Sashe 15
Alqibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dukkaninsu suna tsaye gaban motocin gidansu,wanda kaso mafi yawa na 'yan gidan nasu sunzo mata,ciki harda hajja,bata da wasu kaya masu yawa da zata koma dasu,don kusan duk ta kyautar dasu,kamar su katifarta botiki house wear dinta da sauran tarkacenta ciki harda jakar goyo ga wadanda basu da qarfi,yau jinta take kamar wadda aka 'yanta daga kurkuku,kana kallon fuskarta zaka shaida hakan.
Cikin yaran da sukayi sabo dasu suke kuma mata kallon yayarsu ta qaraso tana cewa
"Anty fatima.....ance anason magana dake" ta fada tana nuno wata mota,daga kai tayi ta kalli motar,babu kowa kusa da ita,hakan yasa ta tambaya waye?
"Wai mamar qawarki ce"
"Mamar qawata?" Ta maimaita cikin mamaki,kafin tasan amsar da zata bada hajja tace
"Yi maza kije ki dawo kuzo mu wuce kada muyi rana a hanya" saita waiwaya ta cewa salma tazo ta rakata,suka jera tare har zuwa jikin motar.
Suna tsaiwa aka bude murfin motar aka fito,kallo daya tayi masa ta shaidashi,saurayin dazu ne,wanda yaketa faman binta da kallo,sanye cikin shadda dinkin zamani,kanshi babu hula,kallo daya zaka masa kasa cewa wayayyen mutum ne,wanda ilimin zamani ya rasashi,da murmushi yake dubanta
"Ayimin afuwa,nayi qarya da maman qawarki ko?,naga alamun idan ba hakan nayi ba babu lallai na samu ganinki,mai yiwuwa ma nayi asarar dama ta" itadai batace komai ba sai dubanshi da take,gami da son jin ba'asin kiranta,ganin kamar yana bata musu lokaci yasa ta tambayeshi kai tsaye
"Allah dai yasa lafiya,ko yarinyar tayi batan kan wadda kasa a kira ma?,don mi bansanka ba" murmushi ya saki yana dubanta
"Ni na sanki,tun ba yau ba,saidai kuma yau din idanuna suka fara ganinki" bata fahimci zancansa ba,kuma taga alamar kamar yana son maida zancan wasa ya kuma bata mata lokaci,don haka tace
"Zaifi kyau ka fadi saqonka,don na bar iyayena na jira" gyara tsaiwarsa yayi
"A'ah,aiko ba za'ayi haka ba,ya zamu barsu mama na jiranmu?,inaga kawai ki bani lambar wayarki sai muyi magana"
"Baka da abin cewa,don haka sai anjima" ta fada tana yin gaba.
Ga tsammaninta salma na biye da ita,amma tana waiwayawa saita taras acan ta barota,dan tsaiwa tayi har salman ta iskota,cikin hade rai tace
"Ki tabbatar da cewa ba number wayata kika bashi ba" dariya salman tayi
"To meye amfaninta idan ba'a bashi ba,kika san inda rana zata fadi?,kika sani ma ko shine mijin da kiketa jira Allah ya kawoshi yanzu,indai hakane ai kinga yazo a dai dai,za'ayi aurenmu kamar yadda aka tsara" baki zahran ta tabe
"Ke kuma daga ganin sarkin fawa sai miya tayi zaqi?,to ba girin girin ba tayi mai dai" dariya ta sakeyi
"Zatayi mai lunqui ma kuwa in sha Allah,don shi yace kinyi masa,hakan kuma da kikayi babu komai,don tun ganin farko daya miki yace yaga alamun me ajice dama" tsaki kawai zahran taja,don ita sam abun ya fara barin kanta,tana ga hutu take buqata da kuma samun space sosai da zata hutawa zuciya da qwaqwalwarta.............11
*OUM DUFAIL!!*
_GIDAN ADO ƘAWA DA KECE RAINI_💄💅🏽
_OUM DUFAIL ta tanadar muku dukkan nau'in kayayyakin gyaran fata gashi dama jiki gaba daya ZAHIRINKI DA BAƊININKI samfurin MAIDA TSOHUWA YARINYA_
*kayayyakinmu sune kamar haka*
