ba,data kalli fuskarsa ma sai taga walwalarsa yake abinsa.

Tanata zuba ido tana ganin yadda suka shiga unguwar,mamakin wajen wanda zasuje take,daga dawowarsu daga doguwar tafiya irin wannan.

Bata samu amsar tambayarta ba har sai da suka tsaya qofar gidan,mai gadin madaidaicin gate din ya bude musu suka shige madaidaiciyar harabar gidan da zata iya cin motoci uku zuwa hudu ba tare da sun takura ba,da kansa ya fita,ya zagaya inda take zaune ya bude mata motar,fuskarsa dauke da murmushi yace
"Bismillah" dubansa tayi tana maqale kafada tare d zumbura baki,Ranqwafowa yayi saman kanta yana murmushi
"Beautiful.....wannan bakin naki...." Sai ya saka yatsunsa biyu ya kama labban nata ba tare daya qarasa fadar abinda ke bakinsa ba,janye bakin tayi da sauri saboda yawon daya fara da yatsunsa saman labban nata
"Ranki ya dade.....ina miki barka da shigowa gidan aurenki" ya fada murya can qasa kamar meyin rada,da sauri ta daga ido tana kallonshi
"Ya haidar....kada kayi haka,shi yasa ka hana kowa shiga motar mu....hajja fa" yatsansa ya dora saman lips dinsa yace
"Shshsshhhhh....banason kiran sunan kowa ba,bansan kowa ba sai ke,nan din duniyarmu ce ni dake,kema kuma zaki manta da kowa da komai soon" ba tare data shirya ko ta ankara ba taji gaba daya ya sunkuceta,ta Maqaleshi sosai,saboda ji da take kamar zata fadi
"Karki damu,a hannun soja kike" ya fada yana murmushi,saita maida masa martani itama ta maida kanta qirjinsa ta kwantar,tana jin yadda zuciyarsa ke bugawa da sauri da sauri,sai ta daga kanta cikin mamaki ta dubeshi,murmushi ya sake sakar mata
"My heart beat ko?,kada ki damu,sonki ne da zumudin kasancewa tare dake" wani farinciki taji yana ratsa zuciyarta,tanajin alfahari da kasancewarsa mijinta yana mamaye ruhinta,qaunar hajja ta sake fadada a ranta,tabbas ita din ba qaramar masoyiya bace,me yasa kaf cikin jikoki da 'ya'yan 'yan uwa bata zabi kowa ba sai ita?,ita kadai ta dauka ta mallakawa mutum mai tsada da daraja irin aliyyu?,a hankali a hankali take fuskantar komai,kamar yadda ta taba gaya mata cewa zata gane,zata fahimci gatan datayi mata,bata da bakin gode mata,bata kuma da abinda zatace mata face addu'ar gamawarta da duniya lafiya.

Tana daga hannunsa take qarewa gidan kallo tun daga hanya har shigarsu falo,ba'a cika masa kayan alatu na qarya da barnar kudi ba,amma ya qayatar matuqa ya kuma bada ma'ana,parlour,two bedrooms with toilets a qasa,dining area,kitchen,store da wani toilet din a falo,saman benan gidan ma falo ne da bedroom biyu,kowanne shima da toilet,gaban kowanne daki akwai qawataccen corridor da zai baka damar ganin gaba da bayan gidan,akwai dakuna daga bayan ainihin ginin gidan guda biyu masu falo daya da bandaki,sai wajen ajiye motoci matsakaici ha matsakaiciyar haraba don shan iska.

Dubansa tayi sanda taga yana aje kayansu a dakin daya direta
"Ina nawa bedroom din?" Wani kallo ya mata mai kwantar da zuciyar masoyi,saidai fuskarsa a dan hade take,saiya zare rigar shaddar jikinsa,jinsa yake gaba daya a takure,don bazai iya tuna rabonshi da saka manyan kaya ba,banda wannan tafiyar da hajja ta tubure kan lallai bashi ba saka fingilallu kuma damammun kayan yahudu,bayan garin ma'aiki zashi.

Sai daya qaraso dab da ita ya dagata tsaye yana riqe da qugunta da hannu daya,daya hannun kuma yana warware rolling din doguwar rigar dake kanta
"Banason na raba komai da matata,nafison komai namu mu dinga sharing....bawai saboda babu wadata ko ikon siya ba,a'ah.....inason mu samu kusanci qauna da shaquwa matabbaciya.....irin wadda a tarihin masoya kaf na duniya babu masoyan da suka samu shaquwa da fahimtar juna irin tamu" yakai qarshen zancan sanda yake fidda mata doguwar rigar jikinta,saiya zamana daga ita sai under wear da vest,kaman maye haka ya bita da kallon qurilla,yadan ja baya kadan ta yadda zai samu damar kallonta da kyau,saiya miqa hannunsa i zuwa muhallin dako yaushe yake tsone masa idanu,ya kumayi tafiyar ruwa da nutsuwarsa,gocewa tayi tana dariya,a 'yar tarayyarsu ta qididdigaggun kwanaki,ta gama fuskantar shi din mutum ne da yake qaunarsu,suka kuma matuqar tafiya da hankalinsa,cikin zafin nama ya bita zai cafko yana cewa
"Oh....no,don Allah,kada muyi haka dake pleasessssssss" dai dai nan ya samu nasarar kamotan,ya mannata da jikinsa yana sauke qatuwar ajiyar zuciya,tsayin minti guda kafin yace
"Duk sanda nake tare dake,nakan manta wanene ni....ashe dai da gaske kedin aljannar duniyata ce,don Allah....ki rayu dani,mu mutu tare" martani ta maida masa ta hanyar rungumeshi tsam itama,yadda takeji cikin zuciyarta bazai misaltu ba,a hankali take rada masa wasu kalamai cikin kunnuwansa,kalaman da suka sake rura wutar dake ruruwa cikin zuciyarsa,suka kuma sanya ya daina gane komai,cikin qaramin lokaci suka qwace dukka hankali da nutsuwarsa,wanda hankalin da nutsuwar basu dawo masa ba,har sai data kaishi wata duniya ta daban,duniyar da kullum yake bege da muradin tabbata a cikinta matuqar da zahran ne.
Chapter 65 · 0% Book details