Sashe 19
Alqibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kafin ta qarasa sassansu wayarta dake hannunta tayi tsuwwa,hindatu ce ke kiranta,saita dakata da tafiyar ta tsaya amsa wayar
"Ya akayi ne qawa?"
"Lafiya wallahi.....ya gida yasu daddy?"
"Lafiya lau,duka na barosu a gida bama tare"
"Ina kika tafi kuma?" Zahran ta tuhumeta tana dan tsuke gira
"Ba wani waje bane me nisa,lagos ne,ana bikin wata qawata....so akwai wani event da za'ayi a nan din" gyara tsaiwa tayi
"Amma fisabilillahi hindu biki a kasa yinsa a garinsu amarya har sai an dauki wani event din an kaishi wani gari me nisa haka?"
"Wanne nisa tafiyar jirgi?,yan mintuna marasa yawa anje"
"A ina kuka sauka kenan?"
"Guest house mana,muna da wanda muka sani ne?" Dogon tsaki zahran taja
"Kunnen qashinki shi zai sa mu raba gari dake hindu,tunda bakya yarda da abinda nake gaya miki" dariya ta saki
"Ko kin raba gari dani ni bazan raba dake ba.....karki damu,idan akwai wani abu ba dai dai ba daddy ko mommy xasu yi magana,ni kiranki nayi ma na gaya miki....gobe fa za'a je strike din nan,kuma sai baba ta gani sunce" bata rai zahra tayi
"Wato a duniya shi dalibin nigeria bazai taba gama karatu ta dadin rai farinciki ko walwala ba?.....ai shikenan,sun yiwa kansu,muma mayi azuminmu a dadi,Allah yasa sai an sallace za'a koma" dariya hindatu ta saki
"Wallahi nima haka nace,kinsan hali dai,idan ina azumi ba kanta,bana ganewa kwata kwata" saita kauda wannan zancan ta dauko na farko
"Yanzu yaushe xaki dawo?"
"Gobe in sha Allah...."
"Kin tabbata?"
"Da gaske nake....jibi ma zanzo har gida ki tabbatar da kanki,saka ranki a inuwa" daga haka zahran ta katse wayar,Allah ya sani tana qaunar hindatun,kuma tana da halaye masu kyau na kirki da son jama'a,amma rayuwarta ita a wajenta da iyayenta ba komai bane saboda tsabar wayewa,dukkansu bata zarginsu da aikata alfasha da maza,amma saidai yanayin yadda suke gudanar da rayuwarsu wayewarsu tayi yawa,irin wayewar da dole zata iya janyo maka zargi ga idanun al'umma,kuma yana daga cikin cikar kamalar mutum ya guji dukkan wani abu da zai jefa zarginsa a zuciyar al'umma,da wannan tunanin ta isa sassan hajjan,saita tadda haidar dofane a hannun kujera yana latsa waya,jikinsa wata fara qal din shirt ce ta maza mai V neck short sleeve,sai wandon kaki dake jikinsa,da wani farin qal din booth da yakai masa har qauri,hajja na zaune daga gefansa,da alama wata maganar takeyi dashi,shi kuma yana sauraronta,yayi wani irin kwarjini musamman yau daya bar iya wandon ma kawai a jikinsa,hakanan fatarsa tayi fresh tamkar babu abinda ke damunsa,saidai kuma fuskarnan tana nan kamar kowanne lokaci babu rahama ko digon dariya tattare da ita,sai gashinsa daketa glowing wanda ya qara masa kyau da cikar mazantaka.
Kansa ya daga ya jefeta da wani irin kallo,murya a dake yace
"Ke....zonan" da baya ta dawo ta zauna jikin hajja kamar zata shige cikinta,ya cira kai da lumsassun idanunsa dake cike da kwarjini yace yana duban hajja
"Ya akayi ta fita da wannan shigar?,waye kuma a waje data tsaya dashi?" Duban zahra hajja tayi sannan ta dubeshi
"Me ya samu shigar tata?,sannan idan saurayi yayi sallama da budurwa dama binsu ake a tsaya tare dasu ko kuwa?" Sai daya lumshe idanunsaya budesu sannan yace
"Amma hajja kinfi kowa sanin tsarina a kansu tun sauran na gidan nan ko game da saka qananun mayafai ko?,sannan haka sama taka ba'asan mutum ba yazo ya kirata ta kada wadannan zoqala zoqalan qafafun nata ta fita?".