FACE AND BODY SCRUB=2500(300ml)
Face and body mango butter=3k (250ml)
Face cream= 1800
Corretor oil/vitamin C oil=2k
Fairness skin lotion= 2500
Hot chocolate skin lotion 2500
Serum (for Nuckles )2k
Nuckles cream (stubborn)3500
Mix fruits Arabian black =soap 1800
Mix fruit glycerine soap =1900
Beetroot=1900
Coconut, milk,egg..face soap=1200
Lavender mix fruit soap =1800
Body wash =1500
cleanser=1600
Hair spray =700
Hair oil =1500
Hair relaxer =700
Hair butter 1700
Shampoo =1500
Breast=oil 2k powder 2k
Strech marks cream= 2k
Beetroot pink lips =700
Baby care soap glycerine=1k
Baby care butter =1500
Shea butter baby soap =700
Tsumin tula =2200
Tsumin zinariya =1200
Sliming tea =1500
Amarya set =25k
Liquid Arabian black soap =1900
Cleansing water =1500
*Ku dubamu a handle namu na Facebook da Instagram*
Ummu Dufail
*ko ta number wayarmu kamar haka*
07067943479
*_muna turawa kowacce jaha dake fadin nigeria da yardar Allah_*
*_INGANCI DA RAHUSA SHINE TAKENMU_*🤞🏾🤞🏾🤞🏾
_____________________________
Tunda ta koma gida ibrahim ya samu nayi,kiran safe daban rana daban dare daban,har sai da duk wanda yake tare da ita yasan da xaman ibrahim din,tun tana sharewa itama har ta soma dagawa dole tana saurarensa.
Ibrahim din irin samarin nan ne 'yan hira,ya iya labarai kala daban daban,sau tari koda ba zatayi magana ba zaice babu komai,yau shi zai mata hira,zata tsaya tana saurarensa yanata bata labarai kala kala,saidai kawai tayi murmushi idan wani abun ya bata dariya,haka zasu kwashe kusan awa guda,saidai tace ta gaji.
Ya gaya mata wasu daga cikin abubuwan da suka shafeshi,sunansa da aikinsa da unguwarsu,saidai ita din banda sunanta bata gaya masa komai a kanta ba,don gaba daya komai ya fice mata akai,bata jin wani karsashi akan lamarin sam,shima kuma saita lura bai fiya tambayarta personal abubuwan da suka shafi rayuwarta ba.
Cikin haka maganar auren yammatan ta taso,an soma da kawo kudin hafsat da yasira,naira dubu hamsin hamsin kowaccensu,aka saka rana kamar yadda aka tsara za'a tsaida rana guda daya.
A daren ranar su abba suka kirata,kira na farko tsakaninsu tunda aka fara zancan aurensun.
Tunda ta shiga falon taga zaki a ciki sai taji kamar ta koma,batason ana tattauna personal issues dinta a gabanshi ko kadan,harta shiga ta zauna ta gaida abba babban dashi bai daga kai ya dubeta ba,itama tafison hakan,da da hali ma fiddashi zatayi daga falon.
Cikin nuna kulawa abban yace
"Mamana....nayi magana da hajja,ta shaida min akwai wanda yanzu kuke tare dashi ibrahim ko?" Kai ta gyada idanunta suna kallon qasa
"Eh abba"
"To ma sha Allah,yanzu abinda za'ayi shine,ki shaida masa cewa muna son ganinsa,ya kamata kuma ya turo magabantansa,tunda maganar auren 'yan uwanki ya taso,sai a hada gaba daya"kanta a qasa tace
"To abba".
A hanya tana tafe tana tunani,hakanan sam maganar ibrahim bata kwanta mata a rai ba,amma babu yadda zatayi,ba zataso ace duka sa'anninta kowa babu shi ba saura ita kadai a gidan.
Tana shiga daki saiga kiranshi,ta dauka tana zaman gefan katifa suka fara magana,kafin takai ga gaya masa nata saqon yace
"Baby....ya kamata ace mun soma ganin juna fa,yin waya a iya waya kawai abun ya isa,ya kamata mu canza tsari....a ina zan ganki?"
