Sashe 22
Alqibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Kallo daya ta yiwa sawwaman tasan cewa lallai tasha kuka itama ba na wasa ba,gaba daya idanunta sun tasa har lebunanta,zahran ta qarasa a hankali ta zauna gefan sawwaman
"Ashe kema kinsan abdulyasar?" Kai ta iya jinjinawa kawai ba tare da tace komai ba,saboda wano ciwo dake taso mata a qirji
"Ashe bani kadai bace?....bani kadai ya yiwa haka ba?" Maganar da taja hankalin zahra kenan da ta daga kai ta dubi sawwaman,kallon da take mata yake nuna tana da buqatar qarin bayani
"Abdul yayimin alqawarin aure....infact ma yau sati daya da tura magabatansa gidanmu,amma abun mamaki sai nakejin yau sati biyu dakai kudinsa wajen wata walida....baya ga haka ashe kema...." Hannu ta dagawa sawwama murmushin takaici na fita daga fuskar zahran,a take wasu kalamai da abdul din yake yawan gaya mata suka dinga dawo mata aka tar kamar a sannan yake furta mata su
"Duk duniya akwai wata bayan ke?,duk duniya akwai wata diya mace data isa ta rabani dake?,me kike fargaba a kaina?,akwai wata mace data isa na bata lokacina akanta na tafi zance wajenta idan bake ba.....zahra duk kyan mace....duk ajinta....duk gayunta saidai tabi bayanki"
"Duk abinda kika fada haka ne....hakane sawwama" kuka sawwaman ta fashe dashi,wanda da alama zallar baqinciki da bacin rai yake cin zuciyarta
"Abdul ya cuceni,ya zalunceni...abdul..." Da sauri hajja data fito tace
"Kiy shuru karki sake cewa komai,kuyi haquri ku masa addu'ar Allah ya yafe masa kuskuren daya tafka" miqewa zahra tayi ta koma daki don ba zata iya ci gaba da tattauna wannan maganar ba,hajja da hafsat sune suka sallami sawwama.
A ranar ko kusa ko alama bacci bai gitta ta ba bare ya samu nasarar daukarta ba,duk juyin da zatayin abdul din take tunawa,kalamansa da salon yadda yaso sabuleta daga rayuwarta ta wata siga mai masifar ciwo,shima so yayi yayi mata irin yadda nasir da nuraddeen sukayi mata?,so yayi ya karya mata zuciya?,yayi gutsi gutsi da ita?,don ta tabbatar a yadda ta bawa soyayyar abdulyasar amanna da Allah ya barshi da ransa hakan ya faru babu tantama zata iya rasa lafiyar zuciya,saita goge hawayenta ta miqe ta zauna tana gayawa kanta,wala'alla Allah ne ya sota da rahama ya daukeshi,ubangiji baiyi zataga wannan baqinciki da bacin ran da tashin hankalin ba,amma lallai ta yanke tsammani,hakanan ta debe haso daga dukkan lamarin maza,abun ba qarami bane,sha'aninsu ya wuce tunaninta.
Kwanyarta tana iya tuna mata sanda abdulyasar din yake musanyan waya da ita,ya aje mata wayarsa yacw ta bashi tata aga wanda yafi gaskiya a cikinsu,aga wanda saurayi ko budurwa zasu kira,ashe a sannan wala'alla sabon layi kenan yake sakawa?,ko layin da ba'a sanshi dashi ba?.
Sannan tana iya tuna sanda yakan rufeta da masifa cikin zallar kishi,yana cin alwashin duk randa yaga wani ya kulata ko ta tsaya dashi,ba shakka saiya masa diban karen mahaukaciya ya sadashi da qasa ya take wuyansa,kome zai faru indai a kanta ne saidai ya faru,tana iya tuna sanda yake tsaidata ya rakata makaranta ko wani guri da kansa,tana iya tuna sanda fafur ya hanata shiga kasuwa,ashe duk bogi ce?,qarya ce?,ashe bayan ita hadda sawwama wadda yakai magabatansa?,anya ko magabatan gaske ne bana haya bane?,anya kuwa bana bogi bane?,saboda babu iyayen arziqin da zasuje maka maganar aure wannan satin,wani satin kuma suje maka gidan su wata da saninsu,to bayan ita da sawwama mata nawa ya yaudara?,wannan Allah ne kawai masani.