Wayyo....ji zahra tayi kamar ya kwada mata mari,tunda take ba wanda ya taba aibanta surarta saishi,tasha ji a bakin maza daban daban yadda suke koda halittarta duk da ita ba burgeta hakan yake ba,ba kuma damuwa tayi dasu ba,shine yau shi don wulaqanci zai jefeta da wannan kalmar?.
Hajja kam baki ta kama sannan ta saki tana ruqo hannun zahran
"Karka sake gayawa jikata haka,a ciki ni banga abun laifi ba,indai ba daga bracck aka bata kama rai ba zaka zo ka juyeshi a nan ahto" qaramar ajiyar zuciya ya sauke
"Ke tashi ki bamu waje" ya fada cikin sigar bada umarni,saita miqe da hanzari,ta murguda baki bayan ta juya musu baya cikin ranta tana mita.
Sai da yaga shigewarta sannan ya dubi hajja dai
"Hajja....yarinyar nan,haka kawai kuka kaita universty,ke baki ganin sauyin dabi'u tattare da ita?" Hannu ta daga masa
"Haidar....haidar...me yasa haka ne?,ni babu wani abu da zahrata ta sauya dashi,kada na sake jin wani abu makamancin haka daga bakinka" wayarsa ya mayar aljihun unifoarm din sojojin dake jikinsa,sannan ya miqe a nutse
"Ina kuma zaka muna magana?" Cikin i don't care manner yace
"Akwai kaya da nakeso a fito dasu kafin na shiga ciki,don bazan samu fitowa da wuri ba....idan na fito ma tattauna" daga haka ya soma takawa da wata irin tafiya mai cike da qasaita da nuna qarfi da ginuwar gangar jiki yabar falon.
Sai a sannan zahra dake labe ta fito da hanzari muryarta na rawa kamar zata sake kuka tace
"Kinji ko hajja....kinji sharrin da yakeson yimin,ni ba'ace komai a kanshi ba saboda zaman bariki ba saini don ina makaranta"
"Kinga dagani....na gaji da wannan iskancin naku keda zaki,yara kamar mayu?,kamar masu ganin hanjin juna?,to wallahi idan bakuyi wasa ba aure zan saka iyayenku su daura muku naga qaryar iskanci" wani irin tsalle zahra dake zaune a jikin hajja ga buga kamar wadda aka dorawa kunama a jiki,ita kanta hajjan saida tayi sak cikin tsoron tana duban zahra dake fadin
"A'uzu billahi minash shaidanir rajim,hajja....wacce irin masifa kike ambata da yammacin juma'ar nan?" Ta fada idanunta duka a waje,tafin hannu kawai hajja ta saka tana rufe bakinta dashi tana fadin
"La'ilaha ilallahu,muhammadurrasulullahi,sallallahu alaihi wa sallam inna wuro?,kamar wadda tace miki tsohuwarki ta mutu?,wannan zancen ne masifa?,anya zahra?" Ganin yadda bacin ranta ya bayyana yasa ta sassauta nata,ta qarasa wajen hajjan ta zauna tana narke murya
"Kiyi haquri hajja,ba haka nake nufi ba,don Allah ki haquri,amma.in sha Allah na daina shiga huruminsa,dama ni ba shiga nake ba,shine haka nan ba gaira ba dalili ya matsantamin"
"Kema ai bajin magana kike ba,ko don kinga ina baki kariya?"kamar zatayi kuka tace
"kiyi haquri dai don Allah abar zancan,na daina in sha Allahu" shuru tayi kamar ba zatayi magana ba,sai kuma ta sake ajiyar zuciya
"Ai shikenan....Allah ya kyauta" jin haka don kada ta sake jan wata maganar saita miqe kawai tayi dakinta,a ranta tana juya zancan
"Itama.hajjan nan wani lokacin wlh tuburarriya ce,haka kawai da yammacin ranar juma'a,dai dai sanda ake amsa addu'a ki fadi wannan mummunan kalamin kisa 'yan amin su amsa?" Ita daya ta qaraci mitarta cikin daki harta haqura.