"A gidanmu.....akwai maganar dama da nakeso muyi dakai" cikin 'yar dariya dariya mai kama da murmushi yace
"Ah haba.....ai yanzu an daina wannan yayin,haduwa a gida kamar zamanin da,mudai samu wani waje haka,wanda zamu sake sosai,mu mori soyayyarmu da lokacinmu,inda babu abinda zai dinga razanamu" sosai mamaki ya kama zahra,amma saita danne mamakin nata tace
"Razana kuma kamar wasu marasa gaskiya?" Ta fada sound din muryarta yana sauyawa
"Eh mana,kinsan ita soyayya tana buqatar kebewa da nutsuwa" tsaf ta fahimta inda ya dosa,kuma bata taba tsammatar hakan daga gareshi ba,don haka ta kaurara muryarta sosai
"Ina jin baka shiryawa ganina na ba,a qa'idar gidanmu duk wanda keson ganinmu zai samemu cikin gidanmu ne,idan ka shirya zuwa saina gaya maka saqon gaba daya" daga haka ta katse wayar,ta koma da baya ta kwanta tana nazarin kalamansa,ba shakka ya bata mamaki,saidai kuma ba zata yanke masa hukunci haka da wuri ba,tunda wannan shine karon farko da hakan ta faru.
Ga mamakinta zancan ya wuce,sai gashi bai haqura dayi mata maganar inda zasu hadun ba,harda bata list na sunayen guraren shaqatawa yace ta zabi duk wanda takeso a ciki.
Yanzu ya daina bata mamaki saima tsoro,randa ta gaji da jin zancan ta buda baki cikin bacin rai tace masa
"Ibrahim,wannan maganar da kake yawan gayamin itace take tabbatar min da cewa ba sona kake ba!" Cikin dirircewa yace
"Hana baby....ki daina fadar haka,waye yace miki bana sonki,kinsan yadda nake jinki a zuciyata kuwa?"
"Ban gani a qasa ba,idan ka damu dani....idan har sona kake da gaskiya ka tako kazo ka riskeni gaban mahaifana mana,baka dinga neman kebewa dani a wani waje da babu idon naka ko nawa ba!" ta fada da zafinta
"Shikenan,is ok" shima ya fada cikin sanyin murya ganin yadda ta dauki zafi
"Allah ya baki haquri,yanzu ki gayamin saqon da kika ce tun rannan an baki"
"Ance na gaya maka cewa ka fito"
"Na fito ina?" Ya fada da wani irin sauti
"Aure mana" ta fada itama kai tsaye tana sauraren amsar da zata fito ta gaba daga bakinsa,don tuni ta gama hasashen amsarsa ta qarshe
"Ok...ok...am really sorry,sai yanzu na fahimta" sai kuma yayi cool da muryarsa sosai
"To ai baby shi yasa nakeson mudan hadun,mu fahimta juna kafin akai ga batun aure,tunda kinsan shi batun aure ba qaramar magana bace,zamane na dindindin,kinga dole saimun fahimci juna face to face tukunna" shuru tayi kawai,wani abu mai tauri yana tokare mata wuya,abun akwai zallar rainin hankali da ban mamaki,ada kullum shine bashi da zance saina aurensu,amma a yanzu tazo da batun yana neman noqewa.
Tun daga ranar saiya zamana bashi da zance saina gini yakeson ya fara,mota yakeson ya canza,yanzu kasuwa babu ciniki komai ya zamana sai a slow,gininsa ko linter baikai ba,ga hada lefe da sauransu,kullum cikin qorafin ya fada financial crisis iri iri.
Tuni tayi masa aji sukutum da guda ga ajjiyeshi,gefe guda kuma shirye shiryen biki ake a gidan haiqan,kowanne sashe suna nasu shirin,itama bata zauna ba,ta shiga anayin komai da ita,don 'yan uwanta ne da bata da tamkarsu.
Wannan karon umminta da kanta ta kirata ta mata magana akan ibrahim,abinda bata taba yi ba akanta kenan
"Ki tayani da addu'a" shine amsar da zahran ta baiwa ummin nata,domin tasan abun babu dadi,koda itace kuwa,sun taso tare,karatu da komai tare,amma dukka sauran zasu tafi su bar diyarta?,duk da kasancewarta mutum mai yawan haquri da yarda da qadddara,tana da yawan ibada,abinda yasa take da wata nutsuwa ta musamman kenan
"Addu'a kullum cikinta muke,saidai aci gaba,ubangiji yayi zabi mafi alkhairi" abinda tace mata kenan ba tare data nuna damuwa ko a fuskarta ba.
*_ALƘIBLARSU |||_*🚶🏾♀️🚶🏾♀️🚶🏾♀️
Ana gab da sallar magariba suka dawo daga kai dinkunansu na biki,wanda ta hada dana hajja ummint ilham harda nata duka takai musu zoo road,kasancewar duka duka bikin sati biyar ya rage.
