Sashe 58
Alqibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Turo qofar dakin akayi gami da sallama,yaya sadiq ne a gaba dauke da kwanuka,sai hajja dake bayansa,daga bayan hajjan kuma abba yusuf ne.
Dukkansu bakin gadon suka taho kai tsaye,anty aliya na gaida abba yusuf da hajja,ya sadiq kuma ya gaida anty aliyan,gaidasu tayi sannan sukayi mata sannu da jiki,abba yusuf da ya sadiq din basu jima ba su suka tafi suka bar hajjan,don dama ita din kusan kullum yini takeyi.
Dakin saiya zamana daga ita sai hajjan sai anty aliya,sawa tayi aliya ta kawo mata kujera gaban gadon,tana shirin zama tace
"Nidai jikin nan naki har yanzu banga irin sauqin da nakeso ba....anya zahra'u babu wani abun kuma?" Ta tambaya tana dubanta,shuru tayi mata,don batasan amsar da zata bata ba,duk amsar da xata bata din zata zama tamkar tonuwar asirinta ce,sirri ne da a yanzu bata buqatar kowa yasanshi.
Bata kai ga cewa komai din ba wayar hajja ta soma ringing,tayi kiciniyar daukowa ta kasa,saita miqawa aliya
"Ke fitomin da wayar nan,umaima ce don jaraba ta cusa min ita can ciki....ni idan banda dole ma me ya kaini ta'ammali da wannan aba" dariya sosai aliya tayi sannan ta karbi jakar ta ciro mata,idanuwanta ta fiddo waje
"Kai.....haidar ne" zancan da ya sanya zahra saurin dago da kanta,qirjinta yayi wani irin bugawa,saita tsurawa wayar da hajja tayi hanzarin karba,ita dinma kamar zata wafta ne daga hannun aliyan saboda tsabar sauri.
"Assalamu alaikum" hajja ta fara fada bayan ta saita kanta,shuru na wasu sakanni sannan ta qara magana
"Lafiya qalau alhmdlh.....kaiko zaki lafiya?,wanne irin shuru ne satittika masu yawa?" Shuru ta sakeyo kafin tace
"To alhmdlh....Alhmdlh" daga haka saita miqe ta nufi qofar fita wayar na a kunnenta,aliya tabi bayanta,sai zahra ta bisu da idanu,ji take kamar ta tsaida hajjan ta hanata fita,ta jingina kanta da bango tana maida numfashi sanda suka kammala ficewar.
Batasan mintina nawa tayi a hakan ba saijin dawowarsu hajja tayi,ta bude idanunta da sauri,tabi hajjan da kallo,ta tsammaci jin wani abu daga bakin hajjan,amma sai taga taja kujera tayi zamanta abinta kamar yadda ta tashi dazu,hada idanun da sukayi da zahran sai hajjan tace
"Lafiya?,ko jikinne?" Kai kawai ta girgixa mata,ta maida idanun nata ta sake lumshesu,ita kadai tasan yadda zuciyarta ke mata,kamar ta jawo hajja ta tambayeta me yace?,shi dinne da gaske?,saita sanya ran idan anty aliya ta shigo zata ji wani abu daga gareta,aqalla ko relief zata samu.
Saidai koda anty aliyan ma ta shigo shuru kakeji,bata ce da ita uffan ba itama,kamar ma ba haidar din da aketa dakon kiransa bane ya kira,saima suka shiga wata hirar ta daban,hakan ya sake quntata mata,ranta ya baci sosai,sai kawai ta zame ta kwanta ta rufe idanunta kamar me bacci,saidai duk abinda suke tana jinsu,shiga da fitar 'yan dubiya duka,hakanan taji batason magana da kowa.
A hankali ya kashe wayar ya zurata cikin aljihunsa,wani murmushi fuskarshi ke fitarwa,ya dauki cup din baqin tea adan mitsitsin kofi irin na buzaye,ya qara yawan shayin yaci gaba da kurba a hankali,idanunsa kuma nakan sojojin dake gabansu kadan suna training,wanda shi yafara horas dasu,ya dawo yadan huta ne ya kuma yi waya kamar yadda ya tsara.
