Sashe 4
Alqibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sanye yake da wata farar riga ƙal me gajeran hannu,wanda hakan ya baiwa murɗaɗɗen dantsensa damar bayyana,sai dogon wando shima fari gamida wani farin booth dake qafarsa,daga inda kake wucewa kana iya jiyo qamshin lallausan turarensa da iska ke kwasowa tana bazashi ko ina,ba kayan dazun bane a jikinsa,da alamu ma wanka yaje ya sake ya sauyasu saboda miyar data batashi,waya yake amsawa,kallo daya zaka masa kasan cewa yes!,aikin da yake yayi matuqar dacewa dashi,ko shafawa kayi kasan cewa shi din SOJA NE.
ƙasa ƙasa zahra taja tsaki cikin ranta
"Da wannan kayan yafi kamata ma ace jikinsa ya ɓaci dazu naga ta qaryar gayu da ƙyanƙyami" ta qarashe maganar tana fitar da tsakinta a sarari dai dai sanda ta hangi ya musty na qarasawa inda yake tsayen bayan ya baro wajen me gadi wanda da alama wani saqo ya bashi.
Suna gab da rabuwa kowa ta shige sashensu ba tare da sun ankara ba sukaji muryar ya musty na nufosu yana fadin
"Yaa haidar na magana fa 'yammata" dukkansu babu wadda cikinta bai murɗa mata ba,yusra da tafi kowa tsoro cikinsu cikin rawar murya tace
"Wa yake kira a cikinmu?"
"Dukanku" ya bata amsa yana qunshe dariyarsa,don basu ba,hatta su da suke maza ba kasafai kiran haidar ke musu daɗi ba.
Junansu suka kalla,yusra ta sake cewa cikin qas qas da murya don kada ya jisu
"Amma me kuma muka yi masa ya musty don Allah?"
"Idan kunzo kwaji" daga haka shima ya juya abinsa don kada yayi laifi.
"Kome zai mana ai bazai rabamu da numfashinmu ba ko?,kuzo muje" inji hafsat qanwarsa wadda suke uwa daya uba daya,zahra ko tabe baki tayi,duk da cewa ita dinma a tsorace take,haka suka nufeshi sum sum kamar waɗanda suka ɗauko gawa.
Gaba daya su bakwai din suka zube gabanshi,yayin dashi kuma ke tsaye abinsa yana latsa waya kamar baisan An haliccesu wajen ba.
Saida suka tsammaci ya manta dasu a wajen,sannan ya buda baki kamar wani saraki ya jefo musu tambaya yana ci gaba da latsa wayarsa
"Wace inna wuro a cikinku?" Tambayar duk saita zo musu wani banbarakwai,tunda sunsan dai duk wanda ya kwana ya tashi cikin gidan ya san me sunan,hakan yasa suka kasa amsashi suka hau kallon kallo.
[9/6, 6:12 PM] Anty Rabi'at: *KIJI TSORON ALLAH,KARKI TABA KAYAN DABA NAKI BANE,BA MALLAKARKI BANE*
02
Falon yanzu babu kowa duka sun yoye sai ya hajjan kawai,tana zaune tana gyara falle fallen littafin dala'ilu,da alama ta karantasu ne suka kuma hargitse mata take gyarawa,don ita din har tsufanta bai hanata bibiyar litattafan addini ba.
Ta baya ta rungumeta tana cewa
"Ashe dai har yanzu ana yi dani 'yar tsohuwa mai ran qarfe,bari naje na dawo na kwashi gara,Allah dai ya jiqan tsohon mijinki" daga haka ta juya cikin sassarfa tana barin falon.
Wannan karonma da kallo ya hajjan ta bita,cikin ranta ta amsa addu'ar data yiwa mijinta kuma masoyinta,tana jin yarinyar cikin ranta sosai fiyr da sauran jikokinta,su biyu kacal suka samu irin wannan babban matsayin,duk da qoqarin boyewa da take da kuma nuna duka dai dai suke.
