Sashe 10
Alqibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da kallo hajja ta bisu sanda suke fitowa daga dakin suna 'yar hayaniyarsu,har sunyi gaba hafsat tadan dawo da baya
"Don Allah koda ya haidar zai tambaya ina ina kice kece kika aikemu" baki ta tabe tana dubansu
"Babu ruwan fadimatu zahra'u,ku qarke qalau"
"Hajja mu dake fa bata baci" ta fada tana dariya tayi gaba suka fice.
Kusan awa biyu suka kwashe,har kusan bayan isha'i sannan suka fito,suna tafe suna hirarsu har suka qaraso qofar gidan.
Salma ce a gaba,ita ta fara tura qofar gidan,da sauri ta dawo da baya har tana bige yasira
"Dalla meye haka...kefa kin fiya abun haushi wani lokaci"
"Ya haidar.....wallahi ya dawo,suna baranda shida dasu ya abu sufyan" sak kowaccensu tayi,aka koma kallon kallo tsakaninsu,aka rasa me magana har tsahon wasu sakanni.
Zahra ce ta soma jan tsaki,sannan ta soma yin gaba tana jan hannun hafsat
"Tsoron wai na meye,muje don Allah,fuska kawai xamu masa" qarfafa musu gwiwan da tayi yasa suka soma takawa zuwa ciki.
Zaratan samari ne guda hudu saman wasu fararen kujerun roba,aliyyu na biyar dinsu,dan qaramin teburi ne a gabansu dauke da lemuka da cups,sai dan qayataccen qaramin flask din tea da kofunansa.
Kana dubansu xaka gane akwai abinda suke tattaunawa,saidai aliyyun kacokam hankalinsa nakan wayarsa kamar kullum,lokaci lokaci yana dan sanya bakinsa ba tare daya daga kanshi daga wayar ba,hakan yasa sukaji dadi,sannu a hankali suka fara takawa zasu wuce zuwa sashen da yafi kusa dasu.
Kaman an umarceshi ya daga kansa,idanu biyu sukayi dasu,take kowacce tasha jinin jikinta,yayin da zahra ta fara qoqarin boyewa sosai ta bayansu yadda bazai iya ganinta ba.
Sunan hafsa ya kira,ta amsa kana cikin hanzari ta nufi inda yake,bata wuce sakan biyar ba ta dawo
"Ya haidar yace kuzo" ta fada tana narai narai da ido muryarta na rawa,tilas suka taka zuwa inda suke zaunan,suna hangoshi daga inda suke yana ci gaba da danna wayarsa,yayin da sauran abokan nasa suka dakata da maganar da sukeyi din,wasunsu suka dauki drink suna sha,wasu kuma suka tsiyaya black tea.
"A'ah,yammata.....daga ina haka?" Daya daga cikin abokan nashi mai suna saif ya fada cikin sakin fuska,kasa amsa masa sukayi,sai suka maye gurbin tambayar tashi da gaisuwa cikin sanyin murya dake nuna tsoro,ba wadda ta isa tayi gigin yin wani abun da bai dai dai ba,don dukkansu sun haddace dokokinsa da abinda bai dauka,suna girmama abokanshi sosai kamar yadda suke bashi girma,saidai akwai dan bambanci,kusan sunfi sakewa dasu fiye dashi,don a cikinsu akwai masu sakin fuska ba kamar shi ba.
Shanyasu yayi suka ci gaba da hirarsu,wanda mafi akasari abinda ya shafi aikinsu ne na soja,a qalla sun kusa awa guda a duqe qafafunsu har soma tsami,sai da daya daga cikin abokan nashi qasa qasa yace
"Man,ka ajjiye mutane fa,ka sallamesu idan baka da abun cewa" tsaki yaja yana gyara zamanshi,ya sauke qafarsa da tun dazun daya ke saman daya ya zauna sosai kamar wani saraki sannan ya jefa musu tambayar daga ina suke,cikin rawar murya hafsa tace
"Hajja ce ta aikemu nan baya...."