Da magariba zata gurin me gadi amsowa hajja goro da me gadi yace tazo ta amsa taga qofar gidan nasu cike da jama'a,kusan hakan ba sabon abu bane wajensu,duk randa aliyyu ya sauka a garin gidansun baya rabo da mutane,duk da cewa ko baya nan din ba'a rasa mabuqata jifa jifa masu neman taimako,amma kuma cikarsu bata kaiwa yadda take a yanzun.
A yanzun ma rabon kayan abincin azumi da alama yasa akeyi,don ga kwalayen kayan abinci nan kala kala da qananun buhun shinkafa,tabe baki tayi sanda taji wani yana zabga addu'a da koda layin duk da baya wajen,don baya zama a inda ake rabon,saidai ya wakilta ma'aikatan gidan
"Uban tausayi uban talakawan unguwar nan dama gundumar nan gaba daya,zuciyarka fara tas take hakama ayyukanka,ubangiji yasa kafi haka,ya qara arziqi da daukaka"
"Green snake....under green grass kenan" ta fada qasa qasa tana sake tabe baki,tana tsaye tana kallon yadda suke layi suna karba cikin farinciki,don mai gadin shima yana can,sai daya hangota sannan ya iso yana cewa
"Kiyi haquri uwar masu gida,banga zuwanki ba,saqon hajiya hajja ko?,ina can muna rabon aikin alkhairin haidar.....wannan yaro ya dace,ubangiji ya kareshi yasa yafi haka,yana faranta ran talakawa" ya fada yana cusa kanshi dan dakinsa,ya dauko saqon ya miqa.mata ta karba ta juya,tana sake jiyo kalaman yabo daga bakin mutane.
Ta sani cewa wani lokaci akan zo ma su hajja godiya kan wani abu da aliyyun yayi cikin unguwar,saidai su amsa don babu wanda yasan ma yayi din,kusan haka dabi'arsa take idan zaiyi wani abun alkhairin,itakam tana dauka kawai shashanci ne irin na mutane,don bataga alamu a yadda aliyyun yake da baqar zuciya,zai iya wani abun arziqin da zai farantawa wani rai ba.
*************
Kamar da wasa kuwa wata washegarin ta gama wankewa hajja qananun kayanta ta fito ta falo,tana tsaye gaban tv taji kamar muryar hindatu tana magana,da alama yaran gidansu ne da yau gaba dayan 'yan mazan da matasan abba babba ya raba musu gyaran flowers da farfajiyar gidan,tunda an yiwa wanda yake musu wannan hidimar rasuwa,ya tafi qauye.
Aje remote din tayi tana tafa hannu cikin mamaki da jin dadi
"Na zaci zancanki ne kawai fa da kika ce zaki zo" itama tana murmushin tace
"Kin taba ganin na saba alaqawari" kai ta girgiza tace
"Ina sara miki ta wannan sashen ai".
Sai data gabatar mata da ruwa da lemo sannan ta yiwa hajja magana ta fito suka gaisa,ba wannan bane zuwanta gidan na farko ba,ta taba zuwa sau daya,wannan ne na biyu,hindatun ta jima sosai suna hira,don a nan taci abincin rana ma,sannan ta kira jannah batula nadiya da farida suka hada kira na bai daya suka sha hira har zuwa sanda akayi sallar la'asar,ta shiga nan bandakin zahra din ta daura alwala.
Tana saman abun sallar zata tayar kenan ta waiwayo ta dubi zahra
"Yauma fa na sake ganin yayankunnan,ya hakimce saman kujera qafa daya saman daya yana karatun jarida,duka yaran kowa cikin hankalinsa yake aikinsa ba hayaniya da alama shike gadinsu,bakiga yadda tsare gidan da yayi yayi masa kyau ba"hindatu ta fada,kallonta zahra tayi
"Wanne fa?,ya musty ko ya shamsu?"
"A'ah fa....sojan nan....wallahi nikam idanuna basu taba ganin namijin da yamin kwarjini,ya kuma burgeni,na kuma ji na shirya aurensa ba irinsa....don Allah qawata ki shigemin gaba mana" ta fada cikin karyar da murya.