Tana yawan godiya ga Allah daya sanya qauna da zumunci mai qarfi tsakanin ahalinta,tun daga kan yaranta zuwa jikokinta,tsabar son su zamaTsintsiya madaurinki daya ya sanya tun mijinta na raye suka yanke zaman dukka yaransu maza tattare a waje daya,matanne basu da wannan ikon ko qarfin a kansu,hakan kuma yayi tasiri wajen sake maida zuri'ar tata tsintsiya madaurinki daya,duk da ance zaman tare zo mu zauna zo mu saba,hakanan baka rasa banbancin halaye da ra'ayi wanda kan kawo sabani lokaci zuwa lokaci,saidai a nata ahalin akwai qarancin hakan sosai,don bazai yiwu ace babu ba,kusan halayya ce tadan adam,kuma sunna ce ta zaman tare.
Duk da wannan babban abinda ke bata mamaki da daure mata kai shine rashin jituwar dake tsakanin zahran da yayanta,kusan abune daya dauko dogon tarihi ya kuma samo asali da tushe tun da dadewa,tun abun bai zama wani abun damuwa kallo ko dubayya ba har takai a yanzun yana damunta lokaci zuwa lokaci,saidai tana saka ran watarana komai zai zama tarihi,kamar akwai sauran quruciya ne jikin xahran.
Sashen yayan mahaifinta da suke kira da abba babba ta fara shiga,sashe ne mai kyau kamar yadda ainihin ginin gidan ya nuna,babban falo wanda ya cinye set din kujeru har guda biyu,dakuna a qasa kitchen da bandaki,sai dakunan matan gidan dake sama,duk da kowacce tana da guda daya a qasa.
Mommy ta tadda a falon ,wanda ke mazaunin amaryar abba babba tana cirewa yara da dawowarsu gidan kenan unifoarm,wanda dukkansu yaran gidan suna makaranta guda ne,akan daukosu tare a kuma kaisu tare,bisa jagorancin drivern gidan a wadatacciyar motar da aka ware musu don wannan hidimar.
Kanta ta daga tana amsa sallamarta sanda take cirewa yaronta safarshi,fuskarta fadade da fara'a tace
"Maraba da 'yan boarding" qarasowa tayi tana murmushi,ta zauna hannun kujerar tana amsawa gami da yiwa mus'ab da ake cirewa safa tsiya
"Wai kai bakasan ka girma bane,saura kadan kayi shekara goma fa,amma har yanzu safa ake cire ma"
"Murmushi mommy ta saki
"Kema kya fada inna wuro,kullum sai an cire masa kamar yaron goye..." Dariya ta sakeyi tana kuma dan tsokanarsa kafin daga bisani ta juya tana gaida mommyn,fuska a sake take amsata,ta tambayi abba babba
"Abbanku ai kinsan ba zama,tun sassafe ya fita kasuwa"
"Mama fa?" (Uwar gidan mommy)
"Yau suna hidima ne,ita dinma tun dazu ta fice" jin haka yasa ta miqe tana zura hannu a aljihun rigarta,ta soma zaro alawa masu dan girma tana rabawa wadanda ta taras a falon,duk data girmesu amma ba wani girma ne me yawa can ba,shekarun data basun bazai gaza biyu zuwa uku ba,idan yayi yawa hudu
"Baki gajiya,keda kika dawo daga makaranta harda wata tsaraba" murmushi kawai ta yiwa mummyn tana ficewa.
Sashe na biyu ta shiga,sassan abba yusuf,wanda keda matan aure biyu shima da yara tara,amarya nada uku,uwargidan nada shida,shima dai kamar shigen ginin waccan sashen,komai cikin tsari,da alama kusan dabi'ar jama'ar gidan ce wato tsafta,su dinma faran faran suka gaisa ta wuce sashen abba abu wanda cikakken sunanshi shine abubakar,matarshi daya da yara bakwai,sai abban tsakiya shima matarshi daya,daga nan sai sashen mahaifinta.
Sashe ne dake da girma da qima a idanunta,yake kuma da dimbin tarihi cikin rayuwarta,sashen da a shekarun naya suka rayu kamar sauran sassa dake gidan,cikin walwala farinciki da qaunar juna,qarqashin inuwar adalin uba kuma mahaifi a wajenta,saidai ta farat daya mai rabawa ta raba mai raba soyayyar iyaye da 'ya yansu wato mutuwa,a lokacin da suke tsaka da gudanar da rayuwarsu.
Mahaifinta uba ne da ya zama daya tamkar da dubu,wanda bashi yiwuwa ta manta soyayyarshi garesu,musamman ita din da take 'yar fari a wajensa,ta kuma ci sunan mahaifiyarsa,saiya zamana soyayya da kulawar da yake bata ta dabance,har kullum mutuwarshi sabuwa ce a ranta,rana da lokacin basu taba bace mata ba daga idanunta.