Cikin daren ta yiwa kanta da kanta fada,ta gayawa kanta cewa da batasan abdulyasar ba,kafinshi kuma wasu sun yaudareta,ta kuma ci gaba da rayuwarta ba tare da komai ya sameta koya sauya ba,hakanan a yanzun ma zataci gaba da rayuwa babu shi,zata dora daga inda ta tsaya,ba zata bari damuwar wanda baisan da damuwarta ta dameta ba,damuwar wanda baya doron duniyar ma gaba daya,kai koda yana raye.....dukkan namijin da zai miki haka bai cancanci ki damu kanki saboda shi ba,saboda ya nunawa duniya cewa u r a zero behind decimal point,baki da wani amfani a tare dashi,keda babu duka daya,don me zaki damu da irin wadan nan?,me yasa irin wannan namijin zaki dora damuwarki a kanshi?,a daren,a kuma sannan ta yiwa kanta alaqawarin cire dukkan damuwar wani abun banza namijin daya yaudareta,ta kuma dasawa kanta takunkumin tserewa soyayya da kuma nisantarta bakin iyawarta,har sai taga abinda ya turewa buzu nadi,ko kuma abinda alqalamin qaddararta ya rubuta ya tabbata.
Sosai hajja tayi mamaki washegari da taga sakewa a tare da zahran,wanda sam batayi tsammamin ganin hakan tattare da ita ba,bata tanka mata ba sai taci gaba da biye mata,can qasan ranta tausayin zahran yana ratsata,duk inda ta gifta sai ta bita da kallo,haqiqa ta hadu da jarrabawa mai tsauri da wahala,amma kullum fatanta ya zama nasara ce a rayuwarta.
A irin hakan zahran ta lura da kallon da hajjan ke mata,ta fahimceta sarai,amma sai tayi murmushi
"Wai ya kiketa kallona tsohuwa?,kodai na miki kyau ne?" Kai hajjan ta gyada sannan tace
"Ina miki fata da addu'ar wannan ya zama karonki na qarshe da zaki sake fuskantar qalubale irin wannan kaf rayuwarki" saita rausayar dakai kawai,cikin zuciyarta tana amsa da amin.
Wannan karon ma umminta kasa jurewa tayi sai data titsiyeta
"Innawuro.....ki gayamin gaskiya idan akwai wani abu a qasa...."
"Wallahi ummi bansan komai ba,bansan meke faruwa ba" shuru ummin ta danyi na wasu mintina,sannan a sanyaye tace
"Kin tabbatar ba saida musu mutuncinki kike ba?" Sosai maganar tayi ma ummin kanta nauyi da zahran,saidai ya zamana dole ta yiwa zahran wannan tambayar,saboda uwa bai kamata a muhallin irin wannan da kike bincike da qwaqwwafi ba ki dinga boye wasu maganganun,wai don kawai kunya da nauyinsu,kan zahran a qasa tana fitar da qwalla tace
"Allah ya tsareni ummi,ubangiji ya tsare miki ni,kuma har abada bana fatan ya bani ikon ko damar da zata sanya nayi fatali da tarbiyyar da kuka gine ni a kanta,wallahi wallahi koda tunanin aikata hakan bai taba zuwa kaina ba bare na aikata ummi,ki yarda da 'yarki" nannauyar ajiyar zuciya ta sauke
"Na yarda dake.....ba kuma wai ina zarginki bane,amma ya zama dole nayi aikina na uwa na bincika da kyau,na tabbatar addu'ar da kullum ba dare ba rana da nake miki keda 'yar uwarki dama sauran dukkan yaran dake gidan nan ba zata fadi qasa banza ba,na yarda jarabtace kamar yadda take rubuce a rayuwar kowanne musulmi.....kici gaba da addu'a,kada dimuwa ko zafin jarrabawa yasa ki kasa cin ribar haqurinki....karbi wannan" ta fada taba miqa mata wata doguwar takarda,addu'o'ine a rubuce a cikinta,addu'o'i ingantattu masu ma'ana,wanda suke dauke da kalmomi masu girma da tsarki gami da kambama ubangiji,wadanda su kadai sun isa sanya nutsuwa a zuciyar bawa da samun biyan buqata daga wajen ubangijin talikai.
Godiya ta yiwa ummin sannan ta baro sashen,tun a ranar sata soma addu'o'in ta dinga jin sukuni da nutsuwa yana ratsata,ta sake jin zuciyarta wasai kuma fes,haqiqa ubangiji yayi gaskiya da yace ku saurara,da ambaton Allah kawai zukata suke samun nutsuwa,lallai babu abinda yakai ambaton ubangiji sanya nutsuwa a zuciyar mai damuwa.
