Sashe 49
Alqibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A hankali ya dinga ganin motsinta na daxu cikin idanunsa,ba tare daya ankara ba zuciyarsa ta soma zayyano masa irin abubuwan da yake buqata tare da mace,kowanne tana haska masa shi cikin idanunsa,yana kaucewa da qarfin tsiya tare da qaryata kanshi da kanshi,ya dinga jan tsaki shi daya yana kokawa da tunanin.
Da hanzarinta batare da tsammanin akwai wani a kitchen din ba ta shigo,saita zabura zata koma da baya,daidai sanda suka hada idanu,saita tsaya cak na wasu sakanni,sanda taga ya dauke idanunsa ta fara shigowa ciki don ta wuce,zuciyarta na wani irin bugawa da yaqi daidaita.
Sake daga idanunsa yayi karo na biyu yana kallonta ta qasan idanu,kallon da idan duba daya kayi masa ba zaka zaci ita yake kallo ba,saika dauka a lumshe idanunsa suke,dab da zata giftashi tace
"Ina kwana" ya amsa qasan maqoshinsa.
Ji take kamar zata harde ta fadi,jikinta yana gaya mata akwai idanu a kanta,kamar ta zuqo qofar ficewa daga falon ta fice gaba daya,saidai kash!,dab da zata fita taji muryarsa a dake yana cewa
"Zo nan" haka kawai ya tsinci kansa da fadin hakan ba tare daya shirya ba,sai yaji baiso ta fice ne kawai,kamar tace masa zata qarasa daki ta dauka hijabi,to amma batasan me zaya fassara hakan ba,don haka ta sake juyowa ta dawo zuwa inda yake,dukka idanunsa na kanta da salon kallon qasa qasa mai kama da me bacci
"Hadamin breakfast" ya furta yana sake kurbar tea din hannunsa,ta zaci fita zayayi ya bata waje,sai taga ya matsa gefe kawai abinsa yana ci gaba da shan tea dinsa,daga qarshe ma sai yaja kujera yayi zamansa cikin kitchen din,sannu sannu kansa tsaye yaci gaba da binta da kallo duk motsin da zatayi.
Gaba daya duk sai ta rude ta daburce,sabida wani irin tasiri da idanunsa ke mata cikin jikinta,jikinta duka rawa yake,gani take kaman ba ya zakinsu ba,tun da can idan ya tsareka da idanunsa saika gwammace ya dakeka akan kallonsa mai nauyi,wani irin kwarjini ne cikin idanunsa,batasan me yasa ya tsareta haka da kallo ba,don haka duk aikin da zatayi saita dinga yinsa kwan gaba kwan baya.
Ta bangaren haidar kuwa haka kawai ya samu kansa da nazarinta,tun daga halitta zuwa yanayin aiki,shi kansa baisan nazarin na meye ba,amma ya kasa dainawa ko hana kanshi,har zuwa lokacin data sanya hannu zata sauke prying pan,wanda sam ta manta da ya kamata tasa wani tsumma ko safar hannu ta kitchen dake rataye kafin ta sauke din,sai ta saka hannun nata kawai kai tsaye.
Cikin tsananin jin zafi ta saki prying pan din tana sakin qara,abinda ke ciki ya tarwatse,radadi da zugi ya soma ratsata,ta fara yarfe hannunta.
Cikin sauri ya iso wajen kamar qiftawar idanu,yasa qafarsa da sauri ya ture frying pan din wanda saura kadan ta sanya qafarta still,hannun nata ya kama da sauri yana dubawa,tuni qwalla ta fara cika mata idanu saboda zafi,tuni yatsun sunyi ja,sai yajata suka isa bakin famfo ya kunna ya tara hannun a qasan ruwan dake zuba,a hankali sanyin ruwan ya fara ratsata,radadin ya tafi,saita lumshe idanu tana sakin ajiyar zuciya,dai dai lokacin da yake kallon fuskarta da lamsassun idanunta ke a rufe har yanzu.