"Amma.....bansan hikimarka na hana ayi mata maganarka ba,sannan kaidin baka kirata ba" cewar saif dake zaune a gefanshi,sanye da wando da booth na sojoji,sai shirt dake jikinsa,saman kansa hular malafa ce itama irin ta sojojin,sak shigar dake jikin zaki kenan,bambancin kawai shi farar shirt ce a jikinsa,hakanan hular na aje daga gefansa.
Sai daya daga cup din ya qarasa shanye shayin ciki ya dire kofin sannan ya bashi amsa
"Inaso ne a sanda xan koma soyayyata tayi mata yawan da ba zata iya boyeta ba,tayi ɗokina fiye da kowanne mutum cikin ahalina...." Murmushi saif ya sake sannan yace
"Kana da yaqinin tana sonka kota fara sonka kenan?" Miqewa tsaye yayi ya maida hularsa saman kansa,ya dauki bindigar da sukayi amfani da ita,ya kira daya daga cikin sojin dake zirga zirga ya bashi yace yakai tint dinsa sannan ya maida dubansa ga saif
"Ba'a iya rayuwa da al'ummata nake soja kawai ba,har a soyayya ni din sojan ne,ban barta na taho nan ba,sai dana tabbatar na dana mata tarkon da bata isa ta tsallakeshi ba,na bar mata tabon da bazai taba goguwa ba........na yarda da kaina,na kuma yarda da qwarewata....".
Miqewa saif yayi yana murmushi yayi saluting nashi,sai shima ya saki murmushin ya juya yana takawa a hankali zuwan wajen sojojin daya baro.
******** ********
Tun daga ranar take kasa kunne ko zataji wani yayi zancan ya zakin amma bata ji ba,har hajja kuwa,saidai wani lokaci idan ya kira hajjan tana gane hakan,amma harsu gana wayar ta koma gida ba zatace da ita komai ba.
Sannu sannu saita fahimta bayan hajjan ma yana kiran manyan gidan,ranar data gane hakan kawai sai taji ranta ya baci sosai,a lokacin nurse tana zare mata ruwan da yayi saura
"Ya kamata ku sallameni hakan,na gaji da zaman asibitinku" murmushi nurse din ta saki
"Madam ko kina tausayin me gidane daya biya kudin asibitin?,shi yace a barki ki huta sosai koda an gama baki dukka magungunan" shuru tayi tana mamaki,wanne me gida kenan?,ta tambayi kanta,amma kuma tunda taji tace maigidanta lallai ba shakka ya haidar take nufi,idan hakane shin yasan bata da lafiya?,tambayar da bata da amsarta kenan.
Washegari ta takura akan lallai sai sun sallameta,hakanan suka rubuta mata sallamar tunda ta takura suka tattara suka koma gida.
Tun randa suka koma gidan tayi qoqarin basar da komai,tayi qoqari ta cire tunaninsa da damuwa dashi daga ranta,saboda ta fuskanci akwai wata a qasa tattare da hajjan,sai taci alwashin ba zata bari kuwa bari hajjan ta gano lagonta,amma abinda bata sani ba shine shin zata iya?.
_gobe ina da uzururruka,idan kunjini shuru kuyi afuwa,idan kuma dama ta samu zaku ganni da yardar mai duka,na gode_39
Da yammacine liqis,tana zaune a falon hajjanta,gidan yau kusan shuru yake saboda dukka yaran gidan suna islamiyya,saura kuma kowa yana wajen sabgarsa ta yau da kullum,kamar sassan nasu yau su biyu ne daga ita sai hajjan.
Da yake anguwar tasu babu laifi basa rasa nepa,tv ce a kunne take aiki,saidai dukka hankalin zahra yana kan wayar hannunta,charting take,kuma tana jin dadin xaman sosai.