Cikin satin ta hada kayanta ta koma bakin karatunta,tunda komai ya daidaita an koma makaranta,ta kuma fuskanci karatunta da kyau,ta watsar da duk wani damuwa da hayaniyar soyayya,babu wani da namiji da take tsaiwa ta kalla sau biyu ma bare ta saurari kalaman bakinsa,duk ta musu kudin goro gaba dayansu.
*_BAYAN WANI LOKACI_*
Zaune take cikin dakin kwanan dalibai wanda ya zama mallakinsu ita da hindatu batula da jannah,yayin da nadiya da farida suke daki daya daura da nasu suda wasu mutum biyun,to amma idan baka sani ba zaka zaci dukkansu daki guda suke,saboda kusan komai a nan dakinsu zahran sukeyi,hatta da abinci daya sukeyi,duk da basi fiya ma girma abinci ba,saidai suyo takeaway,idan kaga girkakken abinci to aikin zahra ne,sau tari sukan mata qorafin tana walahar da kanta da wani girki,ta bari kawai suyo takeaway suci,takan ce
"Ni ban saba bafa,abincin da zaka girka da kanka yafi albarka,sannan kayan anincin da nazo dasu daga gida saina jibgesu su lalace?,ko kuma na maidasu gida idan an tambayeni nace qawaye suna siya min ina ci?" To su dinma idan ta dafa kowa dafifi yake wajen ci,saboda ita din ba baya bace wajen iya girki.
Kamar yau dinma dakin nasu cike yake da hayaniyar 'yammata,kasancewar suna cikin ranakun qarshen mako ne,kuma wannan karon kusan dukkaninsu basuje gida weekend ba,ita zahra saboda CA da zasu fara,kuma a satin zasuyi kusan gudan hudu,shi yasa taga gwara ta zauna waje guda tayi karatu sosai.
Yau dinma ita ta dafa musu abincin,kowa yaci ya qoshi,da suka kammala saita taja takardunta da system dinta saman gadonta ta barsu nan tsakar dakin kan carfet din da suka malale dakin dashi
"Yar allazi boko" taji su suna tsokanarta,bata kulasu ba sai murmushi kawai datayi taci gaba da karatunta,batason ta tsaya tankasu su dauke mata hankalinta,suma sukanyi karatun,amma saidai baiko kai nata ba,sukance sun gaji basu iyawa,da sun taba iya yadda zasu iya suke ajewa su shiga sabgarsu.
"Ashe kema kinsan abdulyasar?" Kai ta iya jinjinawa kawai ba tare da tace komai ba,saboda wano ciwo dake taso mata a qirji
"Ashe bani kadai bace?....bani kadai ya yiwa haka ba?" Maganar da taja hankalin zahra kenan da ta daga kai ta dubi sawwaman,kallon da take mata yake nuna tana da buqatar qarin bayani
"Abdul yayimin alqawarin aure....infact ma yau sati daya da tura magabatansa gidanmu,amma abun mamaki sai nakejin yau sati biyu dakai kudinsa wajen wata walida....baya ga haka ashe kema...." Hannu ta dagawa sawwama murmushin takaici na fita daga fuskar zahran,a take wasu kalamai da abdul din yake yawan gaya mata suka dinga dawo mata aka tar kamar a sannan yake furta mata su
"Duk duniya akwai wata bayan ke?,duk duniya akwai wata diya mace data isa ta rabani dake?,me kike fargaba a kaina?,akwai wata mace data isa na bata lokacina akanta na tafi zance wajenta idan bake ba.....zahra duk kyan mace....duk ajinta....duk gayunta saidai tabi bayanki"
"Duk abinda kika fada haka ne....hakane sawwama" kuka sawwaman ta fashe dashi,wanda da alama zallar baqinciki da bacin rai yake cin zuciyarta
"Abdul ya cuceni,ya zalunceni...abdul..." Da sauri hajja data fito tace
"Kiy shuru karki sake cewa komai,kuyi haquri ku masa addu'ar Allah ya yafe masa kuskuren daya tafka" miqewa zahra tayi ta koma daki don ba zata iya ci gaba da tattauna wannan maganar ba,hajja da hafsat sune suka sallami sawwama.
