Sashe 40
Alqibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A tsaye ta samesu a falo,tana sallama umminta ta fara gani,sam batasan tazo ba,bata kuma bawa ranta zatazo din ba,saboda batajin dadi ance mata kusan sati guda kenan,duk da ita bata gaya mata ba.
Qarasawa tayi ta gaidata,sannan ta dubi salma dake riqe da jakar hajja,tana ta zuba zance ita dasu yasira wadda itama yau tazo din,duk an fito da jakankunan kayansu maman,wani sanyi ya ratsa zuciyarta,itakam dama ta gaji,so take kawai ayi a gama su wuce ko ta samu sa'ida hajja ta sakar mata mara tayi fitsari.
Data wuwwulga idanunta bata ga jakarta ba,sai tabi bayan salma data koma dauko jakar hannun hajja,ta isketa tana neman jakar a inda hajjan tace mata tana nan
"Don wulaqanci a dauki jakar kowa amma banda tawa,saboda ni bani da gata da galihu?"
"Ai an debi kayan da za'a koma miki dasu,an kawo miki wasu" duban salman tayi sanda take zuge zip din jakar
"Kamar yaya?"girarta ta daga
"Eh to....bari na tsegunta miki,kamar naji hajja tana fadin anan ke za'a barki,zaku taho tare da ya haidar ko?"
"Kambun bala'i!.....ni!,wallahi bazan zauna ba,tabdijan,ai itama hajjan ba haka mukayi da ita ba" ta fada tana jin wani tashin hankali yana ratsata,dafata salma tayi tana boye dariyarta
"Easy mana zuhra."
"Anqi easy din.....naga alama hajja wani abu daban takemin ba so ba,in banda haka ta yaya zata ce na zauna da wannan mutumin a cikin gidansa?,ya kasheni kenan akai musu gawata ko?,dama haka takeso".
"eh haka nakeso don ƙaniyarki....indai wannan shine rashin son to bana qaunarki fadi ki qara fada,ke salma tsaiwar me kikeyi ke kuma daga daukomi jaka?,miqomin driver yazo,ko mu wuce mu barki anan ki tayata zama" wani zillo salma tayi sai gata kusa da hajjan tana cewa
"Rufamin asiri kada ya zaki ya cillani ta window nayi kwanan qofar gida,a jawa yarona da mijina asara" kuka zahra ta saki harda dora hannu aka
"To wallahi nima bazan zauna ba,kowa tsoronsa yake amma haka kawai ni an hadani dashi?,saboda niba mutum bace?,idan ma cinyeni zaiyi ya cinyeni?"
"Eh haka nake nufi don gidanku,ja'irar yarinya" hajja ta sake cewa tana qwalalowa zahra idanu gamida tamke fuskarta kaman bada xahra'un tata take magana ba
"Wuce muje" ta fada tana nunawa salma hanya,tuni salman tayi gaba,tana danne dariyar dake taso mata,ita ta tseguntawa hajja cewa gobe zasuyi liyafar cin abincin dare dukka wadanda aka qarawa girma,kuma kowa da matarsa yake zuwa,idan ma akwai yara harda su,nan take hajjan tace dole haidar dinta shima asan ya zama babban mutum,dama a wajen taga idanun wata qabila yana haka haka akan jikan nata,duk inda yayi tana binsa da wani kallon yaudara na banza da wofi,tota Allah ba tataba,ba qaramin dariya akaci a motar ba da wannan ruɗu da hajjan ta hada ba,tuni itama hajja tabi bayanta,ai kuwa itama zahran saita kwashi jakarta ta rufawa hajjan baya.
Kacibus sukayi da umminta wadda ta sake shigowa ta rage mararta kada fitsari ya dameta a mota,duk sai suka ja baya,ta dubi ummin itama ummin ta dubeta,kallon da tayi mata shi ya sanyayar mata da jiki,saita tsugunna saman jakartata a wajen,ita kuma ummin ta wuce ciki abinta.