Wayar hajja dake gefanta taji ta dauki burari,ta waiwaya ta kalli wayar da yake tana dab da ita kan hannun kujerar da take kai,number ce babu suna,yanzun hajja ta tashi bata jima ba ta shiga toilet,saita miqa hannunta daya ta jawo wayar ta daga ta kara a kunnenta,yayin da daya hannun take ci gaba da danne dannenta dashi a tata wayar
"Hajjan bata kusa,amma idan ta iso xa'a gaya mata" shuru taji anyi,duk da cewa da alamu bawai rashin network bane,tunda ga hayaniya irin daga dan nesa da inda me wayar yakeyin wayar nan tana shigo mata tana ji,saita dan maida hankalinta kan kiran,ta daga wayar ta duba taga ana kan layi,ta sake maidawa kunnenta tana fadin
"Hello....ance hajjan bata kusa,idan ta fito za'a gaya mata" jin still dai an sake yin shuru sai ta daga wayar daga kunneta hadi da jan tsaki,ta kashe kiran,ta maida wayar gefanta ta aje taci gaba da chart dinta.
Tana shirin shiga wani grp nasu na 'yan makarantar kachako unity girls,group ne na 'yan set dinsu da suka gama makaranta a shekarar,saiga saqo daga saman watsapp dinta ya shigo da baquwar number,bata fasa shiga grp din ba,sai data shiga ta gama uzurinta ta fito sannan ta duba saqon,saqone da bai wuce layi daya ba,amma saiya tsaya mata a rai,ta dinga nanatashi ita kadai
*_KINYI NESA DA IDANUNA DA RAYUWATA,AMMA KINA KUSA DA RUHI DA ZUCIYATA_*
sake shiga profile din tayi ko zata ga suna,babu suna babu dp,ta bincike contact dinta tsaf babu me irin number,zargin da yazo kanta yasa tayi saurin daukar wayar hajja ta bude,ta loda numbers din ta danna dial ko zataga suna ya fito a number amma babu,tabbacin zarginta ba haka yake ba kenan,ba haidar bane,to waye?.
Jin takun tahowar hajjan yasa ta maida mata wayar ta ajjiye,don ta lura yanzu wani gani gani take mata akan wayarta,saidai ta ganta hajjan
"Me akemin da waya ne?,bana son fa satar lamba ahto....idan mutum naso yayimin magana da kaina na dauka na bashi" shuru zahra ta mata,sai da taga ba zatayi shuru ba sannan tace
"Ni ai duka wayarki hajja babu lambar da xan sata fa,babu,ni kawai ko bandakin zaki shiga ki dinga shiga da abarki ma huta" baki ta tabe
"Oho dai,banda rashin gaskiya daga jin tahowata sai a maida waya da sauri a aje,kinga kuwa ai babu gaskiya ne" ta qarasa maganar tana zama,sai kawai zahran tayi kwanciyarta ba tare data sake amsa mata ba,tana ci gaba da maimaita saqon,jikinta yana bata daga inda saqon ya fito,amma zuciyarta ta gaza gasgata hakan,har sai data gaji da kallon saqon,kamar shi xai bata amsar tambayarta,ta sauka daga watsapp dinma gaba daya,saita dora wayar saman qirjinta ta lumshe idanunta tana tuna wasu abubuwa da suka zame mata farilla kullum sai tayi bitarsu a kwanyarta,haka nan tunasu suke sanyata nishadi suke kuma debe mata kewa.
****** ****** *******
*_BAYAN WASU KWANAKI_*
Yamma ce lis,wanda tun safiyar ranar ake fama da hadowar hadari da kuma washewarsa,saidai zuwa yammacin hadarin ya hadu sosai a sama,yana bada iska mai sanyi hadi da qamshin qasa,wanda hakan ke alamta cewa ruwan sama na tafe kowanne lokaci daga sannan
Ita da umaima da ilham ne a falon hajjan,ilham na mata manyan kitso a kanta saboda wankeshi da tayi,ya kuma isheta hakanan babu kitso,tana mata kitson suna hira jefi jefi,suna kuma kallon tashar arewa 24,gidan yauma babu mutane sosai,duk sun tafi sunan faccalar hafsat data haihu,da yake macace me kirki,kusan kowa ya santa a gidan,sauran yaran kuwa kowa yana makaranta.