A hankali tayi sallama cikin falon,qannenta dake xaune suna cin abincin rana suka amsa,cikin farinciki qauna irin ta 'yan uwantaka suka miqe suna mata oyoyo,fuskarta washe da fara'a take amsa musu,wanda hayaniyarsu ta fito da mahaifiyarta dake kitchen.
Kyakkyawar mace mai kyan zubi da haiba,ma'abociyar tsafta nutsuwa da kyakkyawar dabi'a,wanda kyawun dabi'arta ya sanya koda bayan rasuwar mai gidanta dangin mijinta suka kasa rabuwa da ita,suka roqi alfarma taci gaba da xama dasu har zuwa sanda xata buqaci aure,su kuma zasu tsaya mata tamkar nata dangin.
Duk da cewa bata rasa wani gata ko kulawa daga nata dangin ba,amma hakan bai hanata amsar tayinsu ba,saboda tsantsar dattako irin na uwar mijinta,da yadda ta nuna mata qauna da kulawa tun haduwarsu har xuwa yau din,bugu da qari kuma,bata jin xata iya sake aure a sauran rayuwarta data rage,tunda ta rasa miji daya tamkar da dubu irin sa'id uban 'ya'yanta.
A nutse ta qarasa daura da inda mahaifiyar tata ke zaune
"Ina wuni ummi"
"Lafiya qalau,ya makaranta ya kuka barosu"
"Lafiya lau ummi,wannan karon duka babu dadi,ni kadai aka bari a makaranta,yasira ta rigani dawowa" tana zare carbin hannunta ta amsa
"Eh ai jikin nata alhmdlh da sauqi,jiya na shiga na dubata" ajiyar zuciya tadan saki
"Tana raina ummi,gobe in sha Allahu nima zanje na dubata"
"Ya kamata kuwa,don dazu yaayan ma ya kirani yace an daukoki ko?"
"Eh su ya musty ne ma suka je a motar wancan mutumin" sosai ummin nata ta tsareta da idanu tana kallonta,sai a sannan ga gane tabargazar data tafka,saita dauke nata idanun tana son wayancewa
"Inna wuro?,waye wancan mutumin?,yayan naku?,ashe qara lalacewa kike?,duk fadan da nake miki bakiji kenan?" Marairaice mata tayi,don idan da sabo ta saba da fada daga wajen ummin indai a kanshi ne,abu na qarshe kuma data fi tsana kenan a rayuwarta
"Kiyi haquri ummi,mantawa nayi,bazan sake ba" kanta ta dauke kawai daga gareta,tasan ta fada ne kawai,amma wannan halayyar ta jima dason rabata da ita amma ta kasa,ta zame mata jiki,rabuwa da ita sai a hankali,bata tashi daga wajen ba sai data ji tace
"Allah ya kyauta,Allah ya rabaki da wannan halin".
Dakinta dake sashen wanda ba kasafai ta fiya kwana a ciki ba ta wuce,tsaf yake kamar ko yaushe,duk da bata kwana ciki amma kullum saita gyarashi,'yar madaidaiciyat cupboard dinta ta bude,ta zabi kayan sawa adadin wanda takeso,ta debi kayan kwalliya mayafanta da sauran muhimman abubuwa don maidasu sassan hajja,saboda muddin ta dawo hutu tafi xama a can,bama ita kadai ba duka 'yammatan gidan dakin dake sashen hajjan suke tarewa har sai ta koma.
Ita dinma tafison zaman can din,saboda tafi sakewa sosai fiye da sassansu,hajjan na barinta tayi yadda takeso koma bayan ummin nata dake da tsauri da kuma dokoki iri iri.
Kai tsaye ta koma sassan hajjan,duka sun fice da alama kowacce akwai abinda zatayi,hakan ya mata itama saboda wanka takesonyi ta kuma rama bashin baccin da batayi ba daren jiya a makaranta,don su kwana waqe waqe na murnar tafiya gida hutu,gabanin asuba koma kowa ya shiga sabgarsa taci gaba da hada kayansa da kuma bin layin wanka.