"Kunci sa'a ta gayamin,amma daga yauu....kada ku sake na sake ganinku kamar i yanzu a waje....ku bacemin a gun" da sauri dukkansu suka miqe,hakan ya sanya ta manta da cewa boye masa take ta miqe itama da sauri.
"Ke!...zonan" ya fada da wani dakakken sauti daya sanya cikinta bada wani sauti na quuuu,ko ba'a fada ba da ita yake babu neman qarin bayani
"Ba daku nake ba.....ku bace daga nan kafin na tashi" ya baiwa sauran umarni,hakanan tana ji tana gani suka wuce suka barta.
A hankali take takowa zuwa inda suke kamar kazar da qwai ya fashewa a ciki,duk yadda taso baiwa kanta qwarin gwiwa amma ta kasa tattaroshi,batayi tunanin zai ganta ba sam
"Kina cikinsu dama zahran hajja?" Daya daga cikin abokan nasa mai suna fahad wanda sai yanzu yayi magana ya furta,wani kallo aliyyun ya watsa mishi kafin ya maida dubansa a kanta yana jifanta da wani kallo yace
"A ina nace miki yau ki kwana?" Shuru kamar ba zata amsa ba sannan tace
"Makaranta"
"Da kyau!,me kike a gida yau din?"
"Babu komai"
Kanshi ya gyada shuru na wasu 'yan mintuna,sannan ya zira hannunshi a aljihu ya ciro key din mota ya wurga mata
"Ki cewa labaran ya kunna miki ruwa ya baki mesa" muqullin tabi da kallo tana maimaita abinda ya fada cikin qwaqwalwarta.
Ta fahimci abinda yake nufi tsaf,wato taje ta wanke mishi mota kenan koko yaya?,so yake ya disgata gaban abokanshi,data sake daga kai ta kalleshi ya maida qafafunsa yadda suke yaci gaba da sabgarsa.
Tsam ta miqe riqe da muqullin ta juya ta soma takawa
"Fahad.....kana so ka jawa mutane raini wajen yaran nan,na gaya maka tun ba yanzu ba banaso ko?" Ta jiyoshi yana fada cikin miskilanci,sai taja qaramin tsaki tana tunanin aikin daya sanyata yanzun,kuma tabbas yana hangota indai motarshi da take hangowa muqullinta ne a hannunsa,bama shi ba har duka abokan nashi suna iya ganota.....
_kuyimin afuwa jina shuru kwana biyu,hidima ce ta biki ta riqeni,naso muku bayani amma hakan bai samu ba,Allah yayi mana jagora_8
*KU MATSO MAZA KUJI LABARIN*
*_Oumahmad collection's_*
*_Shin kina buqatar waje daya tattare dukkan abubuwan buqata da kike son saye ba bata lokaci ko rarraba waje?_*
*to ga OUMAHMAD COLLECTIONS*
*_wadanda ke saida_*
_kayan kitchen_
_kayan sawa nau'i daban daban_
_jakankuna da takalma 'yan ubansu_
_wayoyin hannu kala daban daban na zamani_
_mayafai na gani na fada_
_kayan sawar yara na alfarma_
_kayan daki daga qasashe daban daban,irinsu dubai,china,India,turkey,Malaysia_
_ADRESS DINSU_👇🏽👇🏽
*_Kano hotoro_*
*Ko ku dubasu a facebook da sunan*
*_Maryam muhd_*
*Ko kira kai tsaye ta lambar waya kamar haka*
07014488636
*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽
__________________________________
*KIJI TSORON ALLAH☝🏾☝🏾☝🏾,KARKI TABA ABINDA BA NAKI BA,BA KUMA MALLAKINKI BANE*❗❗❗
Kamar yadda yace bata fasa ba ta isa wajen labaran din,ta kuma buqaci ya hada mata famfon kamar yadda aka saba idan za'a wankewa wani cikin gidan mota,sai daya gama ta kalleshi
"Ance ka bani klien"
"Ah'ah....ai indai motar yallabai Aliyyu za'a wanke yana da carwash dinsa da ake wanke masa dashi,bari na dauko miki" har ya juya zai tafi ta dakatar dashi da sauri tana cewa
"Klien yace a bani,shi zaka daukomin" jimm yayi kadan sannan ya gyada kanshi yayi gaba,babu jimawa ya dawo dashi ya miqa mata,ta bishi da kallo har sai da taga bacewarsa sannan ta taka zuwa wajen mai musu aike aike cikin gidan,wanda wani lokaci yakan zauna a gidan na wasu kwanaki idan yana da ayyuka da yawa har zuwa sanda zai ragesu kana ya tafi gidansu
"Soson qarfe nakeson ka bani aro don Allah hayatu" ta fada tana dan waigawa taga yana ganinta?.