Dukkansu bakin gadon suka taho kai tsaye,anty aliya na gaida abba yusuf da hajja,ya sadiq kuma ya gaida anty aliyan,gaidasu tayi sannan sukayi mata sannu da jiki,abba yusuf da ya sadiq din basu jima ba su suka tafi suka bar hajjan,don dama ita din kusan kullum yini takeyi.
Dakin saiya zamana daga ita sai hajjan sai anty aliya,sawa tayi aliya ta kawo mata kujera gaban gadon,tana shirin zama tace
"Nidai jikin nan naki har yanzu banga irin sauqin da nakeso ba....anya zahra'u babu wani abun kuma?" Ta tambaya tana dubanta,shuru tayi mata,don batasan amsar da zata bata ba,duk amsar da xata bata din zata zama tamkar tonuwar asirinta ce,sirri ne da a yanzu bata buqatar kowa yasanshi.
Bata kai ga cewa komai din ba wayar hajja ta soma ringing,tayi kiciniyar daukowa ta kasa,saita miqawa aliya
"Ke fitomin da wayar nan,umaima ce don jaraba ta cusa min ita can ciki....ni idan banda dole ma me ya kaini ta'ammali da wannan aba" dariya sosai aliya tayi sannan ta karbi jakar ta ciro mata,idanuwanta ta fiddo waje
"Kai.....haidar ne" zancan da ya sanya zahra saurin dago da kanta,qirjinta yayi wani irin bugawa,saita tsurawa wayar da hajja tayi hanzarin karba,ita dinma kamar zata wafta ne daga hannun aliyan saboda tsabar sauri.
"Assalamu alaikum" hajja ta fara fada bayan ta saita kanta,shuru na wasu sakanni sannan ta qara magana
"Lafiya qalau alhmdlh.....kaiko zaki lafiya?,wanne irin shuru ne satittika masu yawa?" Shuru ta sakeyo kafin tace
"To alhmdlh....Alhmdlh" daga haka saita miqe ta nufi qofar fita wayar na a kunnenta,aliya tabi bayanta,sai zahra ta bisu da idanu,ji take kamar ta tsaida hajjan ta hanata fita,ta jingina kanta da bango tana maida numfashi sanda suka kammala ficewar.
Batasan mintina nawa tayi a hakan ba saijin dawowarsu hajja tayi,ta bude idanunta da sauri,tabi hajjan da kallo,ta tsammaci jin wani abu daga bakin hajjan,amma sai taga taja kujera tayi zamanta abinta kamar yadda ta tashi dazu,hada idanun da sukayi da zahran sai hajjan tace
"Lafiya?,ko jikinne?" Kai kawai ta girgixa mata,ta maida idanun nata ta sake lumshesu,ita kadai tasan yadda zuciyarta ke mata,kamar ta jawo hajja ta tambayeta me yace?,shi dinne da gaske?,saita sanya ran idan anty aliya ta shigo zata ji wani abu daga gareta,aqalla ko relief zata samu.
Saidai koda anty aliyan ma ta shigo shuru kakeji,bata ce da ita uffan ba itama,kamar ma ba haidar din da aketa dakon kiransa bane ya kira,saima suka shiga wata hirar ta daban,hakan ya sake quntata mata,ranta ya baci sosai,sai kawai ta zame ta kwanta ta rufe idanunta kamar me bacci,saidai duk abinda suke tana jinsu,shiga da fitar 'yan dubiya duka,hakanan taji batason magana da kowa.
A hankali ya kashe wayar ya zurata cikin aljihunsa,wani murmushi fuskarshi ke fitarwa,ya dauki cup din baqin tea adan mitsitsin kofi irin na buzaye,ya qara yawan shayin yaci gaba da kurba a hankali,idanunsa kuma nakan sojojin dake gabansu kadan suna training,wanda shi yafara horas dasu,ya dawo yadan huta ne ya kuma yi waya kamar yadda ya tsara.