A gajiye libis take,saboda sun dan sha tafiya a qafa kafin su samu abin hawa,saboda yau ana wahalar abun hawa wanda batasan dalilin da ya kawo hakan ba.
Cikin yaran da sukayi sabo dasu suke kuma mata kallon yayarsu ta qaraso tana cewa
"Anty fatima.....ance anason magana dake" ta fada tana nuno wata mota,daga kai tayi ta kalli motar,babu kowa kusa da ita,hakan yasa ta tambaya waye?
"Wai mamar qawarki ce"
"Mamar qawata?" Ta maimaita cikin mamaki,kafin tasan amsar da zata bada hajja tace
"Yi maza kije ki dawo kuzo mu wuce kada muyi rana a hanya" saita waiwaya ta cewa salma tazo ta rakata,suka jera tare har zuwa jikin motar.
Suna tsaiwa aka bude murfin motar aka fito,kallo daya tayi masa ta shaidashi,saurayin dazu ne,wanda yaketa faman binta da kallo,sanye cikin shadda dinkin zamani,kanshi babu hula,kallo daya zaka masa kasa cewa wayayyen mutum ne,wanda ilimin zamani ya rasashi,da murmushi yake dubanta
"Ayimin afuwa,nayi qarya da maman qawarki ko?,naga alamun idan ba hakan nayi ba babu lallai na samu ganinki,mai yiwuwa ma nayi asarar dama ta" itadai batace komai ba sai dubanshi da take,gami da son jin ba'asin kiranta,ganin kamar yana bata musu lokaci yasa ta tambayeshi kai tsaye
"Allah dai yasa lafiya,ko yarinyar tayi batan kan wadda kasa a kira ma?,don mi bansanka ba" murmushi ya saki yana dubanta
"Ni na sanki,tun ba yau ba,saidai kuma yau din idanuna suka fara ganinki" bata fahimci zancansa ba,kuma taga alamar kamar yana son maida zancan wasa ya kuma bata mata lokaci,don haka tace
"Zaifi kyau ka fadi saqonka,don na bar iyayena na jira" gyara tsaiwarsa yayi
"A'ah,aiko ba za'ayi haka ba,ya zamu barsu mama na jiranmu?,inaga kawai ki bani lambar wayarki sai muyi magana"
"Baka da abin cewa,don haka sai anjima" ta fada tana yin gaba.
Ga tsammaninta salma na biye da ita,amma tana waiwayawa saita taras acan ta barota,dan tsaiwa tayi har salman ta iskota,cikin hade rai tace
"Ki tabbatar da cewa ba number wayata kika bashi ba" dariya salman tayi
"To meye amfaninta idan ba'a bashi ba,kika san inda rana zata fadi?,kika sani ma ko shine mijin da kiketa jira Allah ya kawoshi yanzu,indai hakane ai kinga yazo a dai dai,za'ayi aurenmu kamar yadda aka tsara" baki zahran ta tabe
"Ke kuma daga ganin sarkin fawa sai miya tayi zaqi?,to ba girin girin ba tayi mai dai" dariya ta sakeyi
"Zatayi mai lunqui ma kuwa in sha Allah,don shi yace kinyi masa,hakan kuma da kikayi babu komai,don tun ganin farko daya miki yace yaga alamun me ajice dama" tsaki kawai zahran taja,don ita sam abun ya fara barin kanta,tana ga hutu take buqata da kuma samun space sosai da zata hutawa zuciya da qwaqwalwarta.............11
*OUM DUFAIL!!*
_GIDAN ADO ƘAWA DA KECE RAINI_💄💅🏽
_OUM DUFAIL ta tanadar muku dukkan nau'in kayayyakin gyaran fata gashi dama jiki gaba daya ZAHIRINKI DA BAƊININKI samfurin MAIDA TSOHUWA YARINYA_
*kayayyakinmu sune kamar haka*
FACE AND BODY SCRUB=2500(300ml)
Face and body mango butter=3k (250ml)
Face cream= 1800
Corretor oil/vitamin C oil=2k
Fairness skin lotion= 2500
Hot chocolate skin lotion 2500
Serum (for Nuckles )2k
Nuckles cream (stubborn)3500
Mix fruits Arabian black =soap 1800
Mix fruit glycerine soap =1900
Beetroot=1900
Coconut, milk,egg..face soap=1200
Lavender mix fruit soap =1800
Body wash =1500
cleanser=1600
Hair spray =700
Hair oil =1500
Hair relaxer =700
Hair butter 1700
Shampoo =1500
Breast=oil 2k powder 2k
Strech marks cream= 2k
Beetroot pink lips =700
Baby care soap glycerine=1k
Baby care butter =1500
Shea butter baby soap =700
Tsumin tula =2200
Tsumin zinariya =1200
Sliming tea =1500
Amarya set =25k
Liquid Arabian black soap =1900
Cleansing water =1500
*Ku dubamu a handle namu na Facebook da Instagram*
Ummu Dufail
*ko ta number wayarmu kamar haka*
07067943479
*_muna turawa kowacce jaha dake fadin nigeria da yardar Allah_*
*_INGANCI DA RAHUSA SHINE TAKENMU_*🤞🏾🤞🏾🤞🏾
_____________________________
Tunda ta koma gida ibrahim ya samu nayi,kiran safe daban rana daban dare daban,har sai da duk wanda yake tare da ita yasan da xaman ibrahim din,tun tana sharewa itama har ta soma dagawa dole tana saurarensa.