Ba tare da tunanin komai ba ya shiga ciki ya dauko ya miqa matan,ta karba tana jin dadin samun soson sannan ta durfafi motar tana qwafa,gami da qiyasta irin barnar da zatayi masa,yau saita fanshe dukka haushinta akan motar,koma me zai faru ya faru.
Sosai ta zambada klien cikin wani ruwa dake cikin botiki,saboda taji ance ba'a wanke mota da klien,don tana kodar da fentinta,to ba motar ba,shi kansa me motar da zata iya saita kodar dashi,taga kya da gayun da yakewa taqama,kamar wani yafi kyau,itakam ta tsani yadda mata ke kodashi,tana ganin kamar suke tunzurashi ma suke yake sake jin kansa wani,kofi ta ciko ta miqe da niyyar soma watsawa motar
"Zahra'u" taji an ambata sunanta daga bayanta,saita waiwaya,abba babba ne,riqe da maqullin mota da leda a hannunsa
"Na'am abba?....sannu da zuwa" kai ya gyada
"Yauwa....me zakiyi da ruwa kika tarashi haka kamar zakiyi wankin mota" saita marairaice sosai,ta sani cewa mafita tazo,duk da tana son taga ta bata wannan 'yar kyakkyawar motar taga ta tsiya,duk da ta sani ba abune mai sauqi ba,hakan zai iya janyo mata tsatstsauran hukunci daga wajensa,amma ita duk ba damuwarta bane wannan
"Ya Aliyyu ne ya sakani wankin motar" ta fada tana wani sunkui da kai
"Haidar dai?" Ya tambaya cikin mamaki,saiya gyada kai kanta a qasa
"Wannan wanne irin shirmen banza da wofi ne......mace da wankin mota?,ina shi haidar din?" Saita nuna mishi inda suke zaune shi dasu abu sufyan,duk da yanzun shi ya miqe tsaye ya basu baya yana amsa waya,murya ya daga ya kirayi sunanshi,dukkansu hankalinsu ya dawo wajen,sai suka miqe gaba dayansu suka nufo abban.
Cikin girmamawa suka gaidashi sannan suka koma suka barshi da aliyyun,juyawa yayi inda zahra ke tsaye ta baza kunnuwa taji ya zata kaya,ya miqa mata ledar hannunsa
"Qarasamin da ita wajen hajja" hannu biyu tasa ta karba sannan ta juya zuwa sassan hajjan,taso ace a gabanta abban zai masa fadan taga ya zaiyi,amma ko hakan ma ai tasha dashi,tunda ba haka yaso ba.
Dukka suna sassan hajjan kowacce tayi tsuru tsuru,tana ajjiye ledar suna cikata da tambayar yata kaya tsakaninsu,sunga ta dawo da wuri,sai data samu waje ta zauna sannan ta gaya musu yadda akayi,dariya harda masu saukowa daga saman kujerar
"Gaskiya na yadda ya haidar qarshe ne" yasira dake qyaqyata tata dariyar ta fada,cikin dariyar salma ma tace
"Lallai kice ya samu babbar mawankiyar mota,ai kawai a soma biyanki cikin gidan nan an huta biyan su labaran,to wallahi Allah ya qwaceki abba ya qwaceki,don da kin sake kin masa wankin mota da sosan qarfe kashinki ya bushe a gidannan,ke kinsan kudin wannan motar kuwa?" Kafada ta daga cikin rashin damuwa
"Oho,koma nawa ce ai shi ya janyo,haka kawai gaban abokan nan nashi masu shegen ji da kansu da isa saiya yarfani saboda ya raina mana ajawali".