Batafi minti biyu ba ta fito,a lokacin zahran ta dawo bakin qofa ta tsuguna kamar me neman gafara ko taimako
"Kiyi duk yadda zakiyi,kiyi duk qoqarin da zakiyi ki nunawa duniya ban baki tarbiyya ba,ki nunawa duniya na sama dake basu isa dake ba,nayi imanin kaf fadin duniya idan na mutu kika laluba daga farko zuwa qarshe baki da masoyiya kamar hajja har abada,hakanan ko yanzu na mutu zan kwanta cikin kabarina hankalina kwance game da aurenki,don nasan ba zaki tozarta a hannun haidar ba,bazai taba wulaqantaki ba,ba hannun gama garin mutum kike ba,shi din na musamman ne wanda yasan da daraja da mutuncin dan adam,wanda ya kulaa ya kuma girmama rayuwar mahaifiyarki,ruwanki kiga girma da mutucinsa saboda haka,ruwanki kisa qafa ki shure.....zakiga kamar ba'a sonki,tako ina an matsa miki.....soyayya ta gaskiya itace ka tsaya tsayin daka wajen ganin naka ya gyaru kafin kowa,sannan matsalar zamantakewa a hausance sunan mace ke fara fitowa kafin na da namiji....baki da hurumin yankewa haidar hukunci sabida tsohon tunaninki na ba *ALƘIBLARKU* daya ba,akwai banbancin ra'ayi tsakaninku ko?,wannan rusashshiyar hujja ce.....a yanzu ina miki magana da harshen uwa zuwa ga diyarta......ki nutsu ki fara dora komai kan muhallinsa da saitinsa.....sai angwada ake sanin na qwarai" daga haka ummin tayi gaba abinta ba tare data waiwayo ba,ita kadai tasan me takeji a cikin zuciyarta,ita kadai tasan wanne fata ke gareta,ita kadai tasan adadin sau nawa tana hana idanunta bacci don ingantar rayuwar yaranta.
Da qyar ta tashi daga wajen ba tare data dauke jakarta data janyo wajen ba,a hankali tana jin yadda hayaniya da surutunsu keyin nesa da gidan,da alamu ficewa sukeyi,da qyar takai kanta bakin katifar ta zube,duka zantukan ummin nata sun tsaye mata kamar qusa a qahon zuci,hakanan sun kashe mata duk wani qwari na jikinta.27
Tsahon awa guda gidan ya dauki shuru,duk da lokaci zuwa lokaci tana dan jiyo motsi da maganganu sama sama daga falo zuwa kitchen,wanda ta tabbatar da ma'aikata ne.
Tun azahar take kwance bayan ta gama hawayenta son ranta ta godewa Allah,kota kan abinci bata biba,duk da karin safe ne kawai a cikinta,abu daya ke tada ita shine sallah,sai ruwa kawai data ke sha wanda shima cikin dakin yake jiya da dare suka shigo dashi basu shanye ba,haka ta dinga juyi ita kadai,har zuwa lokacin da duhun magarib ya sako kai,aka fara qwala kiran sallahr magariba,saita miqe tana jin yadda tsakiyar cikinta ya qulle,da alamu ulcer dinta tana son tashi kenan idan batayi wasa ba,hakan ya sanya sai data fara fitowa parlour ta bude fridge ta dauki fresh milk mai sanyi babban gora daya tana duban yadda falon ya koma fes,ko ina ɗas ɗas dashi yana fidda qamshi,kamar ba'a taba yin baqi ba,ba abinda ke fita sai wani samfurin qamshin freshner na musamman,ga abinci a jere a cikin tsari saman dining table,saita dauke kanta ta koma daki,ta zauna ta zuqe madarar tas sannan ta shiga bandaki,tana fitsari taji gefan mararta na qullewa
"Ya salam" ta fada,alamun period na iya zuwa anytime kenan,haka ta daura alwalarta ta dawo dakin ta tayar da sallar.
*Aliyyu Haidar*
Sosai yayi relax a bayan motar bayan ya aje hularsa a gefe yana furzar da iska daga bakinsa,yana jin yadda sanyin ac ke ratsashi tare da qara haifar masa da kasala da kuma tayar masa da gajiyarsa ta zirga zirgar wunin yau.
Zuciyarsa da qwaqwalwarsa tayi nisa wajen tuna abubuwan da suka faru yau wayarsa dake aje tare da hularsa ta dauki tsuwwa,dan qaramin tsaki yaja,ba kasafai ya fiya son kira ba,saidai yau yasha kiran har ya gode Allah,a hakama don yana kashewa ne baya amsa wani.