Ibrahim din irin samarin nan ne 'yan hira,ya iya labarai kala daban daban,sau tari koda ba zatayi magana ba zaice babu komai,yau shi zai mata hira,zata tsaya tana saurarensa yanata bata labarai kala kala,saidai kawai tayi murmushi idan wani abun ya bata dariya,haka zasu kwashe kusan awa guda,saidai tace ta gaji.
Ya gaya mata wasu daga cikin abubuwan da suka shafeshi,sunansa da aikinsa da unguwarsu,saidai ita din banda sunanta bata gaya masa komai a kanta ba,don gaba daya komai ya fice mata akai,bata jin wani karsashi akan lamarin sam,shima kuma saita lura bai fiya tambayarta personal abubuwan da suka shafi rayuwarta ba.
Cikin haka maganar auren yammatan ta taso,an soma da kawo kudin hafsat da yasira,naira dubu hamsin hamsin kowaccensu,aka saka rana kamar yadda aka tsara za'a tsaida rana guda daya.
A daren ranar su abba suka kirata,kira na farko tsakaninsu tunda aka fara zancan aurensun.
Tunda ta shiga falon taga zaki a ciki sai taji kamar ta koma,batason ana tattauna personal issues dinta a gabanshi ko kadan,harta shiga ta zauna ta gaida abba babban dashi bai daga kai ya dubeta ba,itama tafison hakan,da da hali ma fiddashi zatayi daga falon.
Cikin nuna kulawa abban yace
"Mamana....nayi magana da hajja,ta shaida min akwai wanda yanzu kuke tare dashi ibrahim ko?" Kai ta gyada idanunta suna kallon qasa
"Eh abba"
"To ma sha Allah,yanzu abinda za'ayi shine,ki shaida masa cewa muna son ganinsa,ya kamata kuma ya turo magabantansa,tunda maganar auren 'yan uwanki ya taso,sai a hada gaba daya"kanta a qasa tace
"To abba".
A hanya tana tafe tana tunani,hakanan sam maganar ibrahim bata kwanta mata a rai ba,amma babu yadda zatayi,ba zataso ace duka sa'anninta kowa babu shi ba saura ita kadai a gidan.
Tana shiga daki saiga kiranshi,ta dauka tana zaman gefan katifa suka fara magana,kafin takai ga gaya masa nata saqon yace
"Baby....ya kamata ace mun soma ganin juna fa,yin waya a iya waya kawai abun ya isa,ya kamata mu canza tsari....a ina zan ganki?"
"A gidanmu.....akwai maganar dama da nakeso muyi dakai" cikin 'yar dariya dariya mai kama da murmushi yace
"Ah haba.....ai yanzu an daina wannan yayin,haduwa a gida kamar zamanin da,mudai samu wani waje haka,wanda zamu sake sosai,mu mori soyayyarmu da lokacinmu,inda babu abinda zai dinga razanamu" sosai mamaki ya kama zahra,amma saita danne mamakin nata tace
"Razana kuma kamar wasu marasa gaskiya?" Ta fada sound din muryarta yana sauyawa
"Eh mana,kinsan ita soyayya tana buqatar kebewa da nutsuwa" tsaf ta fahimta inda ya dosa,kuma bata taba tsammatar hakan daga gareshi ba,don haka ta kaurara muryarta sosai
"Ina jin baka shiryawa ganina na ba,a qa'idar gidanmu duk wanda keson ganinmu zai samemu cikin gidanmu ne,idan ka shirya zuwa saina gaya maka saqon gaba daya" daga haka ta katse wayar,ta koma da baya ta kwanta tana nazarin kalamansa,ba shakka ya bata mamaki,saidai kuma ba zata yanke masa hukunci haka da wuri ba,tunda wannan shine karon farko da hakan ta faru.