Abinda bata so yawan kusancinsu,duk sanda yayi kusa da ita sosai haka takanji wani nauyi daga gangar jikinta har zuciyarta,sai taji kamar ya cika wajen da kwarjininsa da haibarsa,bugun zuciyarta yakan dadu,jiki da zuciyarta yayi wani laushi,ba zata iya fayyace me takeji game dashi ba,saidai ta sani cewa ya rage jin haushi da tsanarsa tun ranar bikin qara musu girma,maimakon haushinsa sai bugun zuciya da jin nauyinsa daya maye gurbi,haka kawai taji wani rauni na mamayarta,hakan ya baiwa qwalla damar ratsowa ta gefen idanunta.
A lokacin yana tsaye yana qarewa fuskarta kallo,yaga wasu abubuwa sama fuskarta da suke kama da nashi,wanda ko qannensa da suka fito ciki daya basuyi tarayya wajen kamanceceniya a su ba,a baya sanda take qarama idan aka fadi akwai kamannin,yana kallon mai fadar ne a matsayin me matsalar gani da kyau,amma a yanzu a dai dai wannan lokacin ya yarda kai tsaye babu musu.
Yatsunsa biyu ya saka a hankali ya dauke qwallar dake fitowa din
"Raguwa....kuka kikewa ciwon?,haka kikewa hajja?" Yaji ba zato ya fada,ita kanta sai data bude idanunta da gashin idanun suka jiqe da hawaye ta dubeshi mamaki fal qasan ranta,suna hada idanu ya janye idonsa kamar bashi ne yayi maganar ba,saiya saka hannu ya kashe famfon,ya jawo hannun saitin bakinsa ya soma karanta mata fatiha babu adadi yana tofa mata,daga ita har shi babu wani me cewa komai,sai hada idanu da sukanyi lokaci zuwa lokaci.33
Karo na qarshe da suka hada idanun saiya saki hannun nata,yaja mata kujera ya mata nuni da idanu kan ta zauna a kai,a sanyaye kuma a hankali ta zauna din,saiya juya ya tsugunna yana tsince barin da tayi,ya gyara komai,kawai sai tagq yaci gaba da girkin
"Ya rabb..." Ta fada tana lumshe idanunta cike da zallar mamakin ya haidar din,dama zai iya amsar mata girki saboda kawai ta qone?,sauqin kaine ko ganin dama?,saboda dai su sun riga da sunsan halinsa,mai fada da kaushin hali shine tambarinsa a wajensu,bata gushe ba tana binsa da kallon mamaki har sanda ya kammala,yana juyowa suka hada ido,karon farko data ji wani abu me kama da kunya ya kamata,saboda kamata da yayi tana kallonsa,sai ya basar kawai yana riqe da plate din ya miqa mata daya,sauran kuma yayi hanyar fita dasu.
A daske a wajen take bin farantin da kallo,ya hada komai perfectly,duk da dama ta kusa gama komai din,amma shima yayi qoqari sosai,ba yunwa take ji ba,amma sai taji tana sha'awar taste dinshi,don haka ta sanya hannu ta diba takai bakinta.
Komai yayi daidai,kamar ita ta zuba seasoning din,a hankali tana ci tana ci sai gashi taci da dan yawa,ta ajjiye plate din tana duba hannunta,bai tashi ba har yanzu saidai alamun quna,hakan yayi mata dadi,tasan kuma sirrin fatihar daya dinga karanta mata ce.
Da kanshi ya dinga gayawa kansa akwai matsala,yana jin tsoron faruwar wani abu,yana ga ya kamata ya maidata gida tun baiyi abun kunya ba,abun kunyar daya tabbatar da cewa hajja saita masa tareren kaf dangi da 'yan uwa.