Ganin sunan me kiran yasa ba shiri yakai hannu ya dauka,labbansa suka motsa cikin ransa ya furta
"Rigimammiyar tsohuwa" saiya kara a kunnensa
"Badai har kunje gida ba?"
"Harma mun huta yanzu haka?"
"Ma sha Allah,sannunku da qoqari,Allah ya qara girma da nisan kwana me amfani"
"Amin ya rabbi...amin Aliyyu,Allah yayiwa rayuwa albarka"
"Amin hajja"
"Yauwa.....dama na kiraka ne na gaya maka,nabar amanar jikata a gidanka" fuska yadan yamutse yana son ya fahimci maganar tata,kamar kuwa tasan tunanin da yakeyi tace
"Matarka zahra....zaku taho tare idan ka gama abinda kake...."
"Amma hajja....bamuyi maganar ba....sannan ma kuma karatunta fa?"
"Kai da ita ku kukasan wani karatu.....,jan kunne na kiraka nayi maka,aronta na baka,bance kuma atabamin ita tun yanzu ba ehe" tun kafin takai ga kashe wayar shiya kashe,saiya jefata gefe yana dafe kansa,hajjan ta soma wuce tunaninsa,tunda harta fara masa manya manyan maganganu irin wannan,banda abinta ma shi da bashi ya nemi a barta ba su suka barta don raɗin kansu har tazo da wannan maganar,shikam wannan sabgar gada dayanta akwai qwara a cikinta.
Da ire iren wannan tunanin daya ci gaba dayi har suka isa gidan,ya fita yabar drivern yana kulle motar,yayi cikin gida,ma'aikatan dake harabar gidan suna masa sannu da dawowa.
A yanayi na gajiya yake nufar dakinsa yana observing na falon,komai fes kamar yadda yakeso,don babu abinda yafi tsana irin qazanta kaf rayuwarshi,shi yasa har yanzu ba abincin kowa yake ci ba,hakanan ba kowa yake bawa wankinsa ba.
Bandaki kawai ya wuce direct ya kunna water heater,saida ruwan ya tafasa ta kashe kanta sannan ya daidaita na zafi dana sanyi yadda zai masa dai dai da wankansa,kana ya shiga qasan ruwan ya soma sauka tun daga kansa yana tafiya da gajiya da kasalar data ma jikinsa qawanya,saiya rufe idanunsa yana tuna irin tarin baiwa da Allah ya masa,musamman a yau din,a hankali can qasan maqoshinsa ya dinga furta
"Alhamdulillah...Alhamdulillah".
Ya kusa minti talatin yana sakarwa jikinsa ruwan dumin sannan ya cuda sabulun wanka ya dauraye ya hada da alwala ya fito.
Sai daya tsane jikinsa da towel sannan ya nemi doguwar riga me gajeran hannu ya sakakkiya ya saka,ya feshe jikinsa da turaruka bayan ya taje kansa,sannan ya koma ya zauna saman kujerar dake dakin ya dauki wayarsa ya soma laluben 'yan gidansu,yanason yi musu ban gajiya,don wayar yakeson ya kashe gaba daya,don idan ya kwanta ya tabbatar salla ce kawai zata tasheshi,saboda yadda yake jin jikinsa.
Abban tsakiya ya fara kira,sannan abba yusuf,abbansa ne daga qarshe sai ya kira ummi,tata number bata shiga ba,don haka ya kira umma sa'annan ya kira mamanshi.
Tana hannun nurain a sannan,da hanzari ya nufi dakin maman yakai mata,don yasan zaiji babu dadi idan yayi gigin daga kiran ya haidar din,tunda yasan bashi yake nema ba.
A ladabce ya gaidata ya mata sannu da hanya,ta amsa masa sannan addu'a ta biyo baya,cikin farincikin dake ratsawa har cikin zuciyarsa yake amsa mata,sai kuma tayi kiran sunanshi
"Don Allah ka kula musu da amanar yarinya da aka bar maka,kada kayi wani abu da xai zamana ka watsamin qasa a ido,ka kuma barar da tarbiyyar da muka baka,a qarshe kuma ka qaryata soyayyar da hajja ke maka"
"In sha Allah mama zan kula....in sha Allah" daga haka sukayi sallama ya aje wayar yana sakin ajiyar zuciya yana shafa kanshi da hannunsa guda.