Sai data fara zuwa gun wayarta dake chargy,hopefully ta taba screen din ya kawo haske cikin zumudi,don ta tabbatar zata iske texs ko miscal na nuraddeen kamar yadda ya saba mata a kullum idan ta dawo hutu.
Saidai kuma ga tarin mamakinta babu kiran hakanan babu saqon nashi,sosai abun ya daure mata kai,amma saita bashi uzuri,ta shiga ta duba balance dinta.
ƙasa ƙasa zahra taja tsaki cikin ranta
"Da wannan kayan yafi kamata ma ace jikinsa ya ɓaci dazu naga ta qaryar gayu da ƙyanƙyami" ta qarashe maganar tana fitar da tsakinta a sarari dai dai sanda ta hangi ya musty na qarasawa inda yake tsayen bayan ya baro wajen me gadi wanda da alama wani saqo ya bashi.
Suna gab da rabuwa kowa ta shige sashensu ba tare da sun ankara ba sukaji muryar ya musty na nufosu yana fadin
"Yaa haidar na magana fa 'yammata" dukkansu babu wadda cikinta bai murɗa mata ba,yusra da tafi kowa tsoro cikinsu cikin rawar murya tace
"Wa yake kira a cikinmu?"
"Dukanku" ya bata amsa yana qunshe dariyarsa,don basu ba,hatta su da suke maza ba kasafai kiran haidar ke musu daɗi ba.
Junansu suka kalla,yusra ta sake cewa cikin qas qas da murya don kada ya jisu
"Amma me kuma muka yi masa ya musty don Allah?"
"Idan kunzo kwaji" daga haka shima ya juya abinsa don kada yayi laifi.
"Kome zai mana ai bazai rabamu da numfashinmu ba ko?,kuzo muje" inji hafsat qanwarsa wadda suke uwa daya uba daya,zahra ko tabe baki tayi,duk da cewa ita dinma a tsorace take,haka suka nufeshi sum sum kamar waɗanda suka ɗauko gawa.
Gaba daya su bakwai din suka zube gabanshi,yayin dashi kuma ke tsaye abinsa yana latsa waya kamar baisan An haliccesu wajen ba.
Saida suka tsammaci ya manta dasu a wajen,sannan ya buda baki kamar wani saraki ya jefo musu tambaya yana ci gaba da latsa wayarsa
"Wace inna wuro a cikinku?" Tambayar duk saita zo musu wani banbarakwai,tunda sunsan dai duk wanda ya kwana ya tashi cikin gidan ya san me sunan,hakan yasa suka kasa amsashi suka hau kallon kallo.
[9/6, 6:12 PM] Anty Rabi'at: *KIJI TSORON ALLAH,KARKI TABA KAYAN DABA NAKI BANE,BA MALLAKARKI BANE*
02
Falon yanzu babu kowa duka sun yoye sai ya hajjan kawai,tana zaune tana gyara falle fallen littafin dala'ilu,da alama ta karantasu ne suka kuma hargitse mata take gyarawa,don ita din har tsufanta bai hanata bibiyar litattafan addini ba.
Ta baya ta rungumeta tana cewa
"Ashe dai har yanzu ana yi dani 'yar tsohuwa mai ran qarfe,bari naje na dawo na kwashi gara,Allah dai ya jiqan tsohon mijinki" daga haka ta juya cikin sassarfa tana barin falon.
Wannan karonma da kallo ya hajjan ta bita,cikin ranta ta amsa addu'ar data yiwa mijinta kuma masoyinta,tana jin yarinyar cikin ranta sosai fiyr da sauran jikokinta,su biyu kacal suka samu irin wannan babban matsayin,duk da qoqarin boyewa da take da kuma nuna duka dai dai suke.
Tana yawan godiya ga Allah daya sanya qauna da zumunci mai qarfi tsakanin ahalinta,tun daga kan yaranta zuwa jikokinta,tsabar son su zamaTsintsiya madaurinki daya ya sanya tun mijinta na raye suka yanke zaman dukka yaransu maza tattare a waje daya,matanne basu da wannan ikon ko qarfin a kansu,hakan kuma yayi tasiri wajen sake maida zuri'ar tata tsintsiya madaurinki daya,duk da ance zaman tare zo mu zauna zo mu saba,hakanan baka rasa banbancin halaye da ra'ayi wanda kan kawo sabani lokaci zuwa lokaci,saidai a nata ahalin akwai qarancin hakan sosai,don bazai yiwu ace babu ba,kusan halayya ce tadan adam,kuma sunna ce ta zaman tare.