Bai taba yarda da zantukan abokansa ba sai yanzu,wani lokaci idan suna irin wadan nan hirarrakin da suka danganci aure,yana dauka shirmensu ne kawai da kuma batawa kai lokaci,har suna ganin ko lafiya ce baida ita?,saboda sun riga da sun saba,dai daiku ne cikin wanda zai zama soja,ya kuma kai mataki da matsayin da haidar din ke kai ba tare da yana mu'amala da mata ba ko kuma shaye shayen abubuwan maye,sai gashi shi din Allah ya tsarkake shi,ya kubutar dashi,ko sigari baya sha bare akai ga barasa da sauransu,game da mata kuwa bai ma tsaiwa ya musu wani dogon kallo,ko yayi dogon nazari a kansu da zaya dami rayuwarsa,hakan ya kawo masa sauqin al'amuransa sosai,ya kuma sake kauda masa duk wani abu game dasu,duk da yasha tsallake tarkunansu,saidai suma suna kama kansu saboda sunsan halinsa,bashi da sauqi sam.
Yana gama cin abincin yayi wanka ya fice,bai dawo ba sai gab da magariba,ganin an kusa kira saiya daura alwala kawai,da niyyar idan ya dawo yayi wanka,sannan ya leqa yaga hannun nata,ya kuma nema musu abinda zasuci,saidai yayi mamaki da yazo tafiya sallah yaga kwanuka kan dining,harta samu qarfin halin yin girki kenan.
Tana dakin taji dawowarsa,saidai bata sa sha'awar fitowa don ta gama duk abinda tasan zai maidata falon,ana kiran sallah ta shiga wanka,ta fito ta shirya cikin hight waisted skert ta shirt mai gajeran hannu wadda ta dace da skert din,ya fidda qugunta sosai tare da plate tummy dinta,gashinta ta taje sosai wanda ta tsefeshi saboda tana period,yawanci haka takeyi,saita tsefe idan zatayi wankan tsarki ta wankeshi sannan a maida mata kitso idan tana ra'ayi.
Kamar daga sama taji sallama a falonsu,saita aje comb din hannunta da take kwantar da gashin nata cikin sauri ta bude qofa ta nufi parlour din.
Dr nasreen ce a tsaye cikin ado kamar yadda take a dabi'ance,kowaccensu fuskarta qunshe da fara'a suka nufi juna cikin murna,don har zuciyarta zahra taji dadin zuwan dr nasreen din,ko banza ta debe mata kewa yau na wasu awanni.
Sai data cikata da kayan ciye ciye sannan ta dubeta cikin mamakin me yasa har yanzu bata zauna ba
"Zauna mana kinata tsaye haka?" Murmushi tayi ta girgiza kai
"Ai banga ta zama ba,dear tana waje fa a tsaye" ido zahra ta fitar
"Kai!,ya shigo mana,me yasa kuma zai tsaya a waje" kai ta girgiza tana qwalalo ido
"Ah wai....ai bazai shigo ba,yasan fa waye mai gidan nan,wannan boss din naki akwai ban tsoro,yasan halinsa sarai....,ki fara shaida masa dai yana da baqo ko?" Saita dan daburce,tana nufin ta shiga dakinsa kenan ta masa magana,tunda ta tabbatar yana dakin tunda ya dawo gidan,dakin da tunda tazo bata taba gigin shigarsa ba,batason tace wani abu da zata dago kome ke tsakaninsu,don haka cikin fara'ar yaqe tace
"Yanzu kuwa zan sanar mishi,ai ba'a bar masoyi a waje ba" tayi qarfin halin tsokanarta,sai ta sake fadada fara'arta tana cewa
"Kema kya fada,shi yasa na kasa zama ai".
Inda zai yiwu zata faki idanun nasreen ne taje ta sanyo hijabi,to amma yin hakan zai sanya ta saka mata ayar tambaya,dole qanwar naqi tayi qundunbala takuma yi shahadar quda ta durfafi dakin.
Fitowarsa daga wanka kenan daure da towel iya qugunsa,yana tsaye gaban mudubi yana sharce ruwan jikinsa,duk da cewa daga wanka ya fito kuma a tube yake amma ac ke kwarara cikin dakin,kamar baya jin yawan da tayi.
A hankali ta bude qofar dakin ta saka kai,ta daga idanunta a hankali tana wulgasu cikin dakin,saiko suka sauka a kansa yana taje kansa da wani cumb,idanunsa cikin madubin yana kallota,ko kadan bata tsammaci samunshi a yanayin data ganshi ba,yanayin qira da duk wata siffa ta jikinsa ta fito muraren,mai tsayayyen jiki da siffa dake nuna qarfi da mazantaka,da kuma alamun ya horu sosai kan aikinsa,kana ganinsa kasan yana daga qarfe.