Tsahon wasu mintuna yana a haka ba tare da yasan me yake tunani ba,saiya miqe ya zura slippers dinsa ya fito falon.
Qarasawa tayi ta gaidata,sannan ta dubi salma dake riqe da jakar hajja,tana ta zuba zance ita dasu yasira wadda itama yau tazo din,duk an fito da jakankunan kayansu maman,wani sanyi ya ratsa zuciyarta,itakam dama ta gaji,so take kawai ayi a gama su wuce ko ta samu sa'ida hajja ta sakar mata mara tayi fitsari.
Data wuwwulga idanunta bata ga jakarta ba,sai tabi bayan salma data koma dauko jakar hannun hajja,ta isketa tana neman jakar a inda hajjan tace mata tana nan
"Don wulaqanci a dauki jakar kowa amma banda tawa,saboda ni bani da gata da galihu?"
"Ai an debi kayan da za'a koma miki dasu,an kawo miki wasu" duban salman tayi sanda take zuge zip din jakar
"Kamar yaya?"girarta ta daga
"Eh to....bari na tsegunta miki,kamar naji hajja tana fadin anan ke za'a barki,zaku taho tare da ya haidar ko?"
"Kambun bala'i!.....ni!,wallahi bazan zauna ba,tabdijan,ai itama hajjan ba haka mukayi da ita ba" ta fada tana jin wani tashin hankali yana ratsata,dafata salma tayi tana boye dariyarta
"Easy mana zuhra."
"Anqi easy din.....naga alama hajja wani abu daban takemin ba so ba,in banda haka ta yaya zata ce na zauna da wannan mutumin a cikin gidansa?,ya kasheni kenan akai musu gawata ko?,dama haka takeso".
"eh haka nakeso don ƙaniyarki....indai wannan shine rashin son to bana qaunarki fadi ki qara fada,ke salma tsaiwar me kikeyi ke kuma daga daukomi jaka?,miqomin driver yazo,ko mu wuce mu barki anan ki tayata zama" wani zillo salma tayi sai gata kusa da hajjan tana cewa
"Rufamin asiri kada ya zaki ya cillani ta window nayi kwanan qofar gida,a jawa yarona da mijina asara" kuka zahra ta saki harda dora hannu aka
"To wallahi nima bazan zauna ba,kowa tsoronsa yake amma haka kawai ni an hadani dashi?,saboda niba mutum bace?,idan ma cinyeni zaiyi ya cinyeni?"
"Eh haka nake nufi don gidanku,ja'irar yarinya" hajja ta sake cewa tana qwalalowa zahra idanu gamida tamke fuskarta kaman bada xahra'un tata take magana ba
"Wuce muje" ta fada tana nunawa salma hanya,tuni salman tayi gaba,tana danne dariyar dake taso mata,ita ta tseguntawa hajja cewa gobe zasuyi liyafar cin abincin dare dukka wadanda aka qarawa girma,kuma kowa da matarsa yake zuwa,idan ma akwai yara harda su,nan take hajjan tace dole haidar dinta shima asan ya zama babban mutum,dama a wajen taga idanun wata qabila yana haka haka akan jikan nata,duk inda yayi tana binsa da wani kallon yaudara na banza da wofi,tota Allah ba tataba,ba qaramin dariya akaci a motar ba da wannan ruɗu da hajjan ta hada ba,tuni itama hajja tabi bayanta,ai kuwa itama zahran saita kwashi jakarta ta rufawa hajjan baya.
Kacibus sukayi da umminta wadda ta sake shigowa ta rage mararta kada fitsari ya dameta a mota,duk sai suka ja baya,ta dubi ummin itama ummin ta dubeta,kallon da tayi mata shi ya sanyayar mata da jiki,saita tsugunna saman jakartata a wajen,ita kuma ummin ta wuce ciki abinta.