"Ya akayi ne qawa?"
"Lafiya wallahi.....ya gida yasu daddy?"
"Lafiya lau,duka na barosu a gida bama tare"
"Ina kika tafi kuma?" Zahran ta tuhumeta tana dan tsuke gira
"Ba wani waje bane me nisa,lagos ne,ana bikin wata qawata....so akwai wani event da za'ayi a nan din" gyara tsaiwa tayi
"Amma fisabilillahi hindu biki a kasa yinsa a garinsu amarya har sai an dauki wani event din an kaishi wani gari me nisa haka?"
"Wanne nisa tafiyar jirgi?,yan mintuna marasa yawa anje"
"A ina kuka sauka kenan?"
"Guest house mana,muna da wanda muka sani ne?" Dogon tsaki zahran taja
"Kunnen qashinki shi zai sa mu raba gari dake hindu,tunda bakya yarda da abinda nake gaya miki" dariya ta saki
"Ko kin raba gari dani ni bazan raba dake ba.....karki damu,idan akwai wani abu ba dai dai ba daddy ko mommy xasu yi magana,ni kiranki nayi ma na gaya miki....gobe fa za'a je strike din nan,kuma sai baba ta gani sunce" bata rai zahra tayi
"Wato a duniya shi dalibin nigeria bazai taba gama karatu ta dadin rai farinciki ko walwala ba?.....ai shikenan,sun yiwa kansu,muma mayi azuminmu a dadi,Allah yasa sai an sallace za'a koma" dariya hindatu ta saki
"Wallahi nima haka nace,kinsan hali dai,idan ina azumi ba kanta,bana ganewa kwata kwata" saita kauda wannan zancan ta dauko na farko
"Yanzu yaushe xaki dawo?"
"Gobe in sha Allah...."
"Kin tabbata?"
"Da gaske nake....jibi ma zanzo har gida ki tabbatar da kanki,saka ranki a inuwa" daga haka zahran ta katse wayar,Allah ya sani tana qaunar hindatun,kuma tana da halaye masu kyau na kirki da son jama'a,amma rayuwarta ita a wajenta da iyayenta ba komai bane saboda tsabar wayewa,dukkansu bata zarginsu da aikata alfasha da maza,amma saidai yanayin yadda suke gudanar da rayuwarsu wayewarsu tayi yawa,irin wayewar da dole zata iya janyo maka zargi ga idanun al'umma,kuma yana daga cikin cikar kamalar mutum ya guji dukkan wani abu da zai jefa zarginsa a zuciyar al'umma,da wannan tunanin ta isa sassan hajjan,saita tadda haidar dofane a hannun kujera yana latsa waya,jikinsa wata fara qal din shirt ce ta maza mai V neck short sleeve,sai wandon kaki dake jikinsa,da wani farin qal din booth da yakai masa har qauri,hajja na zaune daga gefansa,da alama wata maganar takeyi dashi,shi kuma yana sauraronta,yayi wani irin kwarjini musamman yau daya bar iya wandon ma kawai a jikinsa,hakanan fatarsa tayi fresh tamkar babu abinda ke damunsa,saidai kuma fuskarnan tana nan kamar kowanne lokaci babu rahama ko digon dariya tattare da ita,sai gashinsa daketa glowing wanda ya qara masa kyau da cikar mazantaka.
Kansa ya daga ya jefeta da wani irin kallo,murya a dake yace
"Ke....zonan" da baya ta dawo ta zauna jikin hajja kamar zata shige cikinta,ya cira kai da lumsassun idanunsa dake cike da kwarjini yace yana duban hajja
"Ya akayi ta fita da wannan shigar?,waye kuma a waje data tsaya dashi?" Duban zahra hajja tayi sannan ta dubeshi
"Me ya samu shigar tata?,sannan idan saurayi yayi sallama da budurwa dama binsu ake a tsaya tare dasu ko kuwa?" Sai daya lumshe idanunsaya budesu sannan yace
"Amma hajja kinfi kowa sanin tsarina a kansu tun sauran na gidan nan ko game da saka qananun mayafai ko?,sannan haka sama taka ba'asan mutum ba yazo ya kirata ta kada wadannan zoqala zoqalan qafafun nata ta fita?".