Da hanzarinta batare da tsammanin akwai wani a kitchen din ba ta shigo,saita zabura zata koma da baya,daidai sanda suka hada idanu,saita tsaya cak na wasu sakanni,sanda taga ya dauke idanunsa ta fara shigowa ciki don ta wuce,zuciyarta na wani irin bugawa da yaqi daidaita.
Sake daga idanunsa yayi karo na biyu yana kallonta ta qasan idanu,kallon da idan duba daya kayi masa ba zaka zaci ita yake kallo ba,saika dauka a lumshe idanunsa suke,dab da zata giftashi tace
"Ina kwana" ya amsa qasan maqoshinsa.
Ji take kamar zata harde ta fadi,jikinta yana gaya mata akwai idanu a kanta,kamar ta zuqo qofar ficewa daga falon ta fice gaba daya,saidai kash!,dab da zata fita taji muryarsa a dake yana cewa
"Zo nan" haka kawai ya tsinci kansa da fadin hakan ba tare daya shirya ba,sai yaji baiso ta fice ne kawai,kamar tace masa zata qarasa daki ta dauka hijabi,to amma batasan me zaya fassara hakan ba,don haka ta sake juyowa ta dawo zuwa inda yake,dukka idanunsa na kanta da salon kallon qasa qasa mai kama da me bacci
"Hadamin breakfast" ya furta yana sake kurbar tea din hannunsa,ta zaci fita zayayi ya bata waje,sai taga ya matsa gefe kawai abinsa yana ci gaba da shan tea dinsa,daga qarshe ma sai yaja kujera yayi zamansa cikin kitchen din,sannu sannu kansa tsaye yaci gaba da binta da kallo duk motsin da zatayi.
Gaba daya duk sai ta rude ta daburce,sabida wani irin tasiri da idanunsa ke mata cikin jikinta,jikinta duka rawa yake,gani take kaman ba ya zakinsu ba,tun da can idan ya tsareka da idanunsa saika gwammace ya dakeka akan kallonsa mai nauyi,wani irin kwarjini ne cikin idanunsa,batasan me yasa ya tsareta haka da kallo ba,don haka duk aikin da zatayi saita dinga yinsa kwan gaba kwan baya.
Ta bangaren haidar kuwa haka kawai ya samu kansa da nazarinta,tun daga halitta zuwa yanayin aiki,shi kansa baisan nazarin na meye ba,amma ya kasa dainawa ko hana kanshi,har zuwa lokacin data sanya hannu zata sauke prying pan,wanda sam ta manta da ya kamata tasa wani tsumma ko safar hannu ta kitchen dake rataye kafin ta sauke din,sai ta saka hannun nata kawai kai tsaye.
Cikin tsananin jin zafi ta saki prying pan din tana sakin qara,abinda ke ciki ya tarwatse,radadi da zugi ya soma ratsata,ta fara yarfe hannunta.
Cikin sauri ya iso wajen kamar qiftawar idanu,yasa qafarsa da sauri ya ture frying pan din wanda saura kadan ta sanya qafarta still,hannun nata ya kama da sauri yana dubawa,tuni qwalla ta fara cika mata idanu saboda zafi,tuni yatsun sunyi ja,sai yajata suka isa bakin famfo ya kunna ya tara hannun a qasan ruwan dake zuba,a hankali sanyin ruwan ya fara ratsata,radadin ya tafi,saita lumshe idanu tana sakin ajiyar zuciya,dai dai lokacin da yake kallon fuskarta da lamsassun idanunta ke a rufe har yanzu.