"Don Allah koda ya haidar zai tambaya ina ina kice kece kika aikemu" baki ta tabe tana dubansu
"Babu ruwan fadimatu zahra'u,ku qarke qalau"
"Hajja mu dake fa bata baci" ta fada tana dariya tayi gaba suka fice.
Kusan awa biyu suka kwashe,har kusan bayan isha'i sannan suka fito,suna tafe suna hirarsu har suka qaraso qofar gidan.
Salma ce a gaba,ita ta fara tura qofar gidan,da sauri ta dawo da baya har tana bige yasira
"Dalla meye haka...kefa kin fiya abun haushi wani lokaci"
"Ya haidar.....wallahi ya dawo,suna baranda shida dasu ya abu sufyan" sak kowaccensu tayi,aka koma kallon kallo tsakaninsu,aka rasa me magana har tsahon wasu sakanni.
Zahra ce ta soma jan tsaki,sannan ta soma yin gaba tana jan hannun hafsat
"Tsoron wai na meye,muje don Allah,fuska kawai xamu masa" qarfafa musu gwiwan da tayi yasa suka soma takawa zuwa ciki.
Zaratan samari ne guda hudu saman wasu fararen kujerun roba,aliyyu na biyar dinsu,dan qaramin teburi ne a gabansu dauke da lemuka da cups,sai dan qayataccen qaramin flask din tea da kofunansa.
Kana dubansu xaka gane akwai abinda suke tattaunawa,saidai aliyyun kacokam hankalinsa nakan wayarsa kamar kullum,lokaci lokaci yana dan sanya bakinsa ba tare daya daga kanshi daga wayar ba,hakan yasa sukaji dadi,sannu a hankali suka fara takawa zasu wuce zuwa sashen da yafi kusa dasu.
Kaman an umarceshi ya daga kansa,idanu biyu sukayi dasu,take kowacce tasha jinin jikinta,yayin da zahra ta fara qoqarin boyewa sosai ta bayansu yadda bazai iya ganinta ba.
Sunan hafsa ya kira,ta amsa kana cikin hanzari ta nufi inda yake,bata wuce sakan biyar ba ta dawo
"Ya haidar yace kuzo" ta fada tana narai narai da ido muryarta na rawa,tilas suka taka zuwa inda suke zaunan,suna hangoshi daga inda suke yana ci gaba da danna wayarsa,yayin da sauran abokan nasa suka dakata da maganar da sukeyi din,wasunsu suka dauki drink suna sha,wasu kuma suka tsiyaya black tea.
"A'ah,yammata.....daga ina haka?" Daya daga cikin abokan nashi mai suna saif ya fada cikin sakin fuska,kasa amsa masa sukayi,sai suka maye gurbin tambayar tashi da gaisuwa cikin sanyin murya dake nuna tsoro,ba wadda ta isa tayi gigin yin wani abun da bai dai dai ba,don dukkansu sun haddace dokokinsa da abinda bai dauka,suna girmama abokanshi sosai kamar yadda suke bashi girma,saidai akwai dan bambanci,kusan sunfi sakewa dasu fiye dashi,don a cikinsu akwai masu sakin fuska ba kamar shi ba.
Shanyasu yayi suka ci gaba da hirarsu,wanda mafi akasari abinda ya shafi aikinsu ne na soja,a qalla sun kusa awa guda a duqe qafafunsu har soma tsami,sai da daya daga cikin abokan nashi qasa qasa yace
"Man,ka ajjiye mutane fa,ka sallamesu idan baka da abun cewa" tsaki yaja yana gyara zamanshi,ya sauke qafarsa da tun dazun daya ke saman daya ya zauna sosai kamar wani saraki sannan ya jefa musu tambayar daga ina suke,cikin rawar murya hafsa tace
"Hajja ce ta aikemu nan baya...."
"Kunci sa'a ta gayamin,amma daga yauu....kada ku sake na sake ganinku kamar i yanzu a waje....ku bacemin a gun" da sauri dukkansu suka miqe,hakan ya sanya ta manta da cewa boye masa take ta miqe itama da sauri.