Wayyo....ji zahra tayi kamar ya kwada mata mari,tunda take ba wanda ya taba aibanta surarta saishi,tasha ji a bakin maza daban daban yadda suke koda halittarta duk da ita ba burgeta hakan yake ba,ba kuma damuwa tayi dasu ba,shine yau shi don wulaqanci zai jefeta da wannan kalmar?.
Hajja kam baki ta kama sannan ta saki tana ruqo hannun zahran
"Karka sake gayawa jikata haka,a ciki ni banga abun laifi ba,indai ba daga bracck aka bata kama rai ba zaka zo ka juyeshi a nan ahto" qaramar ajiyar zuciya ya sauke
"Ke tashi ki bamu waje" ya fada cikin sigar bada umarni,saita miqe da hanzari,ta murguda baki bayan ta juya musu baya cikin ranta tana mita.
Sai da yaga shigewarta sannan ya dubi hajja dai
"Hajja....yarinyar nan,haka kawai kuka kaita universty,ke baki ganin sauyin dabi'u tattare da ita?" Hannu ta daga masa
"Haidar....haidar...me yasa haka ne?,ni babu wani abu da zahrata ta sauya dashi,kada na sake jin wani abu makamancin haka daga bakinka" wayarsa ya mayar aljihun unifoarm din sojojin dake jikinsa,sannan ya miqe a nutse
"Ina kuma zaka muna magana?" Cikin i don't care manner yace
"Akwai kaya da nakeso a fito dasu kafin na shiga ciki,don bazan samu fitowa da wuri ba....idan na fito ma tattauna" daga haka ya soma takawa da wata irin tafiya mai cike da qasaita da nuna qarfi da ginuwar gangar jiki yabar falon.
Sai a sannan zahra dake labe ta fito da hanzari muryarta na rawa kamar zata sake kuka tace
"Kinji ko hajja....kinji sharrin da yakeson yimin,ni ba'ace komai a kanshi ba saboda zaman bariki ba saini don ina makaranta"
"Kinga dagani....na gaji da wannan iskancin naku keda zaki,yara kamar mayu?,kamar masu ganin hanjin juna?,to wallahi idan bakuyi wasa ba aure zan saka iyayenku su daura muku naga qaryar iskanci" wani irin tsalle zahra dake zaune a jikin hajja ga buga kamar wadda aka dorawa kunama a jiki,ita kanta hajjan saida tayi sak cikin tsoron tana duban zahra dake fadin
"A'uzu billahi minash shaidanir rajim,hajja....wacce irin masifa kike ambata da yammacin juma'ar nan?" Ta fada idanunta duka a waje,tafin hannu kawai hajja ta saka tana rufe bakinta dashi tana fadin
"La'ilaha ilallahu,muhammadurrasulullahi,sallallahu alaihi wa sallam inna wuro?,kamar wadda tace miki tsohuwarki ta mutu?,wannan zancen ne masifa?,anya zahra?" Ganin yadda bacin ranta ya bayyana yasa ta sassauta nata,ta qarasa wajen hajjan ta zauna tana narke murya
"Kiyi haquri hajja,ba haka nake nufi ba,don Allah ki haquri,amma.in sha Allah na daina shiga huruminsa,dama ni ba shiga nake ba,shine haka nan ba gaira ba dalili ya matsantamin"
"Kema ai bajin magana kike ba,ko don kinga ina baki kariya?"kamar zatayi kuka tace
"kiyi haquri dai don Allah abar zancan,na daina in sha Allahu" shuru tayi kamar ba zatayi magana ba,sai kuma ta sake ajiyar zuciya
"Ai shikenan....Allah ya kyauta" jin haka don kada ta sake jan wata maganar saita miqe kawai tayi dakinta,a ranta tana juya zancan
"Itama.hajjan nan wani lokacin wlh tuburarriya ce,haka kawai da yammacin ranar juma'a,dai dai sanda ake amsa addu'a ki fadi wannan mummunan kalamin kisa 'yan amin su amsa?" Ita daya ta qaraci mitarta cikin daki harta haqura.