Abinda bata so yawan kusancinsu,duk sanda yayi kusa da ita sosai haka takanji wani nauyi daga gangar jikinta har zuciyarta,sai taji kamar ya cika wajen da kwarjininsa da haibarsa,bugun zuciyarta yakan dadu,jiki da zuciyarta yayi wani laushi,ba zata iya fayyace me takeji game dashi ba,saidai ta sani cewa ya rage jin haushi da tsanarsa tun ranar bikin qara musu girma,maimakon haushinsa sai bugun zuciya da jin nauyinsa daya maye gurbi,haka kawai taji wani rauni na mamayarta,hakan ya baiwa qwalla damar ratsowa ta gefen idanunta.
A lokacin yana tsaye yana qarewa fuskarta kallo,yaga wasu abubuwa sama fuskarta da suke kama da nashi,wanda ko qannensa da suka fito ciki daya basuyi tarayya wajen kamanceceniya a su ba,a baya sanda take qarama idan aka fadi akwai kamannin,yana kallon mai fadar ne a matsayin me matsalar gani da kyau,amma a yanzu a dai dai wannan lokacin ya yarda kai tsaye babu musu.
Yatsunsa biyu ya saka a hankali ya dauke qwallar dake fitowa din
"Raguwa....kuka kikewa ciwon?,haka kikewa hajja?" Yaji ba zato ya fada,ita kanta sai data bude idanunta da gashin idanun suka jiqe da hawaye ta dubeshi mamaki fal qasan ranta,suna hada idanu ya janye idonsa kamar bashi ne yayi maganar ba,saiya saka hannu ya kashe famfon,ya jawo hannun saitin bakinsa ya soma karanta mata fatiha babu adadi yana tofa mata,daga ita har shi babu wani me cewa komai,sai hada idanu da sukanyi lokaci zuwa lokaci.33
Karo na qarshe da suka hada idanun saiya saki hannun nata,yaja mata kujera ya mata nuni da idanu kan ta zauna a kai,a sanyaye kuma a hankali ta zauna din,saiya juya ya tsugunna yana tsince barin da tayi,ya gyara komai,kawai sai tagq yaci gaba da girkin
"Ya rabb..." Ta fada tana lumshe idanunta cike da zallar mamakin ya haidar din,dama zai iya amsar mata girki saboda kawai ta qone?,sauqin kaine ko ganin dama?,saboda dai su sun riga da sunsan halinsa,mai fada da kaushin hali shine tambarinsa a wajensu,bata gushe ba tana binsa da kallon mamaki har sanda ya kammala,yana juyowa suka hada ido,karon farko data ji wani abu me kama da kunya ya kamata,saboda kamata da yayi tana kallonsa,sai ya basar kawai yana riqe da plate din ya miqa mata daya,sauran kuma yayi hanyar fita dasu.
A daske a wajen take bin farantin da kallo,ya hada komai perfectly,duk da dama ta kusa gama komai din,amma shima yayi qoqari sosai,ba yunwa take ji ba,amma sai taji tana sha'awar taste dinshi,don haka ta sanya hannu ta diba takai bakinta.
Komai yayi daidai,kamar ita ta zuba seasoning din,a hankali tana ci tana ci sai gashi taci da dan yawa,ta ajjiye plate din tana duba hannunta,bai tashi ba har yanzu saidai alamun quna,hakan yayi mata dadi,tasan kuma sirrin fatihar daya dinga karanta mata ce.
Da kanshi ya dinga gayawa kansa akwai matsala,yana jin tsoron faruwar wani abu,yana ga ya kamata ya maidata gida tun baiyi abun kunya ba,abun kunyar daya tabbatar da cewa hajja saita masa tareren kaf dangi da 'yan uwa.
Bai taba yarda da zantukan abokansa ba sai yanzu,wani lokaci idan suna irin wadan nan hirarrakin da suka danganci aure,yana dauka shirmensu ne kawai da kuma batawa kai lokaci,har suna ganin ko lafiya ce baida ita?,saboda sun riga da sun saba,dai daiku ne cikin wanda zai zama soja,ya kuma kai mataki da matsayin da haidar din ke kai ba tare da yana mu'amala da mata ba ko kuma shaye shayen abubuwan maye,sai gashi shi din Allah ya tsarkake shi,ya kubutar dashi,ko sigari baya sha bare akai ga barasa da sauransu,game da mata kuwa bai ma tsaiwa ya musu wani dogon kallo,ko yayi dogon nazari a kansu da zaya dami rayuwarsa,hakan ya kawo masa sauqin al'amuransa sosai,ya kuma sake kauda masa duk wani abu game dasu,duk da yasha tsallake tarkunansu,saidai suma suna kama kansu saboda sunsan halinsa,bashi da sauqi sam.