"Ke!...zonan" ya fada da wani dakakken sauti daya sanya cikinta bada wani sauti na quuuu,ko ba'a fada ba da ita yake babu neman qarin bayani
"Ba daku nake ba.....ku bace daga nan kafin na tashi" ya baiwa sauran umarni,hakanan tana ji tana gani suka wuce suka barta.
A hankali take takowa zuwa inda suke kamar kazar da qwai ya fashewa a ciki,duk yadda taso baiwa kanta qwarin gwiwa amma ta kasa tattaroshi,batayi tunanin zai ganta ba sam
"Kina cikinsu dama zahran hajja?" Daya daga cikin abokan nasa mai suna fahad wanda sai yanzu yayi magana ya furta,wani kallo aliyyun ya watsa mishi kafin ya maida dubansa a kanta yana jifanta da wani kallo yace
"A ina nace miki yau ki kwana?" Shuru kamar ba zata amsa ba sannan tace
"Makaranta"
"Da kyau!,me kike a gida yau din?"
"Babu komai"
Kanshi ya gyada shuru na wasu 'yan mintuna,sannan ya zira hannunshi a aljihu ya ciro key din mota ya wurga mata
"Ki cewa labaran ya kunna miki ruwa ya baki mesa" muqullin tabi da kallo tana maimaita abinda ya fada cikin qwaqwalwarta.
Ta fahimci abinda yake nufi tsaf,wato taje ta wanke mishi mota kenan koko yaya?,so yake ya disgata gaban abokanshi,data sake daga kai ta kalleshi ya maida qafafunsa yadda suke yaci gaba da sabgarsa.
Tsam ta miqe riqe da muqullin ta juya ta soma takawa
"Fahad.....kana so ka jawa mutane raini wajen yaran nan,na gaya maka tun ba yanzu ba banaso ko?" Ta jiyoshi yana fada cikin miskilanci,sai taja qaramin tsaki tana tunanin aikin daya sanyata yanzun,kuma tabbas yana hangota indai motarshi da take hangowa muqullinta ne a hannunsa,bama shi ba har duka abokan nashi suna iya ganota.....
_kuyimin afuwa jina shuru kwana biyu,hidima ce ta biki ta riqeni,naso muku bayani amma hakan bai samu ba,Allah yayi mana jagora_8
*KU MATSO MAZA KUJI LABARIN*
*_Oumahmad collection's_*
*_Shin kina buqatar waje daya tattare dukkan abubuwan buqata da kike son saye ba bata lokaci ko rarraba waje?_*
*to ga OUMAHMAD COLLECTIONS*
*_wadanda ke saida_*
_kayan kitchen_
_kayan sawa nau'i daban daban_
_jakankuna da takalma 'yan ubansu_
_wayoyin hannu kala daban daban na zamani_
_mayafai na gani na fada_
_kayan sawar yara na alfarma_
_kayan daki daga qasashe daban daban,irinsu dubai,china,India,turkey,Malaysia_
_ADRESS DINSU_👇🏽👇🏽
*_Kano hotoro_*
*Ko ku dubasu a facebook da sunan*
*_Maryam muhd_*
*Ko kira kai tsaye ta lambar waya kamar haka*
07014488636
*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽
__________________________________
*KIJI TSORON ALLAH☝🏾☝🏾☝🏾,KARKI TABA ABINDA BA NAKI BA,BA KUMA MALLAKINKI BANE*❗❗❗
Kamar yadda yace bata fasa ba ta isa wajen labaran din,ta kuma buqaci ya hada mata famfon kamar yadda aka saba idan za'a wankewa wani cikin gidan mota,sai daya gama ta kalleshi
"Ance ka bani klien"
"Ah'ah....ai indai motar yallabai Aliyyu za'a wanke yana da carwash dinsa da ake wanke masa dashi,bari na dauko miki" har ya juya zai tafi ta dakatar dashi da sauri tana cewa
"Klien yace a bani,shi zaka daukomin" jimm yayi kadan sannan ya gyada kanshi yayi gaba,babu jimawa ya dawo dashi ya miqa mata,ta bishi da kallo har sai da taga bacewarsa sannan ta taka zuwa wajen mai musu aike aike cikin gidan,wanda wani lokaci yakan zauna a gidan na wasu kwanaki idan yana da ayyuka da yawa har zuwa sanda zai ragesu kana ya tafi gidansu
"Soson qarfe nakeson ka bani aro don Allah hayatu" ta fada tana dan waigawa taga yana ganinta?.