A ranar ko kusa ko alama bacci bai gitta ta ba bare ya samu nasarar daukarta ba,duk juyin da zatayin abdul din take tunawa,kalamansa da salon yadda yaso sabuleta daga rayuwarta ta wata siga mai masifar ciwo,shima so yayi yayi mata irin yadda nasir da nuraddeen sukayi mata?,so yayi ya karya mata zuciya?,yayi gutsi gutsi da ita?,don ta tabbatar a yadda ta bawa soyayyar abdulyasar amanna da Allah ya barshi da ransa hakan ya faru babu tantama zata iya rasa lafiyar zuciya,saita goge hawayenta ta miqe ta zauna tana gayawa kanta,wala'alla Allah ne ya sota da rahama ya daukeshi,ubangiji baiyi zataga wannan baqinciki da bacin ran da tashin hankalin ba,amma lallai ta yanke tsammani,hakanan ta debe haso daga dukkan lamarin maza,abun ba qarami bane,sha'aninsu ya wuce tunaninta.
Kwanyarta tana iya tuna mata sanda abdulyasar din yake musanyan waya da ita,ya aje mata wayarsa yacw ta bashi tata aga wanda yafi gaskiya a cikinsu,aga wanda saurayi ko budurwa zasu kira,ashe a sannan wala'alla sabon layi kenan yake sakawa?,ko layin da ba'a sanshi dashi ba?.
Sannan tana iya tuna sanda yakan rufeta da masifa cikin zallar kishi,yana cin alwashin duk randa yaga wani ya kulata ko ta tsaya dashi,ba shakka saiya masa diban karen mahaukaciya ya sadashi da qasa ya take wuyansa,kome zai faru indai a kanta ne saidai ya faru,tana iya tuna sanda yake tsaidata ya rakata makaranta ko wani guri da kansa,tana iya tuna sanda fafur ya hanata shiga kasuwa,ashe duk bogi ce?,qarya ce?,ashe bayan ita hadda sawwama wadda yakai magabatansa?,anya ko magabatan gaske ne bana haya bane?,anya kuwa bana bogi bane?,saboda babu iyayen arziqin da zasuje maka maganar aure wannan satin,wani satin kuma suje maka gidan su wata da saninsu,to bayan ita da sawwama mata nawa ya yaudara?,wannan Allah ne kawai masani.
Cikin daren ta yiwa kanta da kanta fada,ta gayawa kanta cewa da batasan abdulyasar ba,kafinshi kuma wasu sun yaudareta,ta kuma ci gaba da rayuwarta ba tare da komai ya sameta koya sauya ba,hakanan a yanzun ma zataci gaba da rayuwa babu shi,zata dora daga inda ta tsaya,ba zata bari damuwar wanda baisan da damuwarta ta dameta ba,damuwar wanda baya doron duniyar ma gaba daya,kai koda yana raye.....dukkan namijin da zai miki haka bai cancanci ki damu kanki saboda shi ba,saboda ya nunawa duniya cewa u r a zero behind decimal point,baki da wani amfani a tare dashi,keda babu duka daya,don me zaki damu da irin wadan nan?,me yasa irin wannan namijin zaki dora damuwarki a kanshi?,a daren,a kuma sannan ta yiwa kanta alaqawarin cire dukkan damuwar wani abun banza namijin daya yaudareta,ta kuma dasawa kanta takunkumin tserewa soyayya da kuma nisantarta bakin iyawarta,har sai taga abinda ya turewa buzu nadi,ko kuma abinda alqalamin qaddararta ya rubuta ya tabbata.
Sosai hajja tayi mamaki washegari da taga sakewa a tare da zahran,wanda sam batayi tsammamin ganin hakan tattare da ita ba,bata tanka mata ba sai taci gaba da biye mata,can qasan ranta tausayin zahran yana ratsata,duk inda ta gifta sai ta bita da kallo,haqiqa ta hadu da jarrabawa mai tsauri da wahala,amma kullum fatanta ya zama nasara ce a rayuwarta.
A irin hakan zahran ta lura da kallon da hajjan ke mata,ta fahimceta sarai,amma sai tayi murmushi
"Wai ya kiketa kallona tsohuwa?,kodai na miki kyau ne?" Kai hajjan ta gyada sannan tace
"Ina miki fata da addu'ar wannan ya zama karonki na qarshe da zaki sake fuskantar qalubale irin wannan kaf rayuwarki" saita rausayar dakai kawai,cikin zuciyarta tana amsa da amin.
Wannan karon ma umminta kasa jurewa tayi sai data titsiyeta
"Innawuro.....ki gayamin gaskiya idan akwai wani abu a qasa...."