Duk da wannan babban abinda ke bata mamaki da daure mata kai shine rashin jituwar dake tsakanin zahran da yayanta,kusan abune daya dauko dogon tarihi ya kuma samo asali da tushe tun da dadewa,tun abun bai zama wani abun damuwa kallo ko dubayya ba har takai a yanzun yana damunta lokaci zuwa lokaci,saidai tana saka ran watarana komai zai zama tarihi,kamar akwai sauran quruciya ne jikin xahran.
Sashen yayan mahaifinta da suke kira da abba babba ta fara shiga,sashe ne mai kyau kamar yadda ainihin ginin gidan ya nuna,babban falo wanda ya cinye set din kujeru har guda biyu,dakuna a qasa kitchen da bandaki,sai dakunan matan gidan dake sama,duk da kowacce tana da guda daya a qasa.
Mommy ta tadda a falon ,wanda ke mazaunin amaryar abba babba tana cirewa yara da dawowarsu gidan kenan unifoarm,wanda dukkansu yaran gidan suna makaranta guda ne,akan daukosu tare a kuma kaisu tare,bisa jagorancin drivern gidan a wadatacciyar motar da aka ware musu don wannan hidimar.
Kanta ta daga tana amsa sallamarta sanda take cirewa yaronta safarshi,fuskarta fadade da fara'a tace
"Maraba da 'yan boarding" qarasowa tayi tana murmushi,ta zauna hannun kujerar tana amsawa gami da yiwa mus'ab da ake cirewa safa tsiya
"Wai kai bakasan ka girma bane,saura kadan kayi shekara goma fa,amma har yanzu safa ake cire ma"
"Murmushi mommy ta saki
"Kema kya fada inna wuro,kullum sai an cire masa kamar yaron goye..." Dariya ta sakeyi tana kuma dan tsokanarsa kafin daga bisani ta juya tana gaida mommyn,fuska a sake take amsata,ta tambayi abba babba
"Abbanku ai kinsan ba zama,tun sassafe ya fita kasuwa"
"Mama fa?" (Uwar gidan mommy)
"Yau suna hidima ne,ita dinma tun dazu ta fice" jin haka yasa ta miqe tana zura hannu a aljihun rigarta,ta soma zaro alawa masu dan girma tana rabawa wadanda ta taras a falon,duk data girmesu amma ba wani girma ne me yawa can ba,shekarun data basun bazai gaza biyu zuwa uku ba,idan yayi yawa hudu
"Baki gajiya,keda kika dawo daga makaranta harda wata tsaraba" murmushi kawai ta yiwa mummyn tana ficewa.
Sashe na biyu ta shiga,sassan abba yusuf,wanda keda matan aure biyu shima da yara tara,amarya nada uku,uwargidan nada shida,shima dai kamar shigen ginin waccan sashen,komai cikin tsari,da alama kusan dabi'ar jama'ar gidan ce wato tsafta,su dinma faran faran suka gaisa ta wuce sashen abba abu wanda cikakken sunanshi shine abubakar,matarshi daya da yara bakwai,sai abban tsakiya shima matarshi daya,daga nan sai sashen mahaifinta.
Sashe ne dake da girma da qima a idanunta,yake kuma da dimbin tarihi cikin rayuwarta,sashen da a shekarun naya suka rayu kamar sauran sassa dake gidan,cikin walwala farinciki da qaunar juna,qarqashin inuwar adalin uba kuma mahaifi a wajenta,saidai ta farat daya mai rabawa ta raba mai raba soyayyar iyaye da 'ya yansu wato mutuwa,a lokacin da suke tsaka da gudanar da rayuwarsu.
Mahaifinta uba ne da ya zama daya tamkar da dubu,wanda bashi yiwuwa ta manta soyayyarshi garesu,musamman ita din da take 'yar fari a wajensa,ta kuma ci sunan mahaifiyarsa,saiya zamana soyayya da kulawar da yake bata ta dabance,har kullum mutuwarshi sabuwa ce a ranta,rana da lokacin basu taba bace mata ba daga idanunta.
A hankali tayi sallama cikin falon,qannenta dake xaune suna cin abincin rana suka amsa,cikin farinciki qauna irin ta 'yan uwantaka suka miqe suna mata oyoyo,fuskarta washe da fara'a take amsa musu,wanda hayaniyarsu ta fito da mahaifiyarta dake kitchen.