Batafi minti biyu ba ta fito,a lokacin zahran ta dawo bakin qofa ta tsuguna kamar me neman gafara ko taimako
"Kiyi duk yadda zakiyi,kiyi duk qoqarin da zakiyi ki nunawa duniya ban baki tarbiyya ba,ki nunawa duniya na sama dake basu isa dake ba,nayi imanin kaf fadin duniya idan na mutu kika laluba daga farko zuwa qarshe baki da masoyiya kamar hajja har abada,hakanan ko yanzu na mutu zan kwanta cikin kabarina hankalina kwance game da aurenki,don nasan ba zaki tozarta a hannun haidar ba,bazai taba wulaqantaki ba,ba hannun gama garin mutum kike ba,shi din na musamman ne wanda yasan da daraja da mutuncin dan adam,wanda ya kulaa ya kuma girmama rayuwar mahaifiyarki,ruwanki kiga girma da mutucinsa saboda haka,ruwanki kisa qafa ki shure.....zakiga kamar ba'a sonki,tako ina an matsa miki.....soyayya ta gaskiya itace ka tsaya tsayin daka wajen ganin naka ya gyaru kafin kowa,sannan matsalar zamantakewa a hausance sunan mace ke fara fitowa kafin na da namiji....baki da hurumin yankewa haidar hukunci sabida tsohon tunaninki na ba *ALƘIBLARKU* daya ba,akwai banbancin ra'ayi tsakaninku ko?,wannan rusashshiyar hujja ce.....a yanzu ina miki magana da harshen uwa zuwa ga diyarta......ki nutsu ki fara dora komai kan muhallinsa da saitinsa.....sai angwada ake sanin na qwarai" daga haka ummin tayi gaba abinta ba tare data waiwayo ba,ita kadai tasan me takeji a cikin zuciyarta,ita kadai tasan wanne fata ke gareta,ita kadai tasan adadin sau nawa tana hana idanunta bacci don ingantar rayuwar yaranta.
Da qyar ta tashi daga wajen ba tare data dauke jakarta data janyo wajen ba,a hankali tana jin yadda hayaniya da surutunsu keyin nesa da gidan,da alamu ficewa sukeyi,da qyar takai kanta bakin katifar ta zube,duka zantukan ummin nata sun tsaye mata kamar qusa a qahon zuci,hakanan sun kashe mata duk wani qwari na jikinta.27
Tsahon awa guda gidan ya dauki shuru,duk da lokaci zuwa lokaci tana dan jiyo motsi da maganganu sama sama daga falo zuwa kitchen,wanda ta tabbatar da ma'aikata ne.
Tun azahar take kwance bayan ta gama hawayenta son ranta ta godewa Allah,kota kan abinci bata biba,duk da karin safe ne kawai a cikinta,abu daya ke tada ita shine sallah,sai ruwa kawai data ke sha wanda shima cikin dakin yake jiya da dare suka shigo dashi basu shanye ba,haka ta dinga juyi ita kadai,har zuwa lokacin da duhun magarib ya sako kai,aka fara qwala kiran sallahr magariba,saita miqe tana jin yadda tsakiyar cikinta ya qulle,da alamu ulcer dinta tana son tashi kenan idan batayi wasa ba,hakan ya sanya sai data fara fitowa parlour ta bude fridge ta dauki fresh milk mai sanyi babban gora daya tana duban yadda falon ya koma fes,ko ina ɗas ɗas dashi yana fidda qamshi,kamar ba'a taba yin baqi ba,ba abinda ke fita sai wani samfurin qamshin freshner na musamman,ga abinci a jere a cikin tsari saman dining table,saita dauke kanta ta koma daki,ta zauna ta zuqe madarar tas sannan ta shiga bandaki,tana fitsari taji gefan mararta na qullewa
"Ya salam" ta fada,alamun period na iya zuwa anytime kenan,haka ta daura alwalarta ta dawo dakin ta tayar da sallar.
*Aliyyu Haidar*
Sosai yayi relax a bayan motar bayan ya aje hularsa a gefe yana furzar da iska daga bakinsa,yana jin yadda sanyin ac ke ratsashi tare da qara haifar masa da kasala da kuma tayar masa da gajiyarsa ta zirga zirgar wunin yau.
Zuciyarsa da qwaqwalwarsa tayi nisa wajen tuna abubuwan da suka faru yau wayarsa dake aje tare da hularsa ta dauki tsuwwa,dan qaramin tsaki yaja,ba kasafai ya fiya son kira ba,saidai yau yasha kiran har ya gode Allah,a hakama don yana kashewa ne baya amsa wani.
Ganin sunan me kiran yasa ba shiri yakai hannu ya dauka,labbansa suka motsa cikin ransa ya furta
"Rigimammiyar tsohuwa" saiya kara a kunnensa
"Badai har kunje gida ba?"