"Wallahi ummi bansan komai ba,bansan meke faruwa ba" shuru ummin ta danyi na wasu mintina,sannan a sanyaye tace
"Kin tabbatar ba saida musu mutuncinki kike ba?" Sosai maganar tayi ma ummin kanta nauyi da zahran,saidai ya zamana dole ta yiwa zahran wannan tambayar,saboda uwa bai kamata a muhallin irin wannan da kike bincike da qwaqwwafi ba ki dinga boye wasu maganganun,wai don kawai kunya da nauyinsu,kan zahran a qasa tana fitar da qwalla tace
"Allah ya tsareni ummi,ubangiji ya tsare miki ni,kuma har abada bana fatan ya bani ikon ko damar da zata sanya nayi fatali da tarbiyyar da kuka gine ni a kanta,wallahi wallahi koda tunanin aikata hakan bai taba zuwa kaina ba bare na aikata ummi,ki yarda da 'yarki" nannauyar ajiyar zuciya ta sauke
"Na yarda dake.....ba kuma wai ina zarginki bane,amma ya zama dole nayi aikina na uwa na bincika da kyau,na tabbatar addu'ar da kullum ba dare ba rana da nake miki keda 'yar uwarki dama sauran dukkan yaran dake gidan nan ba zata fadi qasa banza ba,na yarda jarabtace kamar yadda take rubuce a rayuwar kowanne musulmi.....kici gaba da addu'a,kada dimuwa ko zafin jarrabawa yasa ki kasa cin ribar haqurinki....karbi wannan" ta fada taba miqa mata wata doguwar takarda,addu'o'ine a rubuce a cikinta,addu'o'i ingantattu masu ma'ana,wanda suke dauke da kalmomi masu girma da tsarki gami da kambama ubangiji,wadanda su kadai sun isa sanya nutsuwa a zuciyar bawa da samun biyan buqata daga wajen ubangijin talikai.
Godiya ta yiwa ummin sannan ta baro sashen,tun a ranar sata soma addu'o'in ta dinga jin sukuni da nutsuwa yana ratsata,ta sake jin zuciyarta wasai kuma fes,haqiqa ubangiji yayi gaskiya da yace ku saurara,da ambaton Allah kawai zukata suke samun nutsuwa,lallai babu abinda yakai ambaton ubangiji sanya nutsuwa a zuciyar mai damuwa.
Cikin satin ta hada kayanta ta koma bakin karatunta,tunda komai ya daidaita an koma makaranta,ta kuma fuskanci karatunta da kyau,ta watsar da duk wani damuwa da hayaniyar soyayya,babu wani da namiji da take tsaiwa ta kalla sau biyu ma bare ta saurari kalaman bakinsa,duk ta musu kudin goro gaba dayansu.
*_BAYAN WANI LOKACI_*
Zaune take cikin dakin kwanan dalibai wanda ya zama mallakinsu ita da hindatu batula da jannah,yayin da nadiya da farida suke daki daya daura da nasu suda wasu mutum biyun,to amma idan baka sani ba zaka zaci dukkansu daki guda suke,saboda kusan komai a nan dakinsu zahran sukeyi,hatta da abinci daya sukeyi,duk da basi fiya ma girma abinci ba,saidai suyo takeaway,idan kaga girkakken abinci to aikin zahra ne,sau tari sukan mata qorafin tana walahar da kanta da wani girki,ta bari kawai suyo takeaway suci,takan ce
"Ni ban saba bafa,abincin da zaka girka da kanka yafi albarka,sannan kayan anincin da nazo dasu daga gida saina jibgesu su lalace?,ko kuma na maidasu gida idan an tambayeni nace qawaye suna siya min ina ci?" To su dinma idan ta dafa kowa dafifi yake wajen ci,saboda ita din ba baya bace wajen iya girki.
Kamar yau dinma dakin nasu cike yake da hayaniyar 'yammata,kasancewar suna cikin ranakun qarshen mako ne,kuma wannan karon kusan dukkaninsu basuje gida weekend ba,ita zahra saboda CA da zasu fara,kuma a satin zasuyi kusan gudan hudu,shi yasa taga gwara ta zauna waje guda tayi karatu sosai.
Yau dinma ita ta dafa musu abincin,kowa yaci ya qoshi,da suka kammala saita taja takardunta da system dinta saman gadonta ta barsu nan tsakar dakin kan carfet din da suka malale dakin dashi
"Yar allazi boko" taji su suna tsokanarta,bata kulasu ba sai murmushi kawai datayi taci gaba da karatunta,batason ta tsaya tankasu su dauke mata hankalinta,suma sukanyi karatun,amma saidai baiko kai nata ba,sukance sun gaji basu iyawa,da sun taba iya yadda zasu iya suke ajewa su shiga sabgarsu.