Kyakkyawar mace mai kyan zubi da haiba,ma'abociyar tsafta nutsuwa da kyakkyawar dabi'a,wanda kyawun dabi'arta ya sanya koda bayan rasuwar mai gidanta dangin mijinta suka kasa rabuwa da ita,suka roqi alfarma taci gaba da xama dasu har zuwa sanda xata buqaci aure,su kuma zasu tsaya mata tamkar nata dangin.
Duk da cewa bata rasa wani gata ko kulawa daga nata dangin ba,amma hakan bai hanata amsar tayinsu ba,saboda tsantsar dattako irin na uwar mijinta,da yadda ta nuna mata qauna da kulawa tun haduwarsu har xuwa yau din,bugu da qari kuma,bata jin xata iya sake aure a sauran rayuwarta data rage,tunda ta rasa miji daya tamkar da dubu irin sa'id uban 'ya'yanta.
A nutse ta qarasa daura da inda mahaifiyar tata ke zaune
"Ina wuni ummi"
"Lafiya qalau,ya makaranta ya kuka barosu"
"Lafiya lau ummi,wannan karon duka babu dadi,ni kadai aka bari a makaranta,yasira ta rigani dawowa" tana zare carbin hannunta ta amsa
"Eh ai jikin nata alhmdlh da sauqi,jiya na shiga na dubata" ajiyar zuciya tadan saki
"Tana raina ummi,gobe in sha Allahu nima zanje na dubata"
"Ya kamata kuwa,don dazu yaayan ma ya kirani yace an daukoki ko?"
"Eh su ya musty ne ma suka je a motar wancan mutumin" sosai ummin nata ta tsareta da idanu tana kallonta,sai a sannan ga gane tabargazar data tafka,saita dauke nata idanun tana son wayancewa
"Inna wuro?,waye wancan mutumin?,yayan naku?,ashe qara lalacewa kike?,duk fadan da nake miki bakiji kenan?" Marairaice mata tayi,don idan da sabo ta saba da fada daga wajen ummin indai a kanshi ne,abu na qarshe kuma data fi tsana kenan a rayuwarta
"Kiyi haquri ummi,mantawa nayi,bazan sake ba" kanta ta dauke kawai daga gareta,tasan ta fada ne kawai,amma wannan halayyar ta jima dason rabata da ita amma ta kasa,ta zame mata jiki,rabuwa da ita sai a hankali,bata tashi daga wajen ba sai data ji tace
"Allah ya kyauta,Allah ya rabaki da wannan halin".
Dakinta dake sashen wanda ba kasafai ta fiya kwana a ciki ba ta wuce,tsaf yake kamar ko yaushe,duk da bata kwana ciki amma kullum saita gyarashi,'yar madaidaiciyat cupboard dinta ta bude,ta zabi kayan sawa adadin wanda takeso,ta debi kayan kwalliya mayafanta da sauran muhimman abubuwa don maidasu sassan hajja,saboda muddin ta dawo hutu tafi xama a can,bama ita kadai ba duka 'yammatan gidan dakin dake sashen hajjan suke tarewa har sai ta koma.
Ita dinma tafison zaman can din,saboda tafi sakewa sosai fiye da sassansu,hajjan na barinta tayi yadda takeso koma bayan ummin nata dake da tsauri da kuma dokoki iri iri.
Kai tsaye ta koma sassan hajjan,duka sun fice da alama kowacce akwai abinda zatayi,hakan ya mata itama saboda wanka takesonyi ta kuma rama bashin baccin da batayi ba daren jiya a makaranta,don su kwana waqe waqe na murnar tafiya gida hutu,gabanin asuba koma kowa ya shiga sabgarsa taci gaba da hada kayansa da kuma bin layin wanka.
Sai data fara zuwa gun wayarta dake chargy,hopefully ta taba screen din ya kawo haske cikin zumudi,don ta tabbatar zata iske texs ko miscal na nuraddeen kamar yadda ya saba mata a kullum idan ta dawo hutu.
Saidai kuma ga tarin mamakinta babu kiran hakanan babu saqon nashi,sosai abun ya daure mata kai,amma saita bashi uzuri,ta shiga ta duba balance dinta.