"Amma.....bansan hikimarka na hana ayi mata maganarka ba,sannan kaidin baka kirata ba" cewar saif dake zaune a gefanshi,sanye da wando da booth na sojoji,sai shirt dake jikinsa,saman kansa hular malafa ce itama irin ta sojojin,sak shigar dake jikin zaki kenan,bambancin kawai shi farar shirt ce a jikinsa,hakanan hular na aje daga gefansa.
Sai daya daga cup din ya qarasa shanye shayin ciki ya dire kofin sannan ya bashi amsa
"Inaso ne a sanda xan koma soyayyata tayi mata yawan da ba zata iya boyeta ba,tayi ɗokina fiye da kowanne mutum cikin ahalina...." Murmushi saif ya sake sannan yace
"Kana da yaqinin tana sonka kota fara sonka kenan?" Miqewa tsaye yayi ya maida hularsa saman kansa,ya dauki bindigar da sukayi amfani da ita,ya kira daya daga cikin sojin dake zirga zirga ya bashi yace yakai tint dinsa sannan ya maida dubansa ga saif
"Ba'a iya rayuwa da al'ummata nake soja kawai ba,har a soyayya ni din sojan ne,ban barta na taho nan ba,sai dana tabbatar na dana mata tarkon da bata isa ta tsallakeshi ba,na bar mata tabon da bazai taba goguwa ba........na yarda da kaina,na kuma yarda da qwarewata....".
Miqewa saif yayi yana murmushi yayi saluting nashi,sai shima ya saki murmushin ya juya yana takawa a hankali zuwan wajen sojojin daya baro.
******** ********
Tun daga ranar take kasa kunne ko zataji wani yayi zancan ya zakin amma bata ji ba,har hajja kuwa,saidai wani lokaci idan ya kira hajjan tana gane hakan,amma harsu gana wayar ta koma gida ba zatace da ita komai ba.
Sannu sannu saita fahimta bayan hajjan ma yana kiran manyan gidan,ranar data gane hakan kawai sai taji ranta ya baci sosai,a lokacin nurse tana zare mata ruwan da yayi saura
"Ya kamata ku sallameni hakan,na gaji da zaman asibitinku" murmushi nurse din ta saki
"Madam ko kina tausayin me gidane daya biya kudin asibitin?,shi yace a barki ki huta sosai koda an gama baki dukka magungunan" shuru tayi tana mamaki,wanne me gida kenan?,ta tambayi kanta,amma kuma tunda taji tace maigidanta lallai ba shakka ya haidar take nufi,idan hakane shin yasan bata da lafiya?,tambayar da bata da amsarta kenan.
Washegari ta takura akan lallai sai sun sallameta,hakanan suka rubuta mata sallamar tunda ta takura suka tattara suka koma gida.
Tun randa suka koma gidan tayi qoqarin basar da komai,tayi qoqari ta cire tunaninsa da damuwa dashi daga ranta,saboda ta fuskanci akwai wata a qasa tattare da hajjan,sai taci alwashin ba zata bari kuwa bari hajjan ta gano lagonta,amma abinda bata sani ba shine shin zata iya?.
_gobe ina da uzururruka,idan kunjini shuru kuyi afuwa,idan kuma dama ta samu zaku ganni da yardar mai duka,na gode_39
Da yammacine liqis,tana zaune a falon hajjanta,gidan yau kusan shuru yake saboda dukka yaran gidan suna islamiyya,saura kuma kowa yana wajen sabgarsa ta yau da kullum,kamar sassan nasu yau su biyu ne daga ita sai hajjan.
Da yake anguwar tasu babu laifi basa rasa nepa,tv ce a kunne take aiki,saidai dukka hankalin zahra yana kan wayar hannunta,charting take,kuma tana jin dadin xaman sosai.