Da magariba zata gurin me gadi amsowa hajja goro da me gadi yace tazo ta amsa taga qofar gidan nasu cike da jama'a,kusan hakan ba sabon abu bane wajensu,duk randa aliyyu ya sauka a garin gidansun baya rabo da mutane,duk da cewa ko baya nan din ba'a rasa mabuqata jifa jifa masu neman taimako,amma kuma cikarsu bata kaiwa yadda take a yanzun.
A yanzun ma rabon kayan abincin azumi da alama yasa akeyi,don ga kwalayen kayan abinci nan kala kala da qananun buhun shinkafa,tabe baki tayi sanda taji wani yana zabga addu'a da koda layin duk da baya wajen,don baya zama a inda ake rabon,saidai ya wakilta ma'aikatan gidan
"Uban tausayi uban talakawan unguwar nan dama gundumar nan gaba daya,zuciyarka fara tas take hakama ayyukanka,ubangiji yasa kafi haka,ya qara arziqi da daukaka"
"Green snake....under green grass kenan" ta fada qasa qasa tana sake tabe baki,tana tsaye tana kallon yadda suke layi suna karba cikin farinciki,don mai gadin shima yana can,sai daya hangota sannan ya iso yana cewa
"Kiyi haquri uwar masu gida,banga zuwanki ba,saqon hajiya hajja ko?,ina can muna rabon aikin alkhairin haidar.....wannan yaro ya dace,ubangiji ya kareshi yasa yafi haka,yana faranta ran talakawa" ya fada yana cusa kanshi dan dakinsa,ya dauko saqon ya miqa.mata ta karba ta juya,tana sake jiyo kalaman yabo daga bakin mutane.
Ta sani cewa wani lokaci akan zo ma su hajja godiya kan wani abu da aliyyun yayi cikin unguwar,saidai su amsa don babu wanda yasan ma yayi din,kusan haka dabi'arsa take idan zaiyi wani abun alkhairin,itakam tana dauka kawai shashanci ne irin na mutane,don bataga alamu a yadda aliyyun yake da baqar zuciya,zai iya wani abun arziqin da zai farantawa wani rai ba.
*************
Kamar da wasa kuwa wata washegarin ta gama wankewa hajja qananun kayanta ta fito ta falo,tana tsaye gaban tv taji kamar muryar hindatu tana magana,da alama yaran gidansu ne da yau gaba dayan 'yan mazan da matasan abba babba ya raba musu gyaran flowers da farfajiyar gidan,tunda an yiwa wanda yake musu wannan hidimar rasuwa,ya tafi qauye.
Aje remote din tayi tana tafa hannu cikin mamaki da jin dadi
"Na zaci zancanki ne kawai fa da kika ce zaki zo" itama tana murmushin tace
"Kin taba ganin na saba alaqawari" kai ta girgiza tace
"Ina sara miki ta wannan sashen ai".
Sai data gabatar mata da ruwa da lemo sannan ta yiwa hajja magana ta fito suka gaisa,ba wannan bane zuwanta gidan na farko ba,ta taba zuwa sau daya,wannan ne na biyu,hindatun ta jima sosai suna hira,don a nan taci abincin rana ma,sannan ta kira jannah batula nadiya da farida suka hada kira na bai daya suka sha hira har zuwa sanda akayi sallar la'asar,ta shiga nan bandakin zahra din ta daura alwala.
Tana saman abun sallar zata tayar kenan ta waiwayo ta dubi zahra
"Yauma fa na sake ganin yayankunnan,ya hakimce saman kujera qafa daya saman daya yana karatun jarida,duka yaran kowa cikin hankalinsa yake aikinsa ba hayaniya da alama shike gadinsu,bakiga yadda tsare gidan da yayi yayi masa kyau ba"hindatu ta fada,kallonta zahra tayi
"Wanne fa?,ya musty ko ya shamsu?"
"A'ah fa....sojan nan....wallahi nikam idanuna basu taba ganin namijin da yamin kwarjini,ya kuma burgeni,na kuma ji na shirya aurensa ba irinsa....don Allah qawata ki shigemin gaba mana" ta fada cikin karyar da murya.