Yana gama cin abincin yayi wanka ya fice,bai dawo ba sai gab da magariba,ganin an kusa kira saiya daura alwala kawai,da niyyar idan ya dawo yayi wanka,sannan ya leqa yaga hannun nata,ya kuma nema musu abinda zasuci,saidai yayi mamaki da yazo tafiya sallah yaga kwanuka kan dining,harta samu qarfin halin yin girki kenan.
Tana dakin taji dawowarsa,saidai bata sa sha'awar fitowa don ta gama duk abinda tasan zai maidata falon,ana kiran sallah ta shiga wanka,ta fito ta shirya cikin hight waisted skert ta shirt mai gajeran hannu wadda ta dace da skert din,ya fidda qugunta sosai tare da plate tummy dinta,gashinta ta taje sosai wanda ta tsefeshi saboda tana period,yawanci haka takeyi,saita tsefe idan zatayi wankan tsarki ta wankeshi sannan a maida mata kitso idan tana ra'ayi.
Kamar daga sama taji sallama a falonsu,saita aje comb din hannunta da take kwantar da gashin nata cikin sauri ta bude qofa ta nufi parlour din.
Dr nasreen ce a tsaye cikin ado kamar yadda take a dabi'ance,kowaccensu fuskarta qunshe da fara'a suka nufi juna cikin murna,don har zuciyarta zahra taji dadin zuwan dr nasreen din,ko banza ta debe mata kewa yau na wasu awanni.
Sai data cikata da kayan ciye ciye sannan ta dubeta cikin mamakin me yasa har yanzu bata zauna ba
"Zauna mana kinata tsaye haka?" Murmushi tayi ta girgiza kai
"Ai banga ta zama ba,dear tana waje fa a tsaye" ido zahra ta fitar
"Kai!,ya shigo mana,me yasa kuma zai tsaya a waje" kai ta girgiza tana qwalalo ido
"Ah wai....ai bazai shigo ba,yasan fa waye mai gidan nan,wannan boss din naki akwai ban tsoro,yasan halinsa sarai....,ki fara shaida masa dai yana da baqo ko?" Saita dan daburce,tana nufin ta shiga dakinsa kenan ta masa magana,tunda ta tabbatar yana dakin tunda ya dawo gidan,dakin da tunda tazo bata taba gigin shigarsa ba,batason tace wani abu da zata dago kome ke tsakaninsu,don haka cikin fara'ar yaqe tace
"Yanzu kuwa zan sanar mishi,ai ba'a bar masoyi a waje ba" tayi qarfin halin tsokanarta,sai ta sake fadada fara'arta tana cewa
"Kema kya fada,shi yasa na kasa zama ai".
Inda zai yiwu zata faki idanun nasreen ne taje ta sanyo hijabi,to amma yin hakan zai sanya ta saka mata ayar tambaya,dole qanwar naqi tayi qundunbala takuma yi shahadar quda ta durfafi dakin.
Fitowarsa daga wanka kenan daure da towel iya qugunsa,yana tsaye gaban mudubi yana sharce ruwan jikinsa,duk da cewa daga wanka ya fito kuma a tube yake amma ac ke kwarara cikin dakin,kamar baya jin yawan da tayi.
A hankali ta bude qofar dakin ta saka kai,ta daga idanunta a hankali tana wulgasu cikin dakin,saiko suka sauka a kansa yana taje kansa da wani cumb,idanunsa cikin madubin yana kallota,ko kadan bata tsammaci samunshi a yanayin data ganshi ba,yanayin qira da duk wata siffa ta jikinsa ta fito muraren,mai tsayayyen jiki da siffa dake nuna qarfi da mazantaka,da kuma alamun ya horu sosai kan aikinsa,kana ganinsa kasan yana daga qarfe.