Wayar hajja dake gefanta taji ta dauki burari,ta waiwaya ta kalli wayar da yake tana dab da ita kan hannun kujerar da take kai,number ce babu suna,yanzun hajja ta tashi bata jima ba ta shiga toilet,saita miqa hannunta daya ta jawo wayar ta daga ta kara a kunnenta,yayin da daya hannun take ci gaba da danne dannenta dashi a tata wayar
"Hajjan bata kusa,amma idan ta iso xa'a gaya mata" shuru taji anyi,duk da cewa da alamu bawai rashin network bane,tunda ga hayaniya irin daga dan nesa da inda me wayar yakeyin wayar nan tana shigo mata tana ji,saita dan maida hankalinta kan kiran,ta daga wayar ta duba taga ana kan layi,ta sake maidawa kunnenta tana fadin
"Hello....ance hajjan bata kusa,idan ta fito za'a gaya mata" jin still dai an sake yin shuru sai ta daga wayar daga kunneta hadi da jan tsaki,ta kashe kiran,ta maida wayar gefanta ta aje taci gaba da chart dinta.
Tana shirin shiga wani grp nasu na 'yan makarantar kachako unity girls,group ne na 'yan set dinsu da suka gama makaranta a shekarar,saiga saqo daga saman watsapp dinta ya shigo da baquwar number,bata fasa shiga grp din ba,sai data shiga ta gama uzurinta ta fito sannan ta duba saqon,saqone da bai wuce layi daya ba,amma saiya tsaya mata a rai,ta dinga nanatashi ita kadai
*_KINYI NESA DA IDANUNA DA RAYUWATA,AMMA KINA KUSA DA RUHI DA ZUCIYATA_*
sake shiga profile din tayi ko zata ga suna,babu suna babu dp,ta bincike contact dinta tsaf babu me irin number,zargin da yazo kanta yasa tayi saurin daukar wayar hajja ta bude,ta loda numbers din ta danna dial ko zataga suna ya fito a number amma babu,tabbacin zarginta ba haka yake ba kenan,ba haidar bane,to waye?.
Jin takun tahowar hajjan yasa ta maida mata wayar ta ajjiye,don ta lura yanzu wani gani gani take mata akan wayarta,saidai ta ganta hajjan
"Me akemin da waya ne?,bana son fa satar lamba ahto....idan mutum naso yayimin magana da kaina na dauka na bashi" shuru zahra ta mata,sai da taga ba zatayi shuru ba sannan tace
"Ni ai duka wayarki hajja babu lambar da xan sata fa,babu,ni kawai ko bandakin zaki shiga ki dinga shiga da abarki ma huta" baki ta tabe
"Oho dai,banda rashin gaskiya daga jin tahowata sai a maida waya da sauri a aje,kinga kuwa ai babu gaskiya ne" ta qarasa maganar tana zama,sai kawai zahran tayi kwanciyarta ba tare data sake amsa mata ba,tana ci gaba da maimaita saqon,jikinta yana bata daga inda saqon ya fito,amma zuciyarta ta gaza gasgata hakan,har sai data gaji da kallon saqon,kamar shi xai bata amsar tambayarta,ta sauka daga watsapp dinma gaba daya,saita dora wayar saman qirjinta ta lumshe idanunta tana tuna wasu abubuwa da suka zame mata farilla kullum sai tayi bitarsu a kwanyarta,haka nan tunasu suke sanyata nishadi suke kuma debe mata kewa.
****** ****** *******
*_BAYAN WASU KWANAKI_*
Yamma ce lis,wanda tun safiyar ranar ake fama da hadowar hadari da kuma washewarsa,saidai zuwa yammacin hadarin ya hadu sosai a sama,yana bada iska mai sanyi hadi da qamshin qasa,wanda hakan ke alamta cewa ruwan sama na tafe kowanne lokaci daga sannan
Ita da umaima da ilham ne a falon hajjan,ilham na mata manyan kitso a kanta saboda wankeshi da tayi,ya kuma isheta hakanan babu kitso,tana mata kitson suna hira jefi jefi,suna kuma kallon tashar arewa 24,gidan yauma babu mutane sosai,duk sun tafi sunan faccalar hafsat data haihu,da yake macace me kirki,kusan kowa ya santa a gidan,sauran yaran kuwa kowa yana makaranta.