"Harma mun huta yanzu haka?"
"Ma sha Allah,sannunku da qoqari,Allah ya qara girma da nisan kwana me amfani"
"Amin ya rabbi...amin Aliyyu,Allah yayiwa rayuwa albarka"
"Amin hajja"
"Yauwa.....dama na kiraka ne na gaya maka,nabar amanar jikata a gidanka" fuska yadan yamutse yana son ya fahimci maganar tata,kamar kuwa tasan tunanin da yakeyi tace
"Matarka zahra....zaku taho tare idan ka gama abinda kake...."
"Amma hajja....bamuyi maganar ba....sannan ma kuma karatunta fa?"
"Kai da ita ku kukasan wani karatu.....,jan kunne na kiraka nayi maka,aronta na baka,bance kuma atabamin ita tun yanzu ba ehe" tun kafin takai ga kashe wayar shiya kashe,saiya jefata gefe yana dafe kansa,hajjan ta soma wuce tunaninsa,tunda harta fara masa manya manyan maganganu irin wannan,banda abinta ma shi da bashi ya nemi a barta ba su suka barta don raɗin kansu har tazo da wannan maganar,shikam wannan sabgar gada dayanta akwai qwara a cikinta.
Da ire iren wannan tunanin daya ci gaba dayi har suka isa gidan,ya fita yabar drivern yana kulle motar,yayi cikin gida,ma'aikatan dake harabar gidan suna masa sannu da dawowa.
A yanayi na gajiya yake nufar dakinsa yana observing na falon,komai fes kamar yadda yakeso,don babu abinda yafi tsana irin qazanta kaf rayuwarshi,shi yasa har yanzu ba abincin kowa yake ci ba,hakanan ba kowa yake bawa wankinsa ba.
Bandaki kawai ya wuce direct ya kunna water heater,saida ruwan ya tafasa ta kashe kanta sannan ya daidaita na zafi dana sanyi yadda zai masa dai dai da wankansa,kana ya shiga qasan ruwan ya soma sauka tun daga kansa yana tafiya da gajiya da kasalar data ma jikinsa qawanya,saiya rufe idanunsa yana tuna irin tarin baiwa da Allah ya masa,musamman a yau din,a hankali can qasan maqoshinsa ya dinga furta
"Alhamdulillah...Alhamdulillah".
Ya kusa minti talatin yana sakarwa jikinsa ruwan dumin sannan ya cuda sabulun wanka ya dauraye ya hada da alwala ya fito.
Sai daya tsane jikinsa da towel sannan ya nemi doguwar riga me gajeran hannu ya sakakkiya ya saka,ya feshe jikinsa da turaruka bayan ya taje kansa,sannan ya koma ya zauna saman kujerar dake dakin ya dauki wayarsa ya soma laluben 'yan gidansu,yanason yi musu ban gajiya,don wayar yakeson ya kashe gaba daya,don idan ya kwanta ya tabbatar salla ce kawai zata tasheshi,saboda yadda yake jin jikinsa.
Abban tsakiya ya fara kira,sannan abba yusuf,abbansa ne daga qarshe sai ya kira ummi,tata number bata shiga ba,don haka ya kira umma sa'annan ya kira mamanshi.
Tana hannun nurain a sannan,da hanzari ya nufi dakin maman yakai mata,don yasan zaiji babu dadi idan yayi gigin daga kiran ya haidar din,tunda yasan bashi yake nema ba.
A ladabce ya gaidata ya mata sannu da hanya,ta amsa masa sannan addu'a ta biyo baya,cikin farincikin dake ratsawa har cikin zuciyarsa yake amsa mata,sai kuma tayi kiran sunanshi
"Don Allah ka kula musu da amanar yarinya da aka bar maka,kada kayi wani abu da xai zamana ka watsamin qasa a ido,ka kuma barar da tarbiyyar da muka baka,a qarshe kuma ka qaryata soyayyar da hajja ke maka"
"In sha Allah mama zan kula....in sha Allah" daga haka sukayi sallama ya aje wayar yana sakin ajiyar zuciya yana shafa kanshi da hannunsa guda.
Tsahon wasu mintuna yana a haka ba tare da yasan me yake tunani ba,saiya miqe ya zura slippers dinsa ya fito falon.