Ga mamakinta zancan ya wuce,sai gashi bai haqura dayi mata maganar inda zasu hadun ba,harda bata list na sunayen guraren shaqatawa yace ta zabi duk wanda takeso a ciki.
Yanzu ya daina bata mamaki saima tsoro,randa ta gaji da jin zancan ta buda baki cikin bacin rai tace masa
"Ibrahim,wannan maganar da kake yawan gayamin itace take tabbatar min da cewa ba sona kake ba!" Cikin dirircewa yace
"Hana baby....ki daina fadar haka,waye yace miki bana sonki,kinsan yadda nake jinki a zuciyata kuwa?"
"Ban gani a qasa ba,idan ka damu dani....idan har sona kake da gaskiya ka tako kazo ka riskeni gaban mahaifana mana,baka dinga neman kebewa dani a wani waje da babu idon naka ko nawa ba!" ta fada da zafinta
"Shikenan,is ok" shima ya fada cikin sanyin murya ganin yadda ta dauki zafi
"Allah ya baki haquri,yanzu ki gayamin saqon da kika ce tun rannan an baki"
"Ance na gaya maka cewa ka fito"
"Na fito ina?" Ya fada da wani irin sauti
"Aure mana" ta fada itama kai tsaye tana sauraren amsar da zata fito ta gaba daga bakinsa,don tuni ta gama hasashen amsarsa ta qarshe
"Ok...ok...am really sorry,sai yanzu na fahimta" sai kuma yayi cool da muryarsa sosai
"To ai baby shi yasa nakeson mudan hadun,mu fahimta juna kafin akai ga batun aure,tunda kinsan shi batun aure ba qaramar magana bace,zamane na dindindin,kinga dole saimun fahimci juna face to face tukunna" shuru tayi kawai,wani abu mai tauri yana tokare mata wuya,abun akwai zallar rainin hankali da ban mamaki,ada kullum shine bashi da zance saina aurensu,amma a yanzu tazo da batun yana neman noqewa.
Tun daga ranar saiya zamana bashi da zance saina gini yakeson ya fara,mota yakeson ya canza,yanzu kasuwa babu ciniki komai ya zamana sai a slow,gininsa ko linter baikai ba,ga hada lefe da sauransu,kullum cikin qorafin ya fada financial crisis iri iri.
Tuni tayi masa aji sukutum da guda ga ajjiyeshi,gefe guda kuma shirye shiryen biki ake a gidan haiqan,kowanne sashe suna nasu shirin,itama bata zauna ba,ta shiga anayin komai da ita,don 'yan uwanta ne da bata da tamkarsu.
Wannan karon umminta da kanta ta kirata ta mata magana akan ibrahim,abinda bata taba yi ba akanta kenan
"Ki tayani da addu'a" shine amsar da zahran ta baiwa ummin nata,domin tasan abun babu dadi,koda itace kuwa,sun taso tare,karatu da komai tare,amma dukka sauran zasu tafi su bar diyarta?,duk da kasancewarta mutum mai yawan haquri da yarda da qadddara,tana da yawan ibada,abinda yasa take da wata nutsuwa ta musamman kenan
"Addu'a kullum cikinta muke,saidai aci gaba,ubangiji yayi zabi mafi alkhairi" abinda tace mata kenan ba tare data nuna damuwa ko a fuskarta ba.
*_ALƘIBLARSU |||_*🚶🏾♀️🚶🏾♀️🚶🏾♀️
Ana gab da sallar magariba suka dawo daga kai dinkunansu na biki,wanda ta hada dana hajja ummint ilham harda nata duka takai musu zoo road,kasancewar duka duka bikin sati biyar ya rage.
A gajiye libis take,saboda sun dan sha tafiya a qafa kafin su samu abin hawa,saboda yau ana wahalar abun hawa wanda batasan dalilin da ya kawo hakan ba.