Ba tare da tunanin komai ba ya shiga ciki ya dauko ya miqa matan,ta karba tana jin dadin samun soson sannan ta durfafi motar tana qwafa,gami da qiyasta irin barnar da zatayi masa,yau saita fanshe dukka haushinta akan motar,koma me zai faru ya faru.
Sosai ta zambada klien cikin wani ruwa dake cikin botiki,saboda taji ance ba'a wanke mota da klien,don tana kodar da fentinta,to ba motar ba,shi kansa me motar da zata iya saita kodar dashi,taga kya da gayun da yakewa taqama,kamar wani yafi kyau,itakam ta tsani yadda mata ke kodashi,tana ganin kamar suke tunzurashi ma suke yake sake jin kansa wani,kofi ta ciko ta miqe da niyyar soma watsawa motar
"Zahra'u" taji an ambata sunanta daga bayanta,saita waiwaya,abba babba ne,riqe da maqullin mota da leda a hannunsa
"Na'am abba?....sannu da zuwa" kai ya gyada
"Yauwa....me zakiyi da ruwa kika tarashi haka kamar zakiyi wankin mota" saita marairaice sosai,ta sani cewa mafita tazo,duk da tana son taga ta bata wannan 'yar kyakkyawar motar taga ta tsiya,duk da ta sani ba abune mai sauqi ba,hakan zai iya janyo mata tsatstsauran hukunci daga wajensa,amma ita duk ba damuwarta bane wannan
"Ya Aliyyu ne ya sakani wankin motar" ta fada tana wani sunkui da kai
"Haidar dai?" Ya tambaya cikin mamaki,saiya gyada kai kanta a qasa
"Wannan wanne irin shirmen banza da wofi ne......mace da wankin mota?,ina shi haidar din?" Saita nuna mishi inda suke zaune shi dasu abu sufyan,duk da yanzun shi ya miqe tsaye ya basu baya yana amsa waya,murya ya daga ya kirayi sunanshi,dukkansu hankalinsu ya dawo wajen,sai suka miqe gaba dayansu suka nufo abban.
Cikin girmamawa suka gaidashi sannan suka koma suka barshi da aliyyun,juyawa yayi inda zahra ke tsaye ta baza kunnuwa taji ya zata kaya,ya miqa mata ledar hannunsa
"Qarasamin da ita wajen hajja" hannu biyu tasa ta karba sannan ta juya zuwa sassan hajjan,taso ace a gabanta abban zai masa fadan taga ya zaiyi,amma ko hakan ma ai tasha dashi,tunda ba haka yaso ba.
Dukka suna sassan hajjan kowacce tayi tsuru tsuru,tana ajjiye ledar suna cikata da tambayar yata kaya tsakaninsu,sunga ta dawo da wuri,sai data samu waje ta zauna sannan ta gaya musu yadda akayi,dariya harda masu saukowa daga saman kujerar
"Gaskiya na yadda ya haidar qarshe ne" yasira dake qyaqyata tata dariyar ta fada,cikin dariyar salma ma tace
"Lallai kice ya samu babbar mawankiyar mota,ai kawai a soma biyanki cikin gidan nan an huta biyan su labaran,to wallahi Allah ya qwaceki abba ya qwaceki,don da kin sake kin masa wankin mota da sosan qarfe kashinki ya bushe a gidannan,ke kinsan kudin wannan motar kuwa?" Kafada ta daga cikin rashin damuwa
"Oho,koma nawa ce ai shi ya janyo,haka kawai gaban abokan nan nashi masu shegen ji da kansu da isa saiya yarfani saboda ya raina mana ajawali".